< Ayyukan Manzanni 28 >
1 Bayan da muka kai bakin tekun lafiya, sai muka tarar cewa sunan tsibirin Malta ne.
In ko so se bili oteli, tedaj so spoznali, da se otok imenuje Melita.
2 Mutanen tsibirin kuwa suka nuna mana babban alheri. Suka hura wuta suka marabce mu duka saboda ana ruwan sama da kuma sanyi.
Divjaki pa so nam izkazovali ne majheno ljudmilost; kajti naložili so grmado, in sprejeli so nas vse, za dež, ki je šel, in za mraz.
3 Bulus ya tattara tarin itace, yayinda kuma yake sa itacen a wuta, sai maciji ya ɓullo saboda zafi, ya dāfe a hannunsa.
Ko je pa zgrabil Pavel kup hoste, in je del na ogenj, izide gad od vročine, in obesi mu se za roko.
4 Da mutanen tsibirin suka ga macijin yana lilo a hannunsa, sai suka ce wa juna “Lalle, wannan mutum mai kisankai ne; gama ko da yake ya tsira daga teku, Adalci bai bar shi ya rayu ba.”
Ko so pa videli divjaki, da mu visi zver na roki, govorili so med seboj: Gotovo je ta človek ubijalec, kterega, otetega iz morja, pravica maščevalka ne pustí živeti.
5 Amma Bulus ya karkaɗe macijin a cikin wuta, bai kuwa ji wani ciwo ba.
On pa otrese zver na ogenj, in nič hudega mu se ni zgodilo.
6 Mutanen kuma suka yi zato zai kumbura ko kuma nan da nan zai fāɗi matacce, amma da aka daɗe ba su ga wani abu ya faru da shi ba, sai suka sāke ra’ayi suka ce shi wani allah ne.
Oni so pa čakali, da bo otekel ali h krati padel in umrl. Ko so pa dolgo čakali, in so videli, da mu se nič hudega ne zgodí, premenili so so, in pravili so, da je bog.
7 Akwai wani filin nan kusa wanda yake na Fubiliyus, babban shugaban tsibirin. Shi ne ya karɓe mu a gidansa da alheri ya kuma ciyar da mu har kwana uku.
Okoli tega kraja pa so bile pristave poglavarja otoka, po imenu Publija, kteri nas je sprejel in tri dní prijazno gostil.
8 Mahaifinsa kuwa yana kwanciya a gado yana fama da zazzaɓi da atuni. Bulus ya shiga ciki don yă gan shi, bayan ya yi masa addu’a, sai ya ɗibiya masa hannuwa ya warkar da shi.
Zgodí se pa, da je oče Publijev od mrzlice in griže bolan ležal: k temu Pavel vnide, In molivši, položi na-nj roke, in uzdravil ga je.
9 Sa’ad da wannan ya faru, sauran marasa lafiya a tsibirin suka zo aka kuma warkar da su.
In ko se je to zgodilo, dohajali so tudi drugi, kteri so imeli bolezni na otoku, in ozdravljali so se;
10 Suka girmama mu ta kowane hali da muka shirya za mu tashi, sai suka ba mu abubuwan da muke bukata.
Kteri so nas tudi z velikimi častmi častili, in ko smo odšli, naložili so, kar je bilo potreba.
11 Bayan wata uku sai muka tashi a wani jirgin ruwan da ya ci damina a tsibirin. Jirgin ruwa kuwa na Alekzandariya ne yana da siffar tagwayen allolin Kasto da Follus.
A po treh mesecih smo se odpeljali na ladji Aleksandrijskej, ktera je bila prezimila na otoku, in je imela znamenje Dvojčkov.
12 Muka isa Sirakus a can muka yi kwana uku.
In pripeljavši se v Sirakuze, ostali smo tu tri dni.
13 Daga can muka tashi muka isa Regiyum. Kashegari iskar kudu ta taso, kashegari kuma muka kai Futeyoli.
Odtod smo se okoli peljali, in prišli smo v Regijo, in ko je en dan potem potegnil jug, prišli smo drugi dan v Puteole.
14 A can muka tarar da waɗansu’yan’uwa waɗanda suka gayyaci mu mu yi mako ɗaya da su. Da haka dai muka kai Roma.
Tu smo našli bratov, in prosili so nas, naj bi pri njih prebili sedem dni; in tako smo prišli v Rim.
15 ’Yan’uwan da suke can sun sami labari cewa muna zuwa, sai suka tashi tun daga Kasuwar Affiyus da Masauƙi Uku don su tarye mu. Da ganin mutanen nan sai Bulus ya gode wa Allah ya kuma sami ƙarfafawa.
In odtod, ko so bratje slišali za nas, izšli so nam naproti noter do Agapijevega Trga in Treh Krčem; in ko jih je videl Pavel, zahvalil je Boga, in napolnil se je zaupanja.
16 Da muka isa Roma, sai aka yarda wa Bulus yă zauna shi kaɗai, tare da sojan da zai yi gadinsa.
Ko smo pa prišli v Rim, izročil je stotnik jetnike vojvodu; a Pavlu se je dovolilo prebivati, kjer sam hoče, z vojakom, kteri ga je varoval.
