< Ayyukan Manzanni 27 >

1 Sa’ad da aka yanke shawara cewa za mu tashi a jirgin ruwa zuwa Italiya, sai aka danƙa Bulus da waɗansu’yan kurkuku a hannun wani jarumin mai suna Juliyos, wanda yake na Bataliyar Babban Sarki.
jalapathēnāsmākam itōliyādēśaṁ prati yātrāyāṁ niścitāyāṁ satyāṁ tē yūliyanāmnō mahārājasya saṁghātāntargatasya sēnāpatēḥ samīpē paulaṁ tadanyān katinayajanāṁśca samārpayan|
2 Muka shiga jirgin ruwa daga Andiramitiyum wanda yake shirin tashi zuwa tasoshin da suke bakin tekun lardin Asiya, sai muka kama tafiya. Aristarkus, mutumin Makidoniya daga Tessalonika, yana tare da mu.
vayam ādrāmuttīyaṁ pōtamēkam āruhya āśiyādēśasya taṭasamīpēna yātuṁ matiṁ kr̥tvā laṅgaram utthāpya pōtam amōcayāma; mākidaniyādēśasthathiṣalanīkīnivāsyāristārkhanāmā kaścid janō'smābhiḥ sārddham āsīt|
3 Kashegari muka sauka a Sidon; Juliyos kuwa, cikin alheri ga Bulus, ya bar shi yă je wajen abokansa domin su biya masa bukatunsa.
parasmin divasē 'smābhiḥ sīdōnnagarē pōtē lāgitē tatra yūliyaḥ sēnāpatiḥ paulaṁ prati saujanyaṁ pradarthya sāntvanārthaṁ bandhubāndhavān upayātum anujajñau|
4 Daga can kuma muka sāke kama tafiya muka zaga ta bayan tsibirin Saifurus saboda iska tana gāba da mu.
tasmāt pōtē mōcitē sati sammukhavāyōḥ sambhavād vayaṁ kuprōpadvīpasya tīrasamīpēna gatavantaḥ|
5 Sa’ad da muka ƙetare tekun da yake sassan gaɓar Silisiya da Famfiliya sai muka sauka a Mira ta Lisiya.
kilikiyāyāḥ pāmphūliyāyāśca samudrasya pāraṁ gatvā lūkiyādēśāntargataṁ murānagaram upātiṣṭhāma|
6 A can jarumin ya sami wani jirgin ruwan Alekzandariyan da za shi Italiya sai ya sa mu a ciki.
tatsthānād itāliyādēśaṁ gacchati yaḥ sikandariyānagarasya pōtastaṁ tatra prāpya śatasēnāpatistaṁ pōtam asmān ārōhayat|
7 Tafiyar ta ɗauki kwanaki da yawa muna yi kaɗan-kaɗan da ƙyar muka iso kusa da gaɓar Kinidus. Da iskar ta hana mu ci gaba, sai muka bi ta bayan tsibirin Kirit ɗaura da Salmone.
tataḥ paraṁ bahūni dināni śanaiḥ śanaiḥ rgatvā knīdapārśvōpasthtiḥ pūrvvaṁ pratikūlēna pavanēna vayaṁ salmōnyāḥ sammukham upasthāya krītyupadvīpasya tīrasamīpēna gatavantaḥ|
8 Muka ci gaba a gefen gaɓar da ƙyar har muka iso wani wurin da ake kira Kyakkyawan Mafaka, kusa da garin Laseya.
kaṣṭēna tamuttīryya lāsēyānagarasyādhaḥ sundaranāmakaṁ khātam upātiṣṭhāma|
9 An riga an ɓata lokaci da yawa, tafiya kuwa ta riga ta zama da hatsari domin a lokacin Azumi ya riga ta wuce. Saboda haka Bulus ya gargaɗe su,
itthaṁ bahutithaḥ kālō yāpita upavāsadinañcātītaṁ, tatkāraṇāt nauvartmani bhayaṅkarē sati paulō vinayēna kathitavān,
10 ya ce, “Mutane, ina gani tafiyarmu za tă zama da masifa ta kuma kawo babbar hasara ga jirgin ruwan da kaya, da kuma ga rayukanmu ma.”
