< Ayyukan Manzanni 26 >
1 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
And Agrippa said to Paul, It is permitted to thee to speak for thyself. Then Paul reaching forth his hand, proceeded with his defence:
2 Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
O king Agrippa, I consider myself happy, being about this day to make my defence before thee concerning all those things of which I am accused by the Jews:
3 musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
especially as thou art acquainted with all the customs and questions among the Jews: therefore I pray you to hear me patiently.
4 “Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
Moreover indeed all the Jews know my life from my youth; being from the beginning in my nation and in Jerusalem,
5 Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
knowing me originally, if they may be willing to testify, that according to the most rigid sect of our religion I lived a Pharisee.
6 Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
And now for the hope of the promise which is from God to our fathers, I stand being judged:
7 Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
unto which our twelve tribes constantly worshiping night and day, hope to attain: concerning which hope I am accused by the Jews, O king.
8 Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
Why is it judged by you incredible, if God shall raise the dead?
9 “Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
Moreover indeed, I thought to myself that I ought to do many things contrary to the name of Jesus the Nazarene:
10 Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
which I did also in Jerusalem, and shut up many of the saints in prison; and having received authority from the chief priests, and they being slain, I gave my vote against them;
11 Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
and throughout all the synagogues, frequently punishing them, I compelled them to blaspheme; and being exceeding mad against them, I was persecuting them even also unto foreign cities.
12 “A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
Meanwhile journeying to Damascus with power and authority of the chief priests, I saw on the way, O king,
13 Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
about midday, a light from heaven above the brightness of the sun, shining around me and those traveling with me;
14 Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
and we all having fallen to the ground, I heard a voice speaking to me in the Hebrew tongue, Saul, Saul, why persecutest thou me? it is hard for thee to kick against goads.
15 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
And I said, Who art thou, Lord? And the Lord said, I am Jesus whom thou art persecuting.
16 Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
But rise up, and stand upon thy feet: for unto this have I appeared unto thee, to make thee a minister and a martyr both of those things which thou hast seen, and of which I will appear unto thee;
17 Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
delivering thee from the people, and from the Gentiles, unto whom now I send thee,
18 ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
to open their eyes, to turn them from darkness unto light, and from the power of Satan unto God, in order that they may receive remission of sins, and an inheritance among those who are sanctified by faith in me.
19 “Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
Therefore, O king, I was not disobedient to the heavenly vision:
20 Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
but first to those in Damascus, and also in Jerusalem, and throughout all the country of Judea, and to the Gentiles, I was preaching that they should repent and turn to God, doing things worthy of repentance.
21 Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
On account of these things the Jews, taking me while in the temple, endeavored to kill me.
22 Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
Then having received help from God, I have stood unto this day, witnessing both to small and great, saying nothing but what the prophets and Moses said were about to come to pass:
23 cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
how that Christ must suffer, how being the first from the resurrection of the dead, he is to proclaim light both to the people, and the Gentiles.
24 A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
And he making his defence to these things, Festus says with a loud voice, O Paul, thou art beside thyself; many writings turned thee into insanity.
25 Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
But Paul says, I am not a maniac, most noble Festus; but I speak forth the words of truth and soberness.
26 Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
For the king, to whom I also speak boldly, knows concerning these things: for I am persuaded that nothing of these things is hidden; for this has not been done in a corner.
27 Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
O king Agrippa, dost thou believe the prophets? I know that thou believest them.
28 Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
And Agrippa said to Paul, With little persuasion thou dost persuade thyself to make me a Christian.
29 Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
And Paul said, I would to God, that both in little and in much, not only you, but also all of those hearing me this day, were such as I am, except these bonds.
30 Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
And the king, and the governor, and Bernice, and those sitting with them, arose up:
31 Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
and having gone away, they were talking to one another, saying, that This man is doing nothing worthy of death or of bonds.
32 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”
But Agrippa said to Festus, This man was able to have been released, if he had not appealed to Caesar.