< Ayyukan Manzanni 28 >

1 Bayan da muka kai bakin tekun lafiya, sai muka tarar cewa sunan tsibirin Malta ne.
And when they were safe on shore, they understood, that the island was called Melita.
2 Mutanen tsibirin kuwa suka nuna mana babban alheri. Suka hura wuta suka marabce mu duka saboda ana ruwan sama da kuma sanyi.
And the barbarians shewed us uncommon humanity: for they kindled a fire and took us all in, because of the present rain, and of the cold.
3 Bulus ya tattara tarin itace, yayinda kuma yake sa itacen a wuta, sai maciji ya ɓullo saboda zafi, ya dāfe a hannunsa.
And Paul having gathered together a bundle of sticks, and laid them on the fire, there came out a viper from the heat, and fastened on his hand.
4 Da mutanen tsibirin suka ga macijin yana lilo a hannunsa, sai suka ce wa juna “Lalle, wannan mutum mai kisankai ne; gama ko da yake ya tsira daga teku, Adalci bai bar shi ya rayu ba.”
And when the barbarians saw the venomous creature hanging on his hand, they said to one another, This man is certainly a murderer, whom, though he hath been saved from the sea, yet justice suffereth not to live.
5 Amma Bulus ya karkaɗe macijin a cikin wuta, bai kuwa ji wani ciwo ba.
But he shook off the creature into the fire, and suffered no hurt.
6 Mutanen kuma suka yi zato zai kumbura ko kuma nan da nan zai fāɗi matacce, amma da aka daɗe ba su ga wani abu ya faru da shi ba, sai suka sāke ra’ayi suka ce shi wani allah ne.
They however were expecting that he would swell, or suddenly fall down dead: but when they had waited a good while, and saw no hurt come to him, they changed their opinion and said that he was a god.
7 Akwai wani filin nan kusa wanda yake na Fubiliyus, babban shugaban tsibirin. Shi ne ya karɓe mu a gidansa da alheri ya kuma ciyar da mu har kwana uku.
Now in the parts adjacent to this place was the seat of the chief man of the island, whose name was Publius, who took us into his house, and entertained us three days courteously.
8 Mahaifinsa kuwa yana kwanciya a gado yana fama da zazzaɓi da atuni. Bulus ya shiga ciki don yă gan shi, bayan ya yi masa addu’a, sai ya ɗibiya masa hannuwa ya warkar da shi.
And it happened that the father of Publius lay sick of a fever and dysentery: to whom Paul went in, and prayed, and laid his hands on him, and healed him.
9 Sa’ad da wannan ya faru, sauran marasa lafiya a tsibirin suka zo aka kuma warkar da su.
Upon this, others also in the island, who had diseases came to him and were cured:
10 Suka girmama mu ta kowane hali da muka shirya za mu tashi, sai suka ba mu abubuwan da muke bukata.
who also honoured us with many honors, and furnished us, when we departed, with such things as were necessary.
11 Bayan wata uku sai muka tashi a wani jirgin ruwan da ya ci damina a tsibirin. Jirgin ruwa kuwa na Alekzandariya ne yana da siffar tagwayen allolin Kasto da Follus.
And after three months we departed in a ship of Alexandria, that had wintered in the island, whose sign was Castor and Pollux.
12 Muka isa Sirakus a can muka yi kwana uku.
And being arrived at Syracuse, we staid there three days.
13 Daga can muka tashi muka isa Regiyum. Kashegari iskar kudu ta taso, kashegari kuma muka kai Futeyoli.
From whence coasting round we came to Rhegium, and after one day a south-wind rising, we came the second day to Puteoli:
14 A can muka tarar da waɗansu’yan’uwa waɗanda suka gayyaci mu mu yi mako ɗaya da su. Da haka dai muka kai Roma.
where finding some brethren, we were desired to stay with them seven days: and so we went on to Rome.
15 ’Yan’uwan da suke can sun sami labari cewa muna zuwa, sai suka tashi tun daga Kasuwar Affiyus da Masauƙi Uku don su tarye mu. Da ganin mutanen nan sai Bulus ya gode wa Allah ya kuma sami ƙarfafawa.
And when the brethren heard of us, they came from thence to meet us, some as far as Appii-forum, and others to the Three-taverns: whom when Paul saw, he thanked God and took courage.
16 Da muka isa Roma, sai aka yarda wa Bulus yă zauna shi kaɗai, tare da sojan da zai yi gadinsa.
And when we came to Rome, the centurion delivered the prisoners to the captain of the guard: but Paul was permitted to live by himself with the soldier that had him in custody.
