< Ayyukan Manzanni 25 >
1 Kwana uku bayan isowa a lardin, sai Festus ya haura daga Kaisariya zuwa Urushalima,
Kolm päeva pärast ametisse astumist läks Festus Kaisareast üles Jeruusalemma,
2 inda manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka bayyana a gabansa suka kuma gabatar da ƙararsu a kan Bulus.
kus ülempreestrid ja juutide juhid astusid tema ette ja esitasid süüdistuse Pauluse vastu.
3 Suka roƙi Festus a gaggauce a matsayin alfarma gare su, da yă sa a mai da Bulus Urushalima, gama sun’yan kwanto su kashe shi a hanya.
Nad palusid Festust hea tahte märgiks saata Paulus Jeruusalemma, sest nad plaanisid teda tee peal rünnata ja tappa.
4 Festus ya amsa ya ce, “Bulus yana tsare a Kaisariya, ni da kaina kuma zan je can ba da daɗewa ba.
Aga Festus vastas: „Paulust hoitakse Kaisareas ja ma ise lähen ka varsti sinna.
5 Ku sa waɗansu daga cikin shugabanninku su tafi tare da ni su kawo ƙararsu a kan mutumin a can, in ya aikata wani laifi.”
Tulgu mõni teie juhtidest minuga kaasa ja esitagu tema vastu süüdistus seal, kui ta on midagi valesti teinud.“
6 Bayan ya yi kwanaki takwas ko goma tare da su, sai ya gangara zuwa Kaisariya, kashegari kuma ya kira a yi zaman kotu ya kuma umarta a kawo Bulus a gabansa.
Kui Festus oli seitse või kaheksa päeva nende juures olnud, läks ta alla Kaisareasse. Järgmisel päeval kutsus ta kokku kohtu ja käskis Pauluse tema ette tuua.
7 Da Bulus ya bayyana, sai Yahudawan da suka gangaro daga Urushalima suka tsaya kewaye shi, suna kawo ƙarar masu tsanani da yawa a kansa, waɗanda ba su iya tabbatarwa ba.
Kui Paulus sisse astus, piirasid ta ümber Jeruusalemmast tulnud juudid. Nad esitasid talle palju tõsiseid süüdistusi, kuid ei suutnud neid tõestada.
8 Sa’an nan Bulus ya kāre kansa ya ce, “Ban aikata wani laifi game da dokokin Yahudawa ko game da haikali ko kuma game da Kaisar ba.”
Siis kaitses Paulus ennast: „Ma ei ole teinud midagi valesti ei juutide Seaduse ega templi ega keisri vastu.“
9 Festus, da yake yana so yă yi wa Yahudawa alfarma, sai ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a gabana a kan waɗannan zarge?”
Festus aga, soovides olla juutidele meelepärane, küsis: „Kas sa oled nõus minema nende süüdistustega üles Jeruusalemma ja astuma minu ette kohtus?“
10 Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai.
Paulus vastas: „Mina seisan praegu keisri kohtujärje ees, kus mu üle peab kohut mõistetama. Juutide vastu ma ei ole eksinud, nagu sa isegi hästi tead.
11 In kuwa ina da wani laifin da ya isa kisa, ban ƙi in mutu ba. Amma in ƙarar da waɗannan Yahudawa suka kawo a kaina ba gaskiya ba ne, ba wanda yake da iko ya ba da ni a gare su. Na ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar!”
Kui ma olen siiski süüdi selles, et olen teinud midagi surma väärivat, ei keeldu ma surmast. Kuid kui nende poolt minu vastu esitatud süüdistused ei vasta tõele, ei ole kellelgi õigust mind neile välja anda. Mina nõuan keisri kohut!“
12 Bayan Festus ya yi shawara da majalisarsa sai ya ce, “Ka ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar. To, ga Kaisar kuwa za ka tafi!”
Pärast seda, kui Festus oli arutanud oma nõunikega, ta vastas: „Keisri kohut oled sa nõudnud, keisri ette sa lähed!“
13 Bayan’yan kwanaki sai Sarki Agiriffa da Bernis suka iso Kaisariya don su yi wa Festus gaisuwar bangirma.
Mõni päev hiljem saabusid Kaisareasse kuningas Agrippa ja Berenike Festust tervitama.
14 Da yake za su yi kwanaki da dama a can, sai Festus ya tattauna batun Bulus da sarki. Ya ce, “Akwai mutumin da Felis ya bari a daure.
Ja kuna nad veetsid seal mitu päeva, rääkis Festus kuningale Pauluse juhtumist. Ta ütles: „Feeliks on jätnud vangi ühe mehe.