hē mahēcchā ahaṁ niścayaṁ jānāmi yātrāyāmasyām asmākaṁ klēśā bahūnāmapacayāśca bhaviṣyanti, tē kēvalaṁ pōtasāmagryōriti nahi, kintvasmākaṁ prāṇānāmapi|
11 Amma jarumin, a maimakon ya saurari abin da Bulus ya ce, sai ya bi shawarar matuƙi da kuma mai jirgin ruwan.
tadā śatasēnāpatiḥ paulōktavākyatōpi karṇadhārasya pōtavaṇijaśca vākyaṁ bahumaṁsta|
12 Da yake tashar jirgin ruwan ba tă dace a ci damina a can ba, yawanci suka ba yanke shawara cewa mu ci gaba da tafiya, da bege za mu kai Funis mu ci damina a can. Wannan tashar jirgin ruwa ne a Kirit, tana fuskantar kudu maso yamma da kuma arewa maso yamma.
tat khātaṁ śītakālē vāsārhasthānaṁ na tasmād avācīpratīcōrdiśōḥ krītyāḥ phainīkiyakhātaṁ yātuṁ yadi śaknuvantastarhi tatra śītakālaṁ yāpayituṁ prāyēṇa sarvvē mantrayāmāsuḥ|
13 Da iska ta fara busowa daga kudu a hankali, sai suka yi tsammani sun sami abin da suke nema; saboda haka suka janye ƙugiyar jirgin ruwa suka bi ta gefen tsibirin Kirit.
tataḥ paraṁ dakṣiṇavāyu rmandaṁ vahatīti vilōkya nijābhiprāyasya siddhēḥ suyōgō bhavatīti buddhvā pōtaṁ mōcayitvā krītyupadvīpasya tīrasamīpēna calitavantaḥ|
14 Ba a jima ba, sai ga wata guguwar iska mai ƙarfin da ake kira “’Yar arewa maso gabas,” ta buga daga tsibirin.
kintvalpakṣaṇāt paramēva urakludōnnāmā pratikūlaḥ pracaṇḍō vāyu rvahan pōtē'lagīt
15 Iskar ta ci ƙarfin jirgin ruwan har ya kāsa fuskantar iskar; saboda haka muka sallamar mata tă yi ta tura mu.
tasyābhimukhaṁ gantum pōtasyāśaktatvād vayaṁ vāyunā svayaṁ nītāḥ|
16 Da muka bi ta bayan wani ɗan tsibirin da ake kira Kauda, da ƙyar muka jawo ɗan ƙaramin jirgin kusa da jirgin.
anantaraṁ klaudīnāmna upadvīpasya kūlasamīpēna pōtaṁ gamayitvā bahunā kaṣṭēna kṣudranāvam arakṣāma|
17 Da mutanen suka jawo shi cikin babban jirgin ruwan, sai suka sa igiyoyi ta ƙarƙashin jirgin ruwan kanta don su ɗaɗɗaura shi. Don gudun kada a fyaɗa mu da yashin gaɓar Sirtis, sai suka saukar da ƙugiyar jirgin ruwan, suka bari aka yi ta tura jirgin haka.
tē tāmāruhya rajjcā pōtasyādhōbhāgam abadhnan tadanantaraṁ cēt pōtō saikatē lagatīti bhayād vātavasanānyamōcayan tataḥ pōtō vāyunā cālitaḥ|
18 Haka muka yi ta shan bugun guguwar hadarin nan kashegari suka fara jajjefar da kayan da jirgin yake ɗauke da su a cikin teku.
kintu kramaśō vāyōḥ prabalatvāt pōtō dōlāyamānō'bhavat parasmin divasē pōtasthāni katipayāni dravyāṇi tōyē nikṣiptāni|
19 A rana ta uku, da hannuwansu suka jefar da kayan aikin jirgin ruwan a cikin teku.
tr̥tīyadivasē vayaṁ svahastaiḥ pōtasajjanadravyāṇi nikṣiptavantaḥ|
20 Da dai aka yi kwana da kwanaki ba a ga rana ko taurari ba guguwar iska kuma ta ci gaba da bugowa, a ƙarshe muka fid da zuciya za mu tsira.
tatō bahudināni yāvat sūryyanakṣatrādīni samācchannāni tatō 'tīva vātyāgamād asmākaṁ prāṇarakṣāyāḥ kāpi pratyāśā nātiṣṭhat|
21 Bayan mutanen sun daɗe ba su ci abinci ba, Bulus ya miƙe tsaye a gabansu ya ce, “Mutane, da kun ji shawarata na kada ku tashi daga Kirit, da ba ku fāɗa wannan masifa da hasara ba.
