< Ayyukan Manzanni 28 >

1 Bayan da muka kai bakin tekun lafiya, sai muka tarar cewa sunan tsibirin Malta ne.
And when we had escaped, then we knew that the island was called Melita. But the barbarians shewed us no small courtesy.
2 Mutanen tsibirin kuwa suka nuna mana babban alheri. Suka hura wuta suka marabce mu duka saboda ana ruwan sama da kuma sanyi.
For kindling a fire, they refreshed us all, because of the present rain, and of the cold.
3 Bulus ya tattara tarin itace, yayinda kuma yake sa itacen a wuta, sai maciji ya ɓullo saboda zafi, ya dāfe a hannunsa.
And when Paul had gathered together a bundle of sticks, and had laid them on the fire, a viper coming out of the heat, fastened on his hand.
4 Da mutanen tsibirin suka ga macijin yana lilo a hannunsa, sai suka ce wa juna “Lalle, wannan mutum mai kisankai ne; gama ko da yake ya tsira daga teku, Adalci bai bar shi ya rayu ba.”
And when the barbarians saw the beast hanging on his hand, they said one to another: Undoubtedly this man is a murderer, who though he hath escaped the sea, yet vengeance doth not suffer him to live.
5 Amma Bulus ya karkaɗe macijin a cikin wuta, bai kuwa ji wani ciwo ba.
And he indeed shaking off the beast into the fire, suffered no harm.
6 Mutanen kuma suka yi zato zai kumbura ko kuma nan da nan zai fāɗi matacce, amma da aka daɗe ba su ga wani abu ya faru da shi ba, sai suka sāke ra’ayi suka ce shi wani allah ne.
But they supposed that he would begin to swell up, and that he would suddenly fall down and die. But expecting long, and seeing that there came no harm to him, changing their minds, they said, that he was a god.
7 Akwai wani filin nan kusa wanda yake na Fubiliyus, babban shugaban tsibirin. Shi ne ya karɓe mu a gidansa da alheri ya kuma ciyar da mu har kwana uku.
Now in these places were possessions of the chief man of the island, named Publius, who receiving us, for three days entertained us courteously.
8 Mahaifinsa kuwa yana kwanciya a gado yana fama da zazzaɓi da atuni. Bulus ya shiga ciki don yă gan shi, bayan ya yi masa addu’a, sai ya ɗibiya masa hannuwa ya warkar da shi.
And it happened that the father of Publius lay sick of a fever, and of a bloody flux. To whom Paul entered in; and when he had prayed, and laid his hands on him, he healed him.
9 Sa’ad da wannan ya faru, sauran marasa lafiya a tsibirin suka zo aka kuma warkar da su.
Which being done, all that had diseases in the island, came and were healed:
10 Suka girmama mu ta kowane hali da muka shirya za mu tashi, sai suka ba mu abubuwan da muke bukata.
Who also honoured us with many honours, and when we were to set sail, they laded us with such things as were necessary.
11 Bayan wata uku sai muka tashi a wani jirgin ruwan da ya ci damina a tsibirin. Jirgin ruwa kuwa na Alekzandariya ne yana da siffar tagwayen allolin Kasto da Follus.
And after three months, we sailed in a ship of Alexandria, that had wintered in the island, whose sign was the Castors.
12 Muka isa Sirakus a can muka yi kwana uku.
And when we were come to Syracusa, we tarried there three days.
13 Daga can muka tashi muka isa Regiyum. Kashegari iskar kudu ta taso, kashegari kuma muka kai Futeyoli.
From thence, compassing by the shore, we came to Rhegium: and after one day, the south wind blowing, we came the second day to Puteoli;
14 A can muka tarar da waɗansu’yan’uwa waɗanda suka gayyaci mu mu yi mako ɗaya da su. Da haka dai muka kai Roma.
Where, finding brethren, we were desired to tarry with them seven days: and so we went to Rome.
15 ’Yan’uwan da suke can sun sami labari cewa muna zuwa, sai suka tashi tun daga Kasuwar Affiyus da Masauƙi Uku don su tarye mu. Da ganin mutanen nan sai Bulus ya gode wa Allah ya kuma sami ƙarfafawa.
And from thence, when the brethren had heard of us, they came to meet us as far as Appii Forum, and the Three Taverns: whom when Paul saw, he gave thanks to God, and took courage.
16 Da muka isa Roma, sai aka yarda wa Bulus yă zauna shi kaɗai, tare da sojan da zai yi gadinsa.
And when we were come to Rome, Paul was suffered to dwell by himself, with a soldier that kept him.
