< Ayyukan Manzanni 26 >
1 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
Agrippa sa da til Paulus: Du har lov til å tale om dig selv. Da strakte Paulus sin hånd ut og sa til sitt forsvar:
2 Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
Mot alt det som jøder anklager mig for, kong Agrippa, akter jeg mig lykkelig at jeg idag skal forsvare mig for dig,
3 musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
for du kjenner best alle skikker og spørsmål iblandt jødene; derfor ber jeg dig at du vil høre tålmodig på mig.
4 “Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
Mitt liv fra ungdommen av, som jeg fra første stund har levd iblandt mitt folk og i Jerusalem, kjenner alle jøder,
5 Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
da de forut vet om mig, like fra først av, om de bare vil komme frem med sitt vidnesbyrd, at jeg levde efter det strengeste parti av vår gudsdyrkelse, som fariseer.
6 Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
Og nu står jeg her og skal dømmes for håp på det løfte som av Gud er gitt fedrene,
7 Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
det som vårt tolvstamme-folk under uavlatelig gudstjeneste natt og dag håper å vinne frem til; for dette håp tiltales jeg av jøder, konge!
8 Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
Hvorfor aktes det for utrolig iblandt eder at Gud opvekker døde?
9 “Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
Jeg for min del trodde nu at jeg burde gjøre meget imot Jesu, nasareerens navn;
10 Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
det gjorde jeg også i Jerusalem, og både kastet jeg mange av de hellige i fengsel, efterat jeg hadde fått fullmakt av yppersteprestene, og når de skulde slåes ihjel, gav jeg min stemme til det,
11 Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
og omkring i alle synagogene tvang jeg dem ofte ved straff til å spotte, og jeg raste enn mere mot dem og forfulgte dem like til de utenlandske byer.
12 “A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
Under dette drog jeg da også til Damaskus med makt og myndighet fra yppersteprestene;
13 Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
og midt på dagen så jeg på veien, konge, et lys fra himmelen, klarere enn solen, stråle omkring mig og dem som reiste med mig,
14 Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
og da vi alle falt til jorden, hørte jeg en røst si til mig på det hebraiske mål: Saul! Saul! hvorfor forfølger du mig? det blir hårdt for dig å stampe mot brodden.
15 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
Jeg sa da: Hvem er du, Herre? Og Herren sa: Jeg er Jesus, han som du forfølger.
16 Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
Men reis dig op og stå på dine føtter! for derfor åpenbarte jeg mig for dig: for å utkåre dig til tjener og vidne både om det som du har sett, og om det for hvis skyld jeg vil åpenbare mig for dig,
17 Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
idet jeg frir dig ut fra folket og hedningene, som jeg sender dig til
18 ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
for å oplate deres øine, så de kan vende sig fra mørke til lys og fra Satans makt til Gud, forat de kan få syndenes forlatelse og arvelodd blandt dem som er helliget ved troen på mig.
19 “Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
Derfor, kong Agrippa, blev jeg ikke ulydig mot det himmelske syn;
20 Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
men både for dem i Damaskus først og for Jerusalem og i hele Judeas land og for hedningene forkynte jeg at de skulde omvende sig og komme tilbake til Gud og gjøre gjerninger som er omvendelsen verdige.
21 Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
For disse tings skyld grep nogen jøder mig i templet og søkte å slå mig ihjel.
22 Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
Så har jeg da fått hjelp fra Gud og står til denne dag og vidner både for liten og for stor, idet jeg ikke sier noget annet enn hvad profetene og Moses har sagt skulde skje:
23 cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
at Messias skulde lide, og at han som den første av de dødes opstandelse skulde forkynne lys for folket og for hedningene.
24 A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
Men da han forsvarte sig således, sier Festus med høi røst: Du er vanvittig, Paulus! din megen lærdom driver dig til vanvidd.
25 Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
Men han sier: Jeg er ikke vanvittig, mektigste Festus! men jeg taler sanne og sindige ord.
26 Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
For kongen kjenner til disse ting, og til ham taler jeg også frimodig; for jeg kan ikke tro at noget av dette er ukjent for ham; dette er jo ikke skjedd i en avkrok.
27 Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
Tror du, kong Agrippa, profetene? Jeg vet at du tror.
28 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
Men Agrippa sa til Paulus: Det mangler lite i at du overtaler mig til å bli en kristen.
29 Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
Paulus sa da: Jeg vilde ønske til Gud, enten det mangler lite eller meget, at ikke alene du, men også alle som hører mig idag, måtte bli slik som jeg er, bare uten disse lenker.
30 Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
Da stod kongen op, og landshøvdingen og Berenike og de som satt der med dem,
31 Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
og de gikk til side og talte med hverandre og sa: Denne mann gjør ikke noget som fortjener død eller lenker.
32 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”
Og Agrippa sa til Festus: Denne mann kunde være løslatt, om han ikke hadde innanket sin sak for keiseren.