< Ayyukan Manzanni 25 >
1 Kwana uku bayan isowa a lardin, sai Festus ya haura daga Kaisariya zuwa Urushalima,
Festus therefore having come into the province, after three days went up from Caesarea to Jerusalem.
2 inda manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka bayyana a gabansa suka kuma gabatar da ƙararsu a kan Bulus.
And the chief priests and the leaders of the Jews brought a complaint before him against Paul, and besought him,
3 Suka roƙi Festus a gaggauce a matsayin alfarma gare su, da yă sa a mai da Bulus Urushalima, gama sun’yan kwanto su kashe shi a hanya.
asking for themselves a favor against him, that he would send for him to Jerusalem, intending to place men in wait to kill him on the road.
4 Festus ya amsa ya ce, “Bulus yana tsare a Kaisariya, ni da kaina kuma zan je can ba da daɗewa ba.
But Festus answered that Paul was in custody at Caesarea, and that he himself was going thither shortly.
5 Ku sa waɗansu daga cikin shugabanninku su tafi tare da ni su kawo ƙararsu a kan mutumin a can, in ya aikata wani laifi.”
Let those therefore, said he, who have authority among you, go down with me and accuse this man, if he is guilty of anything.
6 Bayan ya yi kwanaki takwas ko goma tare da su, sai ya gangara zuwa Kaisariya, kashegari kuma ya kira a yi zaman kotu ya kuma umarta a kawo Bulus a gabansa.
And having tarried among them not more than eight or ten days, he went down to Caesarea; and on the morrow, sitting on the judgment-seat, ordered Paul to be brought.
7 Da Bulus ya bayyana, sai Yahudawan da suka gangaro daga Urushalima suka tsaya kewaye shi, suna kawo ƙarar masu tsanani da yawa a kansa, waɗanda ba su iya tabbatarwa ba.
And when he had come, the Jews who came down from Jerusalem stood around, bringing many and heavy charges which they could not prove;
8 Sa’an nan Bulus ya kāre kansa ya ce, “Ban aikata wani laifi game da dokokin Yahudawa ko game da haikali ko kuma game da Kaisar ba.”
while Paul said in his defence, Neither against the law of the Jews, nor against the temple, nor against Caesar have I committed any offence.
9 Festus, da yake yana so yă yi wa Yahudawa alfarma, sai ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a gabana a kan waɗannan zarge?”
But Festus, wishing to gain favor with the Jews, answered Paul and said, Art thou willing to go up to Jerusalem, and there be tried on these charges before me?
10 Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai.
But Paul said, I stand at the judgment-seat of Caesar, where I ought to be tried. To the Jews I have done no wrong, as thou also very well knowest.
11 In kuwa ina da wani laifin da ya isa kisa, ban ƙi in mutu ba. Amma in ƙarar da waɗannan Yahudawa suka kawo a kaina ba gaskiya ba ne, ba wanda yake da iko ya ba da ni a gare su. Na ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar!”
If indeed I am an offender, and have done anything deserving death, I refuse not to die; but if there be nothing in the charges which they bring against me, no man can give me up to them. I appeal to Caesar.
12 Bayan Festus ya yi shawara da majalisarsa sai ya ce, “Ka ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar. To, ga Kaisar kuwa za ka tafi!”
Then Festus having conferred with the council, answered, Thou hast appealed to Caesar; to Caesar shalt thou go.
13 Bayan’yan kwanaki sai Sarki Agiriffa da Bernis suka iso Kaisariya don su yi wa Festus gaisuwar bangirma.
And after some days Agrippa the king and Bernice came to Caesarea to greet Festus.
14 Da yake za su yi kwanaki da dama a can, sai Festus ya tattauna batun Bulus da sarki. Ya ce, “Akwai mutumin da Felis ya bari a daure.
