< Ayyukan Manzanni 25 >

1 Kwana uku bayan isowa a lardin, sai Festus ya haura daga Kaisariya zuwa Urushalima,
Festus, [who was now the governor] of the province, arrived in Caesarea, and three days later he went up to Jerusalem.
2 inda manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka bayyana a gabansa suka kuma gabatar da ƙararsu a kan Bulus.
In Jerusalem, the chief priests and [other] Jewish leaders formally told [Festus] about [the things that they said] that Paul [had done that were wrong].
3 Suka roƙi Festus a gaggauce a matsayin alfarma gare su, da yă sa a mai da Bulus Urushalima, gama sun’yan kwanto su kashe shi a hanya.
They urgently asked Festus to do something for them. [They asked him to command soldiers] to bring Paul to Jerusalem, [so that Festus could put him on trial there]. But they were planning that some [of them] would hide [near the road] and wait [for Paul] and kill him when he was traveling [to Jerusalem].
4 Festus ya amsa ya ce, “Bulus yana tsare a Kaisariya, ni da kaina kuma zan je can ba da daɗewa ba.
But Festus replied, “Paul is in Caesarea, and is being guarded {[soldiers] are guarding him} [there]. I myself will go down to Caesarea in a few days.
5 Ku sa waɗansu daga cikin shugabanninku su tafi tare da ni su kawo ƙararsu a kan mutumin a can, in ya aikata wani laifi.”
Choose some of your leaders to go there with me. [While they are there], they can accuse Paul of the wrong things that you say that he has done.”
6 Bayan ya yi kwanaki takwas ko goma tare da su, sai ya gangara zuwa Kaisariya, kashegari kuma ya kira a yi zaman kotu ya kuma umarta a kawo Bulus a gabansa.
After Festus had been [in Jerusalem] eight or ten days, he went back down to Caesarea. [Several of the Jewish leaders also went there]. The next day Festus [commanded] that Paul be brought {someone to bring Paul} to him [in the assembly hall] so that he could judge him.
7 Da Bulus ya bayyana, sai Yahudawan da suka gangaro daga Urushalima suka tsaya kewaye shi, suna kawo ƙarar masu tsanani da yawa a kansa, waɗanda ba su iya tabbatarwa ba.
[After] Paul was brought to [the assembly hall], the Jewish [leaders] from Jerusalem gathered around him [to accuse him]. They told [Festus] that Paul had committed many crimes. But they could not prove [that Paul had done the things about which they accused him].
8 Sa’an nan Bulus ya kāre kansa ya ce, “Ban aikata wani laifi game da dokokin Yahudawa ko game da haikali ko kuma game da Kaisar ba.”
Then Paul [spoke] to defend himself. He said to Festus, “I have done nothing wrong against the laws of us [(exc)] Jews, and I have not disobeyed the rules concerning our Temple. I have also done nothing wrong against your government [MTY].”
9 Festus, da yake yana so yă yi wa Yahudawa alfarma, sai ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a gabana a kan waɗannan zarge?”
But Festus wanted to please the Jewish [leaders, so] he asked Paul, “Are you [(sg)] willing to go up to Jerusalem so that I can listen as these men accuse you [there]?”
10 Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai.
But Paul [did not want to do that. So] he said [to Festus], “[No], I [am not willing to go to Jerusalem]! I am [now] standing before you, and you [(sg)] are the judge [whom the Roman] Emperor [MTY] [has authorized. This is the place] where I should be judged {where you should judge me}. I have not wronged the Jewish people [at all], as you know very well.
11 In kuwa ina da wani laifin da ya isa kisa, ban ƙi in mutu ba. Amma in ƙarar da waɗannan Yahudawa suka kawo a kaina ba gaskiya ba ne, ba wanda yake da iko ya ba da ni a gare su. Na ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar!”
If I had done something bad [for which I] should be executed {[concerning which the law said that they] should execute me}, I would not plead [with them that they] not kill me. But none of these things about which they accuse me is [true, so] no one can [legally] surrender me to [these Jews]. So I formally request that the emperor [MTY] [should judge me at Rome].”
12 Bayan Festus ya yi shawara da majalisarsa sai ya ce, “Ka ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar. To, ga Kaisar kuwa za ka tafi!”
Then after Festus conferred with the [men who regularly] advised him, he replied to Paul, “You [(sg)] have formally requested [that I should send you] to the emperor [in Rome. So I will arrange for] you to go there [in order that he can judge you].”
13 Bayan’yan kwanaki sai Sarki Agiriffa da Bernis suka iso Kaisariya don su yi wa Festus gaisuwar bangirma.
After several days, King [Herod] Agrippa arrived at Caesarea, along with [his younger sister] Bernice. They had come to [formally] welcome Festus [as the new Governor of the province].
14 Da yake za su yi kwanaki da dama a can, sai Festus ya tattauna batun Bulus da sarki. Ya ce, “Akwai mutumin da Felis ya bari a daure.
