< Ayyukan Manzanni 26 >

1 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
Titia Agrippa pora Paul ke koise, “Tumi nijor laga kotha kobole homoi di ase.” Titia Paul tai hath uthaikene tai nijor laga safai diya kotha koise.
2 Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
“Raja Agrippa, ji-ji kotha Yehudi khan moike bodnam lagai ase, aji apuni usorte utu laga sob jowab dibole homoi pa-a karone moi bisi khushi hoi ase;
3 musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
kelemane Yehudi khan laga niyom te kotha namila kora sob apuni jani thaka karone, aru moike morom kori nomro pora moi laga kotha huni bole anurodh kori ase.
4 “Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
Jineka ami chokra thaka homoi te Jerusalem pora nijor jati khan logote ahise, etu sob Yehudi khan jane.
5 Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
Taikhan jodi gawahi dibole mon thakile to shuru pora taikhan moike jani ase, moi Pharisee hoi kene taikhan laga dhorom te sob pora kara te choli ahise.
6 Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
Aru etiya moi yate khara koi kene bisar huwa to Isor ami laga baba khan ke ki kosom dise utu asha kora karone ase.
7 Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
Etu kosom ke pabo karone asha pora amikhan baroh-jati khan pura mon lagai kene raat-din Isor ke sewa kori ahise. Raja Agrippa, etu asha nimite he Yehudi khan moike golti lagai ase.
8 Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
Jitia Isor mora manu ke jinda kore, kele apnikhan etu to biswas kori bole nohoi bhabe?
9 “Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
Hosa ase, moi bhi Nazareth Jisu naam bhirodh te bisi kaam koribo lage bhabi ahise.
10 Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
Aru moi Jerusalem te eneka korise, mukhyo purohit khan pora hukum loi pobitro khan ke dhori bondhi ghor te haali kene morai diya te moi laga bhi itcha thakise.
11 Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
Aru moi sob mondoli te taikhan ke dukh di-dikene joborjosti kori thakise, khali etu he nohoi kintu bisi gusa hoi kene bahar laga sheher te bhi jai kene taikhan ke dukh digdar di thakise.
12 “A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
Jitia etu kori bole moi moha purohit khan pora hukum loi kene Damascus te jai thakise;
13 Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
aru titia rasta he, O Raja, din laga homoi te akas pora moi dikhise suryo pora bhi bisi ujala, moi aru ami laga logote jai thaka khan usorte chamkise.
14 Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
Aru jitia amikhan sob matite giri jaise, moi ekta awaj Ibrani bhasa te moike kowa hunise, ‘Saul, Saul tumi kele Moike digdar kori ase? Tumi dhar thaka te laat marile tumi karone bisi dukh hobo.’
15 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
Karone moi koise, ‘Probhu, Apuni kun ase?’ Aru Probhu pora koise, ‘Moi Jisu ase junke tumi digdar kori thake.’
16 Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
Kintu uthibi aru tumi laga theng te khara hobi; kelemane Moi aji tumi ki dikhise etu manu ke kobole aru aha kali bhi dikha bole thaka khan ke gawahi dibole dikhai dise;
17 Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
aru Moi tumike Yehudi aru Isor najana khan logote pathabo, aru taikhan hath pora tumike bachai thakibo,
18 ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
tumi pora taikhan laga suku khuli dibo aru taikhan andhar pora ujala te ani dibole, aru Saitan laga takot pora Isor phale ghurai anibole, paap pora khyama pabole, aru biswas pora pobitro khan logote ki jaga ase utu pabole.’
19 “Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
Karone, Raja Agrippa, moi etu sorgo darshan laga kotha ke namani kene chari diya nohoi;
20 Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
kintu poila moi Damascus te thaka khan ke koi dise, aru Jerusalem te thaka khan ke bhi, aru Judea sob te bhi, aru Isor najana khan ke bhi taikhan laga paap pora Isor phale ghuri ahibole, aru mon bodli huwa kaam khan kori bole koi dise.
21 Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
Kelemane etu karone Yehudi khan mondoli pora moike dhori loise, aru morai dibole hoise le.
22 Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
Kintu Isor laga modot pora aji tak yate khara hoi kene chutu, dangor sob usorte gawahi di aru Moses aru bhabobadi khan pora aha dinte ki hobole ase etu kotha kowa khan he nohoile dusra eku kowa nai-
23 cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
etu kotha Khrista bisi dukh koribo aru mora pora tai he prothom jee uthibo, Tai Yehudi khan aru Porjati khan logote puhor laga prochar koribo.
24 A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
Jitia Paul tai nijor kotha koi dise, Festus jor pora hala kori koise, “Paul, tumi pagla hoise; bisi sikha karone tumike pagla bonai dise.”
25 Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
Kintu Paul koise, “O mohan Festus, moi pagla nohoi, kintu hosa aru buddhi laga kotha koi ase.
26 Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
Raja bhi etu sob jani ase, moi eku bhoi nakori kene koi ase, aru etu kotha tai najana eneka ekta bhi kowa nai koi kene moi bhabi ase; etu ghatna to manu khan nathaka te kora nohoi.
27 Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
Raja Agrippa, apuni bhabobadi khan ke biswas kore? Hoi, moi jane, apuni biswas kori ase.”
28 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
Titia Agrippa Paul ke koise, “Olop homoi te, tumi aram pora moike Khristan bonai dibole ase?”
29 Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
Paul koise, “Isor logote moi anurodh kori ase, olop nohoile bisi homoi pichete hoilebi, aji apuni logote bohi ami laga kotha huni thaka sob bhi moi nisena hobole dibi, hoilebi jineka moike rusi pora bandhikena ase etu nisena nohoi.”
30 Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
Jitia tai etu kotha koise, titia Raja aru Governor aru Bernice, aru taikhan logote bohi thaka sob khara hoi jaise;
31 Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
aru taikhan alag jai kene nijor te kotha korise, aru koise, “Etu manu mori bole aru bandibole eneka eku biya kaam kora nohoi.”
32 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”
Titia Agrippa pora Festus ke koise, “Jodi etu manu Caesar logot anurodh nakorile, taike chari dile bhi hobole asele.”

< Ayyukan Manzanni 26 >