17 Bayan kwana uku sai ya kira taron shugabannin Yahudawa. Da suka taru, Bulus ya ce musu, “’Yan’uwana, ko da yake ban yi wa mutanenmu wani laifi ba ko kuma wani abu game da al’adun kakanninmu, aka kama ni a Urushalima aka kuma ba da ni ga Romawa.
And after three days Paul called together the chief of the Jews. And when they were come together, he said unto them, Brethren, though I have done nothing against the people of the Jews, or the customs of our fathers, yet was I delivered a prisoner from Jerusalem into the hands of the Romans:
18 Suka tuhume ni suka kuma so su sake ni, domin ba a same ni da wani laifin da ya cancanci kisa ba.
who when they had examined me, would have set me at liberty, because there was no crime worthy of death found in me:
19 Amma da Yahudawa suka ƙi, sai ya zama mini dole in ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba don ina da wani zargin da zan kawo game da mutanena ba.
but the Jews opposing it, I was obliged to appeal to Cesar; though not as having any thing to accuse my nation of.
20 Saboda wannan ne na nemi in gan ku in kuma yi magana da ku. Saboda begen Isra’ila ne, nake a daure da wannan sarƙa.”
For this reason therefore I desired to see and to speak to you: because that for the hope of Israel I am bound with this chain.
21 Suka amsa cewa, “Ba mu sami wani wasiƙa daga Yahudiya game da kai ba, kuma ba kowa daga cikin’yan’uwan da suka zo daga can ya kawo wani labari ko ya faɗi wani mummuna abu game da kai.
And they said to him, We have neither received letters concerning thee from Judea, nor has any of the brethren, that is come hither, related or spoken any ill of thee.
22 Amma muna so mu ji ra’ayinka, gama mun san cewa mutane ko’ina suna muguwar magana a kan wannan ɗarikar.”
But we would willingly hear from thee what thou thinkest: for as to this sect, we know that it is every where spoken against.
23 Suka shirya su sadu da Bulus wata rana, suka ma zo da yawa fiye da dā a wurin da Bulus yake zama. Daga safe har zuwa yamma ya yi ta yin musu bayani, ya kuma shaida musu mulkin Allah yana ƙoƙarin rinjayarsu game da Yesu daga Dokar Musa da kuma daga Annabawa.
And having appointed him a day, many came to him at his lodging; to whom he discoursed and testified the kingdom of God, persuading them of the things concerning Jesus, both from the law of Moses, and from the prophets, from morning till evening.
24 Waɗansu suka rinjayu da abin da ya faɗa, amma waɗansu suka ba su gaskata ba.
And some regarded the things that were spoken, but others did not believe.
25 Suka kāsa yarda da juna suka fara watsewa bayan Bulus ya yi wannan magana guda cewa, “Ruhu Mai Tsarki ya faɗa wa kakannin-kakanninku gaskiya sa’ad da ya ce ta bakin annabi Ishaya cewa,
And so disagreeing one with another they separated, when Paul had said one word, to wit, that the holy Spirit spake rightly by Esaias the prophet to our fathers,
26 “‘Je ka wurin mutanen nan ka ce, “Za ku yi ta ji amma ba za ku fahimta ba; za ku yi ta dubawa, amma ba za ku gani ba.”
saying, Go to this people and say, Ye shall hear by the hearing of the ear, and not understand; and in seeing ye shall see, and not perceive: for the heart of this people is stupified,
27 Gama zuciyar mutanen nan ta yi tauri; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta a zukatansu, su kuma juyo, in kuwa warkar da su.’
and they hear heavily with their ears, and have closed their eyes; least they should see at all with their eyes, and hear with their ears, and understand with their heart, and be converted, and I should heal them.
28 “Saboda haka na so ku san cewa an aika da ceton Allah ga Al’ummai, za su kuwa saurara!”
Be it known therefore unto you, that the salvation of God is sent to the Gentiles, and they will hear it.
And when he had said these things, the Jews departed, having much debate among themselves.
30 Shekaru biyu cif Bulus ya zauna a can a gidansa na haya yana marabtar duk wanda ya je wurinsa.
And Paul abode two whole years in his own hired house, and received all that came to him:
31 Ya yi wa’azin mulkin Allah yana kuma koyarwa game da Ubangiji Yesu Kiristi, gabagadi ba tare da wani abu ya hana shi ba.
preaching the kingdom of God, and teaching the things concerning the Lord Jesus Christ, with all freedom, none forbidding him.

< Ayyukan Manzanni 28 >