And while they were making a stay of some days there, Festus laid the case of Paul before the king, saying, There is a certain man left in bonds by Felix,
15 Sa’ad da na je Urushalima, manyan firistoci da dattawan Yahudawa suka kawo ƙara game da shi suka kuma nema a hukunta shi.
against whom, when I was at Jerusalem, the chief priests and the elders of the Jews brought a complaint, asking for judgment against him.
16 “Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu.
To whom I answered, It is not the custom of the Romans to give up any man on a charge, before the accused hath the accusers face to face, and hath opportunity to answer for himself concerning the crime laid against him.
17 Da suka zo nan tare da ni, ban yi wani jinkiri ba, na kira zaman kotu kashegari kuma na umarta a kawo mutumin.
When therefore they had come together here, without any delay I sat on the judgment-seat on the day after, and ordered the man to be brought forward.
18 Sa’ad da masu zarginsa suka tashi tsaye don su yi magana, ba su zarge shi da wani laifin da na yi tsammani ba.
And his accusers standing around him brought no accusation of such things as I had conjectured,
19 A maimako haka, sai suka kawo waɗansu’yan maganganu game da addininsu da ba su yarda da shi ba da kuma game da wani Yesu da ya mutu wanda Bulus ya ce yana da rai.
but had against him certain questions of their own religion, and of one Jesus that was dead, whom Paul affirmed to be alive.
20 Na rasa yadda zan bincike irin abubuwan nan; saboda haka na yi tambaya ko zai yarda ya tafi Urushalima a yi masa shari’a a can game da waɗannan zargi.
And I being at a loss about such questions, asked him if he was willing to go to Jerusalem and there be put on trial for these matters.
21 Da Bulus ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Babban Sarki sai na umarta a tsare shi har kafin in aika shi zuwa ga Kaisar.”
But Paul having appealed to be kept in custody for the judgment of Augustus, I ordered him to be kept till I should send him up to Caesar.
22 Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Ni ma zan so in saurari mutumin da kaina.” Sai ya amsa ya ce, “Za ka kuwa ji shi gobe.”
Then Agrippa said to Festus, I should like to hear the man myself. Tomorrow, said he, thou shalt hear him.
23 Kashegari Agiriffa da Bernis suka yi shiga irin ta sarauta suka shiga ɗakin jama’a tare da manyan sojoji da manyan mutanen birni. Da umarnin Festus, sai aka shigo da Bulus.
Accordingly on the morrow Agrippa and Bernice came with great pomp, and entered into the place of hearing, with the chief captains and principal men of the city, and at the order of Festus Paul was brought forward.
24 Sai Festus ya ce, “Sarki Agiriffa, da kuma dukan waɗanda suke tare da mu, kun ga wannan mutum! Dukan jama’ar Yahudawa sun kawo mini kararsa a Urushalima da kuma a nan Kaisariya, suna kururuwa suna cewa bai kamata a bar shi da rai ba.
And Festus said: King Agrippa, and all men who are here present with us! Ye see this man about whom the whole multitude of the Jews applied to me both at Jerusalem and here, crying out that he ought no longer to live.
25 Ban same shi da wani laifin da ya isa kisa ba, amma saboda ya ɗaukaka ƙararsa zuwa gaban Babban Sarki sai na yanke shawara in aika da shi Roma.
But having found that he had done nothing deserving death, and he himself having appealed to Augustus, I determined to send him;
26 Ba ni da wata tabbatacciyar maganar da zan rubuta wa Mai Girma game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku duka, musamman a gabanka, Sarki Agiriffa, saboda a sakamakon wannan bincike zan iya samun abin da zan rubuta.
and as I have nothing certain to write about him to the emperor, I have brought him forward before you, and specially before thee, king Agrippa, that when the examination hath been made, I may have something to write.
27 Don a ganina wauta ce a aika da ɗan kurkuku ba tare da an nuna zargin da ake yi a kansa ba.”
For it seemeth to me unreasonable to send a prisoner and not signify the charges against him;