17 Bayan kwana uku sai ya kira taron shugabannin Yahudawa. Da suka taru, Bulus ya ce musu, “’Yan’uwana, ko da yake ban yi wa mutanenmu wani laifi ba ko kuma wani abu game da al’adun kakanninmu, aka kama ni a Urushalima aka kuma ba da ni ga Romawa.
Zgodí pa se po treh dnéh, da skliče Pavel prvake Judovske; in ko so se sešli, govoril jim je: Možjé bratje! da si ravno jaz ničesar nisem storil zoper narod ali šege očetovske, vendar so me zvezanega iz Jeruzalema izročili v roke Rimljanom;
18 Suka tuhume ni suka kuma so su sake ni, domin ba a same ni da wani laifin da ya cancanci kisa ba.
Kteri so me, zaslišavši me, hoteli izpustiti, za to, ker ni bilo nobene smrtne krivice na meni.
19 Amma da Yahudawa suka ƙi, sai ya zama mini dole in ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba don ina da wani zargin da zan kawo game da mutanena ba.
Ko so se pa Judje ustavljali, prisiljen sem bil sklicati se na cesarja, ne kakor da bi narod svoj imel za kaj tožiti.
20 Saboda wannan ne na nemi in gan ku in kuma yi magana da ku. Saboda begen Isra’ila ne, nake a daure da wannan sarƙa.”
Za voljo tega torej vzroka sem vas poklical, da bi vas videl in ogovoril; kajti za voljo upanja Izraelovega sem okovan v to verigo.
21 Suka amsa cewa, “Ba mu sami wani wasiƙa daga Yahudiya game da kai ba, kuma ba kowa daga cikin’yan’uwan da suka zo daga can ya kawo wani labari ko ya faɗi wani mummuna abu game da kai.
Oni mu pa rekó: Mi nismo ne pisem za-te prejeli iz Judeje, in tudi nobeden izmed bratov ni prišel, da bi sporočil ali govoril kaj o tebi hudega.
22 Amma muna so mu ji ra’ayinka, gama mun san cewa mutane ko’ina suna muguwar magana a kan wannan ɗarikar.”
Prosimo pa slišati od tebe, kaj da misliš; kajti za to ločinko nam je znano, da jej se povsodi zoper govorí.
23 Suka shirya su sadu da Bulus wata rana, suka ma zo da yawa fiye da dā a wurin da Bulus yake zama. Daga safe har zuwa yamma ya yi ta yin musu bayani, ya kuma shaida musu mulkin Allah yana ƙoƙarin rinjayarsu game da Yesu daga Dokar Musa da kuma daga Annabawa.
In ko so mu odločili dan, prišlo jih je k njemu v stanovanje veliko; kterim je razlagal, pričevaje, kraljestvo Božje, in izkazujoč jim to, kar se dotiče Jezusa, iz postave Mojzesove in prerokov, od zore do mraka.
24 Waɗansu suka rinjayu da abin da ya faɗa, amma waɗansu suka ba su gaskata ba.
In nekteri so verovali temu, kar jim je pravil, a nekteri niso verovali.
25 Suka kāsa yarda da juna suka fara watsewa bayan Bulus ya yi wannan magana guda cewa, “Ruhu Mai Tsarki ya faɗa wa kakannin-kakanninku gaskiya sa’ad da ya ce ta bakin annabi Ishaya cewa,
In ker niso bili ene misli med seboj, odhajali so, ko je rekel Pavel eno besedo: Dobro je povedal sveti Duh po Izaiji preroku očetom našim,
26 “‘Je ka wurin mutanen nan ka ce, “Za ku yi ta ji amma ba za ku fahimta ba; za ku yi ta dubawa, amma ba za ku gani ba.”
Govoreč: "Pojdi k temu ljudstvu in reci: S sluhom boste slišali, in ne boste umeli; in z očmí boste gledali, in ne boste videli.
27 Gama zuciyar mutanen nan ta yi tauri; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta a zukatansu, su kuma juyo, in kuwa warkar da su.’
Kajti okamenelo je srce temu ljudstvu, in z ušesi težko slišijo, in očí svoje so zatisnili: da ne bi kako z očmí videli, in z ušesi slišali, in s srcem umeli in izpreobrnili se, ter bi jih uzdravil."
28 “Saboda haka na so ku san cewa an aika da ceton Allah ga Al’ummai, za su kuwa saurara!”
Bodi vam torej znano, da se je poganom poslalo zveličanje Božje: oni bodo tudi poslušali.
In ko je to povedal, odšli so Judje, in imeli so mnogo prepira med seboj.
30 Shekaru biyu cif Bulus ya zauna a can a gidansa na haya yana marabtar duk wanda ya je wurinsa.
Ostal je pa Pavel celi dve leti v svojem najetem stanovanji, in sprejemal je vse, kteri so dohajali k njemu,
31 Ya yi wa’azin mulkin Allah yana kuma koyarwa game da Ubangiji Yesu Kiristi, gabagadi ba tare da wani abu ya hana shi ba.
Oznanjujoč kraljestvo Božje in učeč to, kar je Gospoda Jezusa Kristusa, z vso srčnostjo, in nikdor mu ni branil.