15 Sa’ad da na je Urushalima, manyan firistoci da dattawan Yahudawa suka kawo ƙara game da shi suka kuma nema a hukunta shi.
Kui ma läksin Jeruusalemma, esitasid juudi ülempreestrid ja rahvavanemad tema vastu süüdistuse ja nõudsid tema surmamõistmist.
16 “Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu.
Ma vastasin neile, et Roomas ei ole kombeks kedagi välja anda, enne kui süüdistatav saab seista vastamisi süüdistajatega ja ennast süüdistuste vastu kaitsta.
17 Da suka zo nan tare da ni, ban yi wani jinkiri ba, na kira zaman kotu kashegari kuma na umarta a kawo mutumin.
Kui nad koos minuga siia tulid, ei lükanud ma kohtuasja edasi, vaid kutsusin kohtu järgmisel päeval kokku ja käskisin mehe sisse tuua.
18 Sa’ad da masu zarginsa suka tashi tsaye don su yi magana, ba su zarge shi da wani laifin da na yi tsammani ba.
Aga kui tema süüdistajad rääkima hakkasid, ei esitanud nad temale süüdistust üheski sellises kuriteos, nagu mina ootasin.
19 A maimako haka, sai suka kawo waɗansu’yan maganganu game da addininsu da ba su yarda da shi ba da kuma game da wani Yesu da ya mutu wanda Bulus ya ce yana da rai.
Selle asemel oli neil temaga vaidlus nende oma usu ja kellegi surnud Jeesuse suhtes, kelle kohta Paulus väitis, et ta on elus.
20 Na rasa yadda zan bincike irin abubuwan nan; saboda haka na yi tambaya ko zai yarda ya tafi Urushalima a yi masa shari’a a can game da waɗannan zargi.
Ma olin nõutu, kuidas selliseid asju uurida; nii et ma küsisin, kas ta on valmis minema Jeruusalemma ja astuma seal nendes süüdistustes kohtu ette.
21 Da Bulus ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Babban Sarki sai na umarta a tsare shi har kafin in aika shi zuwa ga Kaisar.”
Aga kui Paulus nõudis, et see asi tuleb üle anda keisrile otsutamiseks, siis ma käskisingi teda kinni pidada, kuni ma võin ta saata keisri juurde.“
22 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Ni ma zan so in saurari mutumin da kaina.” Sai ya amsa ya ce, “Za ka kuwa ji shi gobe.”
Siis ütles Agrippa Festusele: „Ma tahaksin seda meest ise kuulda.“Ta vastas: „Homme saad teda kuulda.“
23 Kashegari Agiriffa da Bernis suka yi shiga irin ta sarauta suka shiga ɗakin jama’a tare da manyan sojoji da manyan mutanen birni. Da umarnin Festus, sai aka shigo da Bulus.
Järgmisel päeval tulid Agrippa ja Berenike kogu oma vürstlikus hiilguses ja astusid kohtusaali koos kõrgete väepealike ja linna tähtsate meestega. Siis toodi Festuse käsul Paulus.
24 Sai Festus ya ce, “Sarki Agiriffa, da kuma dukan waɗanda suke tare da mu, kun ga wannan mutum! Dukan jama’ar Yahudawa sun kawo mini kararsa a Urushalima da kuma a nan Kaisariya, suna kururuwa suna cewa bai kamata a bar shi da rai ba.
Festus ütles: „Kuningas Agrippa ja kõik, kes te siin meiega olete, te näete seda meest! Terve juudi kogukond on nõudnud minult Jeruusalemmas ja siin, Kaisareas, karjudes, et ta ei tohi enam elada.
25 Ban same shi da wani laifin da ya isa kisa ba, amma saboda ya ɗaukaka ƙararsa zuwa gaban Babban Sarki sai na yanke shawara in aika da shi Roma.
Mina aga leidsin, et ta pole teinud midagi surma väärivat, kuid kuna ta ise nõudis keisri kohut, siis ma otsustasin ta sinna saata.
26 Ba ni da wata tabbatacciyar maganar da zan rubuta wa Mai Girma game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku duka, musamman a gabanka, Sarki Agiriffa, saboda a sakamakon wannan bincike zan iya samun abin da zan rubuta.
Aga mul pole midagi tema kohta Tema Majesteedile kirjutada. Seepärast ma olen toonud ta teie ette ja eriti sinu ette, kuningas Agrippa, et mul pärast juurdlust oleks midagi kirjutada.
27 Don a ganina wauta ce a aika da ɗan kurkuku ba tare da an nuna zargin da ake yi a kansa ba.”
Sest mulle tundub mõttetu saata vang Rooma ilma süüdistuste loetelu esitamata.“