17 Bayan kwana uku sai ya kira taron shugabannin Yahudawa. Da suka taru, Bulus ya ce musu, “’Yan’uwana, ko da yake ban yi wa mutanenmu wani laifi ba ko kuma wani abu game da al’adun kakanninmu, aka kama ni a Urushalima aka kuma ba da ni ga Romawa.
And after the third day, he called together the chief of the Jews. And when they were assembled, he said to them: Men, brethren, I, having done nothing against the people, or the custom of our fathers, was delivered prisoner from Jerusalem into the hands of the Romans;
18 Suka tuhume ni suka kuma so su sake ni, domin ba a same ni da wani laifin da ya cancanci kisa ba.
Who, when they had examined me, would have released me, for that there was no cause of death in me;
19 Amma da Yahudawa suka ƙi, sai ya zama mini dole in ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba don ina da wani zargin da zan kawo game da mutanena ba.
But the Jews contradicting it, I was constrained to appeal unto Caesar; not that I had any thing to accuse my nation of.
20 Saboda wannan ne na nemi in gan ku in kuma yi magana da ku. Saboda begen Isra’ila ne, nake a daure da wannan sarƙa.”
For this cause therefore I desired to see you, and to speak to you. Because that for the hope of Israel, I am bound with this chain.
21 Suka amsa cewa, “Ba mu sami wani wasiƙa daga Yahudiya game da kai ba, kuma ba kowa daga cikin’yan’uwan da suka zo daga can ya kawo wani labari ko ya faɗi wani mummuna abu game da kai.
But they said to him: We neither received letters concerning thee from Judea, neither did any of the brethren that came hither, relate or speak any evil of thee.
22 Amma muna so mu ji ra’ayinka, gama mun san cewa mutane ko’ina suna muguwar magana a kan wannan ɗarikar.”
But we desire to hear of thee what thou thinkest; for as concerning this sect, we know that it is every where contradicted.
23 Suka shirya su sadu da Bulus wata rana, suka ma zo da yawa fiye da dā a wurin da Bulus yake zama. Daga safe har zuwa yamma ya yi ta yin musu bayani, ya kuma shaida musu mulkin Allah yana ƙoƙarin rinjayarsu game da Yesu daga Dokar Musa da kuma daga Annabawa.
And when they had appointed him a day, there came very many to him unto his lodgings; to whom he expounded, testifying the kingdom of God, and persuading them concerning Jesus, out of the law of Moses and the prophets, from morning until evening.
24 Waɗansu suka rinjayu da abin da ya faɗa, amma waɗansu suka ba su gaskata ba.
And some believed the things that were said; but some believed not.
25 Suka kāsa yarda da juna suka fara watsewa bayan Bulus ya yi wannan magana guda cewa, “Ruhu Mai Tsarki ya faɗa wa kakannin-kakanninku gaskiya sa’ad da ya ce ta bakin annabi Ishaya cewa,
And when they agreed not among themselves, they departed, Paul speaking this one word: Well did the Holy Ghost speak to our fathers by Isaias the prophet,
26 “‘Je ka wurin mutanen nan ka ce, “Za ku yi ta ji amma ba za ku fahimta ba; za ku yi ta dubawa, amma ba za ku gani ba.”
Saying: Go to this people, and say to them: With the ear you shall hear, and shall not understand; and seeing you shall see, and shall not perceive.
27 Gama zuciyar mutanen nan ta yi tauri; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta a zukatansu, su kuma juyo, in kuwa warkar da su.’
For the heart of this people is grown gross, and with their ears have they heard heavily, and their eyes they have shut; lest perhaps they should see with their eyes, and hear with their ears, and understand with their heart, and should be converted, and I should heal them.
28 “Saboda haka na so ku san cewa an aika da ceton Allah ga Al’ummai, za su kuwa saurara!”
Be it known therefore to you, that this salvation of God is sent to the Gentiles, and they will hear it.
And when he had said these things, the Jews went out from him, having much reasoning among themselves.
30 Shekaru biyu cif Bulus ya zauna a can a gidansa na haya yana marabtar duk wanda ya je wurinsa.
And he remained two whole years in his own hired lodging; and he received all that came in to him,
31 Ya yi wa’azin mulkin Allah yana kuma koyarwa game da Ubangiji Yesu Kiristi, gabagadi ba tare da wani abu ya hana shi ba.
Preaching the kingdom of God, and teaching the things which concern the Lord Jesus Christ, with all confidence, without prohibition.

< Ayyukan Manzanni 28 >