bahudinēṣu lōkairanāhārēṇa yāpitēṣu sarvvēṣāṁ sākṣat paulastiṣṭhan akathayat, hē mahēcchāḥ krītyupadvīpāt pōtaṁ na mōcayitum ahaṁ pūrvvaṁ yad avadaṁ tadgrahaṇaṁ yuṣmākam ucitam āsīt tathā kr̥tē yuṣmākam ēṣā vipad ēṣō'pacayaśca nāghaṭiṣyētām|
22 Amma yanzu ina ƙarfafa ku ku yi ƙarfin hali, domin ba ɗayanku da zai rasa ransa; jirgin ruwan ne kaɗai zai hallaka.
kintu sāmprataṁ yuṣmān vinīya bravīmyahaṁ, yūyaṁ na kṣubhyata yuṣmākam ēkasyāpi prāṇinō hāni rna bhaviṣyati, kēvalasya pōtasya hāni rbhaviṣyati|
23 Jiya da dare wani mala’ikan Allahn da nake nasa nake kuma bauta wa ya tsaya kusa da ni
yatō yasyēśvarasya lōkō'haṁ yañcāhaṁ paricarāmi tadīya ēkō dūtō hyō rātrau mamāntikē tiṣṭhan kathitavān,
24 ya ce, ‘Kada ka ji tsoro, Bulus. Lalle za ka tsaya a gaban Kaisar a yi maka shari’a; Allah kuma cikin alherinsa ya ba ka dukan rayukan mutanen da suke tafiya tare da kai.’
hē paula mā bhaiṣīḥ kaisarasya sammukhē tvayōpasthātavyaṁ; tavaitān saṅginō lōkān īśvarastubhyaṁ dattavān|
25 Saboda haka ku yi ƙarfin hali, ku jama’a, gama gaskata Allah a kan cewa yadda aka faɗa mini ɗin nan, haka zai faru.
ataēva hē mahēcchā yūyaṁ sthiramanasō bhavata mahyaṁ yā kathākathi sāvaśyaṁ ghaṭiṣyatē mamaitādr̥śī viśvāsa īśvarē vidyatē,
26 Duk da haka, dole a fyaɗa mu a wani tsibiri.”
kintu kasyacid upadvīpasyōpari patitavyam asmābhiḥ|
27 A dare na goma sha huɗu iska dai tana ta korarmu a Tekun Adiriyatik, wajen tsakar dare sai masu tuƙin jirgin suka zaci sun yi kusa da ƙasa.
tataḥ param ādriyāsamudrē pōtastathaiva dōlāyamānaḥ san itastatō gacchan caturdaśadivasasya rātrē rdvitīyapraharasamayē kasyacit sthalasya samīpamupatiṣṭhatīti pōtīyalōkā anvamanyanta|
28 Sai suka gwada zurfin ruwan suka ga ya kai ƙafa ɗari da ashirin. Bayan ɗan lokaci kaɗan suka sāke gwadawa suka ga zurfin ya kai ƙafa tasa’in.
tatastē jalaṁ parimāya tatra viṁśati rvyāmā jalānīti jñātavantaḥ| kiñciddūraṁ gatvā punarapi jalaṁ parimitavantaḥ| tatra pañcadaśa vyāmā jalāni dr̥ṣṭvā
29 Don gudun kada a fyaɗa mu a kan duwatsu, sai suka saki ƙugiyoyin jirgin guda huɗu daga bayan jirgin suka yi fata gari ya waye.
cēt pāṣāṇē lagatīti bhayāt pōtasya paścādbhāgataścaturō laṅgarān nikṣipya divākaram apēkṣya sarvvē sthitavantaḥ|
30 Cikin ƙoƙarin tserewa daga jirgin, sai masu tuƙin jirgin suka saukar da ɗan ƙaramin jirgin ruwan cikin tekun, suka yi kamar za su saki waɗansu ƙugiyoyi daga sashen gaba na babban jirgin ne.
kintu pōtīyalōkāḥ pōtāgrabhāgē laṅgaranikṣēpaṁ chalaṁ kr̥tvā jaladhau kṣudranāvam avarōhya palāyitum acēṣṭanta|
31 Sai Bulus ya ce wa jarumin da kuma sojojin, “In mutanen nan ba su tsaya a cikin jirgin nan ba, ba za ku tsira ba.”
tataḥ paulaḥ sēnāpatayē sainyagaṇāya ca kathitavān, ētē yadi pōtamadhyē na tiṣṭhanti tarhi yuṣmākaṁ rakṣaṇaṁ na śakyaṁ|
32 Sai sojojin suka yayyanke igiyoyin da suke riƙe da ɗan ƙaramin jirgin, suka bar shi ya bi ruwa.
tadā sēnāgaṇō rajjūn chitvā nāvaṁ jalē patitum adadāt|
33 Kafin gari ya waye Bulus ya roƙe su duka su ci abinci. Ya ce, “Kwana goma sha huɗu ke nan, kuna zama cikin zulumi kun kuma kasance ba abinci, ba ku ci kome ba.
