< Ayyukan Manzanni 26 >

1 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
And Agrippa said to Paul: Thou art permitted to speak in thy own behalf. Then Paul extended his hand, and made defence, saying:
2 Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
In regard to all the things of which I am accused by the Jews, king Agrippa, I consider myself highly favored, that I may this day make defence before thee:
3 musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
especially, as I know thee to be expert in all the controversies and laws of the Jews. I therefore request thee to hear me with indulgence.
4 “Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
The Jews themselves, if they would testify, know well my course of life from my childhood, which from the beginning was among my nation and in Jerusalem.
5 Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
For they have long been persuaded of me, and have known, that I lived in the princely doctrine of the Pharisees.
6 Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
And now, for the hope of the promise which was made by God to our fathers, I stand and am judged.
7 Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
To this hope, our twelve tribes hope to come, with earnest prayers by day and by night: and for this same hope, king Agrippa, I am accused by the Jews.
8 Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
How judge ye? Are we not to believe, that God will raise the dead?
9 “Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
For I myself, at first, resolved in my own mind, that I would perpetrate many adverse things against the name of Jesus the Nazarean.
10 Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
Which I also did at Jerusalem; and by the authority I received from the chief priests, I cast many of the saints into prison and when they were put to death by them, I took part with those that condemned them.
11 Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
And in every synagogue I tortured them, while I pressed them to become revilers of the name of Jesus. And in the great wrath, with which I was filled against them, I also went to other cities to persecute them.
12 “A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
And, as I was going for this purpose to Damascus, with the authority and license of the chief priests,
13 Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
at mid-day, on the road, I saw, O king, a light exceeding that of the sun, beaming from heaven upon me, and upon all those with me.
14 Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
And we all fell to the ground; and I heard a voice, which said to me, in Hebrew: Saul, Saul! why persecutest thou me? It will be a hard thing for thee to kick against the goads.
15 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
And I said: My Lord, who art thou? And our Lord said to me: I am Jesus the Nazarean, whom thou persecutest.
16 Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
And he said to me: Stand upon thy feet; for I have appeared to thee, for this purpose, to constitute thee a minister and a witness of this thy seeing me, and of thy seeing me hereafter.
17 Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
And I will deliver thee from the people of the Jews, and from other nations; to whom I send thee,
18 ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
to open their eyes; that they may turn from darkness to the light, and from the dominion of Satan unto God; and may receive remission of sins, and a portion with the saints, by faith in me.
19 “Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
Wherefore, king Agrippa, I did not contumaciously withstand the heavenly vision:
20 Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
but I preached from the first to them in Damascus, and to them in Jerusalem and in all the villages of Judaea; and I preached also to the Gentiles, that they should repent, and should turn to God, and should do the works suitable to repentance.
21 Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
And on account of these things, the Jews seized me in the temple, and sought to kill me.
22 Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
But unto this day God hath helped me; and lo, I stand and bear testimony, to the small and to the great; yet saying nothing aside from Moses and the prophets, but the very things which they declared were to take place:
23 cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
namely, that Messiah would suffer, and would become the first fruits of the resurrection from the dead; and that he would proclaim light to the people and to the Gentiles.
24 A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
And when Paul had extended his defence thus far, Festus cried, with a loud voice: Paul, thou art deranged: much study hath deranged thee.
25 Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
Paul replied to him: I am not deranged, excellent Festus; but speak words of truth and rectitude.
26 Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
And king Agrippa is also well acquainted with these things; and I therefore speak confidently before him, because I suppose not one of these things hath escaped his knowledge; for they were not done in secret.
27 Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
King Agrippa, believest thou the prophets? I know that thou believest.
28 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
King Agrippa said to him: Almost, thou persuadest me to become a Christian.
29 Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
And Paul said: I would to God, that not only thou, but likewise all that hear me this day, were almost, and altogether, as I am, aside from these bonds.
30 Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
And the king rose up, and the governor, and Bernice, and those who sat with them.
31 Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
And when they had gone out, they conversed with one another, and said: This man hath done nothing worthy of death or of bonds.
32 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”
And Agrippa said to Festus: The man might be set at liberty, if he had not announced an appeal to Caesar.

< Ayyukan Manzanni 26 >