< Ayyukan Manzanni 26 >

1 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
Agripa pa Pavlu reče: Dopušča ti se, da sam zase govoriš. Tedaj se je Pavel zagovarjal, stegnivši roko:
2 Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
Srečnega se štejem, kralj Agripa, da se imam danes pred teboj zagovarjati za vse, česar me Judje dolžé:
3 musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
Zlasti, ker vém, da poznaš vse šege in prepire, kteri so med Judi: za to te prosim, da bi me potrpežljivo poslušal.
4 “Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
Življenje torej moje od mladosti, kakošno je bilo od začetka med narodom mojim v Jeruzalemu, vedó vsi Judje,
5 Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
Poznajoč me od začetka (če hočejo pričati), da sem po najostrejšej ločinki vere naše živel ko Farizej.
6 Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
In sedaj stojim pred sodbo za voljo upanja obljube, ktero je obljubil Bog očetom našim;
7 Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
Ktero dvanajsteri rodovi naši, služeč Bogu noč in dan, upajo doseči. Za voljo tega upanja sem, kralj Agripa! tožen od Judov.
8 Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
Kaj? Neverjetno vam se zdí, da Bog mrtve obuja?
9 “Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
Tudi jaz sem sicer menil, da moram zoper ime Jezusa Nazarečana veliko nasprotnega storiti;
10 Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
Kar sem tudi storil v Jeruzalemu, in veliko svetih sem jaz v ječe zaprl, ko sem bil od vélikih duhovnov oblast prejel. In ko so jih morili, pristajal sem na sodbo.
11 Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
In po vseh shajališčih sem jih pogosto mučil in silil preklinjati: in neizmerno sem divjal zoper nje, in preganjal sem jih tudi noter do vnanjih mest;
12 “A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
In ko sem za tega voljo šel v Damask z oblastjo in dovoljenjem od vélikih duhovnov:
13 Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
O poldne na potu sem videl, kralj, z neba luč svetlejšo od svetlobe solnčne, ktera je obsijala mene in tiste, kteri so bili z menoj.
14 Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
In ko smo vsi padli na zemljo, slišal sem glas, da mi pravi v Hebrejskem jeziku: Savel! Savel! kaj me preganjaš? Težko ti je proti ostnu brcati.
15 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
Jaz sem pa rekel: Kdo si, Gospod? On pa reče: Jaz sem Jezus, kterega ti preganjaš.
16 Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
Ali vstani in stopi na noge svoje; za to namreč sem ti se prikazal, da te naredim za služabnika in pričo tega, kar si videl, in tega, v čemer ti se bom pokazoval;
17 Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
In otél te bom od ljudstva in poganov, med ktere te sedaj pošiljam,
18 ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
Da jim odpreš očí, da se izpreobrnejo od teme k luči, in od oblasti satanove k Bogu: da prejmó odpuščanje grehov, in delež med svetimi po veri, ktera je v mene.
19 “Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
Za to, kralj Agripa! nisem bil nepokoren nebeškej prikazni,
20 Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
Nego sem najprej tem, kteri so v Damasku in v Jeruzalemu, in po vsej deželi Judejskej, a po tem poganom oznanil, naj se spokoré in izpreobrnejo k Bogu, delajoč vredna dela pokore.
21 Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
Za tega voljo so me Judje v tempeljnu zgrabili in izkusili z rokami umoriti.
22 Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
Ali dobivši pomoč, ktera je od Boga, stojim do današnjega dné, in pričam malim in velikim, ne govoreč nič drugega nego, kar so govorili preroki, da se bo zgodilo, in Mojzes:
23 cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
Da bo Kristus trpel, in da bo, prvi iz vstajanja mrtvih, luč oznanjeval narodu in poganom.
24 A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
Ko je pa to odgovarjal, reče Fest z močnim glasom: Mešaš se, Pavel! Velika učenost tvoja ti jemlje um.
25 Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
On pa reče: Ne mešam se, vrli Fest, nego besede resnice in razumnosti govorim.
26 Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
Saj vé za to kralj, pred kterim tudi svobodno govorim; ne verujem namreč, da bi mu bilo od tega kaj neznano: kajti to se ni godilo v kotu.
27 Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
Veruješ, kralj Agripa, prerokom? Vém, da veruješ.
28 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
Agripa pa Pavlu reče: Malo, pa me boš pregovoril, da Kristjan postanem.
29 Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
Pavel pa reče: Želel bi od Boga, da, bodi si malo ali veliko, da ne bi samo ti, nego tudi vsi, kteri poslušajo danes, takošni bili, karkošen sem tudi jaz, razen vezî teh.
30 Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
In ko je to izgovoril, vstane kralj in poglavar, in Bernika, in kteri so ž njimi sedeli;
31 Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
In ko so bili na stran odšli, razgovarjali so se, govoreč: Ta človek ni nič smrti ali vezî vrednega storil.
32 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”
Agripa pa Festu reče: Izpustil bi se lahko ta človek, da se ni sklical na cesarja.

< Ayyukan Manzanni 26 >