prabhātasamayē paulaḥ sarvvān janān bhōjanārthaṁ prārthya vyāharat, adya caturdaśadināni yāvad yūyam apēkṣamānā anāhārāḥ kālam ayāpayata kimapi nābhuṁgdhaṁ|
34 Ina roƙonku yanzu ku ci abinci. Kuna bukatarsa don ku rayu. Ba ɗayanku da zai rasa ko gashin kansa guda ɗaya.”
atō vinayē'haṁ bhakṣyaṁ bhujyatāṁ tatō yuṣmākaṁ maṅgalaṁ bhaviṣyati, yuṣmākaṁ kasyacijjanasya śirasaḥ kēśaikōpi na naṁkṣyati|
35 Bayan da ya faɗi haka, sai ya ɗauki burodi ya yi godiya ga Allah a gabansu duka. Sa’an nan ya gutsuttsura ya fara ci.
iti vyāhr̥tya paulaṁ pūpaṁ gr̥hītvēśvaraṁ dhanyaṁ bhāṣamāṇastaṁ bhaṁktvā bhōktum ārabdhavān|
36 Dukansu kuwa suka sami ƙarfafawa, suka kuma ci abinci.
anantaraṁ sarvvē ca susthirāḥ santaḥ khādyāni parpyagr̥hlan|
37 Dukanmu a jirgin kuwa mutane 276 ne.
asmākaṁ pōtē ṣaṭsaptatyadhikaśatadvayalōkā āsan|
38 Sa’ad da suka ci iyakar abin da suke so, sai suka rage nauyin jirgin ta wurin zubar da hatsin a cikin tekun.
sarvvēṣu lōkēṣu yathēṣṭaṁ bhuktavatsu pōtasthan gōdhūmān jaladhau nikṣipya taiḥ pōtasya bhārō laghūkr̥taḥ|
39 Da gari ya waye, ba su gane ƙasar da suke ba, amma suka ga wani lungu da gaci mai yashi, sai suka yanke shawara su kai jirgin can in za su iya.
dinē jātē'pi sa kō dēśa iti tadā na paryyacīyata; kintu tatra samataṭam ēkaṁ khātaṁ dr̥ṣṭvā yadi śaknumastarhi vayaṁ tasyābhyantaraṁ pōtaṁ gamayāma iti matiṁ kr̥tvā tē laṅgarān chittvā jaladhau tyaktavantaḥ|
40 Da suka yanke ƙugiyoyin, sai suka bar su a cikin teku a lokaci guda kuma suka ɓalle maɗaurin abin juya jirgin. Sai suka tā da filafilan gaban jirgin daidai yadda iska za tă tura shi gaba, sa’an nan suka nufi gaci.
tathā karṇabandhanaṁ mōcayitvā pradhānaṁ vātavasanam uttōlya tīrasamīpaṁ gatavantaḥ|
41 Amma jirgin ruwan ya shiga yashi ya kafe. Kan jirgin ya shiga cikin yashin ya kāsa motsi, sai jirgin ya fara farfashewa ta baya saboda haukan raƙuman ruwa.
kintu dvayōḥ samudrayōḥ saṅgamasthānē saikatōpari pōtē nikṣiptē 'grabhāgē bādhitē paścādbhāgē prabalataraṅgō'lagat tēna pōtō bhagnaḥ|
42 Sojojin suka yi niyya su kakkashe’yan kurkukun don hana waninsu yă yi iyo yă tsere.
tasmād bandayaścēd bāhubhistarantaḥ palāyantē ityāśaṅkayā sēnāgaṇastān hantum amantrayat;
43 Amma jarumin ya so yă ceci ran Bulus, sai ya hana su aiwatar da niyyarsu. Ya kuma yi umarni duk waɗanda suka iya ruwa su fara fāɗawa zuwa gaci.
kintu śatasēnāpatiḥ paulaṁ rakṣituṁ prayatnaṁ kr̥tvā tān taccēṣṭāyā nivartya ityādiṣṭavān, yē bāhutaraṇaṁ jānanti tē'grē prōllampya samudrē patitvā bāhubhistīrttvā kūlaṁ yāntu|
44 Sauran kuma su bi katakai zuwa can ko kuma a kan tarkacen jirgin ruwan. Ta haka kowa ya kai bakin teku lafiya.
aparam avaśiṣṭā janāḥ kāṣṭhaṁ pōtīyaṁ dravyaṁ vā yēna yat prāpyatē tadavalambya yāntu; itthaṁ sarvvē bhūmiṁ prāpya prāṇai rjīvitāḥ|

< Ayyukan Manzanni 27 >