King Agrippa and Bernice stayed many days in Caesarea. While [they were] there, Festus told Agrippa about Paul. He said to the king, “There is a man here whom Felix kept in prison [while he was governor]. He left him [there when his time as governor ended].
15 Sa’ad da na je Urushalima, manyan firistoci da dattawan Yahudawa suka kawo ƙara game da shi suka kuma nema a hukunta shi.
When I went to Jerusalem, the chief priests and [the other] Jewish elders told me that this man had done many things [against their laws]. They asked me to condemn him [to be executed] {judge him [so that people could kill him]}.
16 “Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu.
But I told them that when someone has been accused [of a crime, we] Romans do not immediately (condemn that person/declare that person to be guilty). First, we [command] him to stand before the people who are accusing him and to say whether or not he has done those things. [After that, the judge will decide what to do with] him.
17 Da suka zo nan tare da ni, ban yi wani jinkiri ba, na kira zaman kotu kashegari kuma na umarta a kawo mutumin.
So those Jews came [here to Caesarea] when I came. I did not delay. The day after [we(exc) arrived], after I sat down at the place where I make decisions, I [commanded] that Paul be brought {[soldiers] to bring Paul} into [the courtroom].
18 Sa’ad da masu zarginsa suka tashi tsaye don su yi magana, ba su zarge shi da wani laifin da na yi tsammani ba.
The Jewish leaders did accuse him, but the things about which they accused him were not any of the [evil] crimes about which I thought [they would accuse him].
19 A maimako haka, sai suka kawo waɗansu’yan maganganu game da addininsu da ba su yarda da shi ba da kuma game da wani Yesu da ya mutu wanda Bulus ya ce yana da rai.
Instead, what they argued about with him were some teachings that [some] Jews believe [and others do not believe. They argued] about a man whose name was Jesus who had died, [but the man they were accusing, whose name is] Paul, kept saying, ‘Jesus is alive again.’
20 Na rasa yadda zan bincike irin abubuwan nan; saboda haka na yi tambaya ko zai yarda ya tafi Urushalima a yi masa shari’a a can game da waɗannan zargi.
I did not know what questions to ask [them, and I did not know how to judge] concerning their dispute. So I asked Paul, ‘Are you [(sg)] willing to go [back] to Jerusalem and have the dispute [between you and these Jews] judged there {and [let me] judge there the dispute [between you and these Jews]}?’
21 Da Bulus ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Babban Sarki sai na umarta a tsare shi har kafin in aika shi zuwa ga Kaisar.”
But Paul answered, ‘[No]. I [am not willing to go to Jerusalem]!
22 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Ni ma zan so in saurari mutumin da kaina.” Sai ya amsa ya ce, “Za ka kuwa ji shi gobe.”
Agrippa said to Festus, “I also would like to hear the man myself.”
23 Kashegari Agiriffa da Bernis suka yi shiga irin ta sarauta suka shiga ɗakin jama’a tare da manyan sojoji da manyan mutanen birni. Da umarnin Festus, sai aka shigo da Bulus.
The next day Agrippa and Bernice came very ceremoniously to the assembly hall. Some [Roman] commanders and prominent men in [Caesarea] came with them. Then, Festus told an officer to bring Paul. So after the officer [went to the prison and] brought him,
24 Sai Festus ya ce, “Sarki Agiriffa, da kuma dukan waɗanda suke tare da mu, kun ga wannan mutum! Dukan jama’ar Yahudawa sun kawo mini kararsa a Urushalima da kuma a nan Kaisariya, suna kururuwa suna cewa bai kamata a bar shi da rai ba.
Festus said, “King Agrippa, and all [the rest of you] who are here, you see this man. Many [HYP] Jews in Jerusalem and also those here [in Caesarea] appealed to me, screaming that we [(exc)] should not let him live any longer.
25 Ban same shi da wani laifin da ya isa kisa ba, amma saboda ya ɗaukaka ƙararsa zuwa gaban Babban Sarki sai na yanke shawara in aika da shi Roma.
But [when I asked them to tell me what he had done, and they told me], I found out that he had not done anything for which he should be executed {[anyone should] execute him}. However, he has asked that our emperor [should judge his case], so I have decided to send him to Rome.
26 Ba ni da wata tabbatacciyar maganar da zan rubuta wa Mai Girma game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku duka, musamman a gabanka, Sarki Agiriffa, saboda a sakamakon wannan bincike zan iya samun abin da zan rubuta.
But I do not know what specifically I should write to the emperor concerning him. That is why I have brought him here. I [want] you all [to hear him speak], and I especially want you [(sg)], King Agrippa, to hear him. Then, after we [(inc)] have questioned him, I may know what I should write [to the emperor about him].
27 Don a ganina wauta ce a aika da ɗan kurkuku ba tare da an nuna zargin da ake yi a kansa ba.”
It seems to me [that it would be] unreasonable to send a prisoner [to the emperor in Rome without my] specifying the [things about which people] are accusing him.”

< Ayyukan Manzanni 25 >