< Ayyukan Manzanni 26 >
1 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
And Agrippa said to Paul, “It is permitted to you to speak for yourself”; then Paul having stretched forth the hand, was making a defense:
2 Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
“Concerning all things of which I am accused by Jews, King Agrippa, I have thought myself blessed, being about to make a defense before you today,
3 musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
especially knowing you to be acquainted with all things—both customs and questions—among Jews; for this reason, I implore you to hear me patiently.
4 “Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
The manner of my life then, indeed, from youth—which from the beginning was among my nation, in Jerusalem—all the Jews know,
5 Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
knowing me before from the first (if they may be willing to testify), that after the most exact sect of our worship, I lived a Pharisee;
6 Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
and now for the hope of the promise made to the fathers by God, I have stood judged,
7 Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
to which our twelve tribes, intently serving night and day, hope to come, concerning which hope I am accused, King Agrippa, by the Jews;
8 Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
why is it judged incredible with you if God raises the dead?
9 “Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
I indeed, therefore, thought with myself that it was necessary [for me] to do many things against the Name of Jesus of Nazareth,
10 Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
which I also did in Jerusalem, and I shut up many of the holy ones in prison, having received the authority from the chief priests; they also being put to death, I gave my vote against them,
11 Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
and in every synagogue, often punishing them, I was constraining [them] to speak evil, being also exceedingly mad against them, I was also persecuting [them] even to strange cities.
12 “A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
In which things, also, going on to Damascus—with authority and commission from the chief priests—
13 Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
at midday, I saw in the way, O king, out of Heaven, above the brightness of the sun, shining around me a light—and those going on with me;
14 Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
and we all having fallen to the earth, I heard a voice speaking to me, and saying in the Hebrew dialect, Saul, Saul, why do you persecute Me? [It is] hard for you to kick against goads!
15 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
And I said, Who are You, Lord? And He said, I am Jesus whom you persecute;
16 Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
but rise, and stand on your feet, for this I appeared to you, to appoint you an officer and a witness both of the things you saw, and of the things [in which] I will appear to you,
17 Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
delivering you from the people, and the nations, to whom I now send you,
18 ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
to open their eyes, to turn [them] from darkness to light, and [from] the authority of Satan to God, for their receiving forgiveness of sins, and a lot among those having been sanctified by faith that [is] toward Me.
19 “Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
After which, King Agrippa, I was not disobedient to the heavenly vision,
20 Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
but to those in Damascus first, and to those in Jerusalem, also to all the region of Judea, and to the nations, I was preaching to convert, and to turn back to God, doing works worthy of conversion;
21 Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
because of these things the Jews—having caught me in the temple—were endeavoring to kill [me].
22 Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
Having obtained, therefore, help from God, until this day, I have stood witnessing both to small and to great, saying nothing besides the things that both the prophets and Moses spoke of as about to come,
23 cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
that the Christ is to suffer, whether first by a resurrection from the dead, He is about to proclaim light to the people and to the nations.”
24 A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
And he thus making a defense, Festus said with a loud voice, “You are mad, Paul; much learning turns you mad!”
25 Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
And he says, “I am not mad, most noble Festus, but of truth and soberness I speak forth the sayings;
26 Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
for the king knows concerning these things, before whom I also speak boldly, for none of these things, I am persuaded, are hidden from him; for this thing has not been done in a corner;
27 Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
do you believe, King Agrippa, the prophets? I have known that you believe!”
28 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
And Agrippa said to Paul, “In [so] little you persuade me to become a Christian?”
29 Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
And Paul said, “I would have wished to God, both in a little, and in much, not only you, but also all those hearing me today, to become such as I also am—except these bonds.”
30 Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
And he having spoken these things, the king rose up, and the governor, Bernice also, and those sitting with them,
31 Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
and having withdrawn, they were speaking to one another, saying, “This man does nothing worthy of death or of bonds”;
32 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”
and Agrippa said to Festus, “This man might have been released if he had not appealed to Caesar.”