< Ayyukan Manzanni 24 >
1 Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
And, after five days, came down the High-priest Ananias, with certain Elders and a certain orator Tertullus, and they informed the governor against Paul.
2 Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
And, when he was called, Tertullus began to make accusation, saying—Seeing that, great peace, we are obtaining through thee, and that, reforms, are being brought about for this nation through thy forethought,
3 Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
both in all ways and in all places, are we accepting it, most excellent Felix, with all thankfulness.
4 Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
But, lest I too long detain thee, I beseech thee to hear us concisely in thy considerateness.
5 “Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
For, finding this man a pest, and moving sedition with all the Jews that are throughout the inhabited earth, a leader also of the sect of the Nazarenes, —
6 har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
who also attempted to desecrate even, the temple, whom we also seized,
8 Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
from whom thou shall be able, thyself, by making examination concerning all these things, to ascertain the things of which, we, are accusing him.
9 Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
Moreover, the Jews also were joining in the attack, saying that, these things, were, so.
10 Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
And Paul answered, when the governor had motioned him to be speaking, —Well knowing thee to have been, for many years, judge unto his nation, cheerfully, as to the things concerning myself, do I make defence;
11 Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
seeing thou art able to ascertain, that there are, not more, than twelve days, since I went up to worship in Jerusalem, —
12 Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
and neither, in the temple, found they me, with any one, disputing, or causing, a halt, of the multitude, either in the synagogues or throughout the city, —
13 Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
neither can they make good the things concerning which they are, now, accusing me.
14 Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
But I confess, this, unto thee, —That, according to the Way which they call a Sect, so, I am rendering divine service unto my father’s God, believing in all the things which, throughout the law, and those which, in the prophets, are written:
15 ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
Having, hope, towards God, which, even these themselves, do entertain—that, a resurrection, there shall certainly be, both of righteous and of unrighteous:
16 Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
herein, even I, myself, am studying to have, an unoffending conscience, towards God and men, continually.
17 “Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
Now, after many years, intending to do, alms, unto my nation, I arrived, —also [to present] offerings; among which they found me, purified in the temple, not with a multitude, nor with tumult;
18 Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
but certain Jews from Asia [caused it], —
19 Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
who ought, before thee, to have presented themselves, and to have been laying accusation, if, anything, they might have had against me: —
20 Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
Or, let, these themselves, say what wrong they found, when I stood before the High-council, —
21 sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
unless concerning this one voice, wherewith I cried aloud among them, as I stood—Concerning the raising of the dead, am, I, to be judged, this day, by you.
22 Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
And Felix deferred them, having more exact knowledge concerning the Way, —saying—As soon as, Lysias the captain, hath come down, I will give judgment as to your affairs, —
23 Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
giving orders unto the centurion, that he should be kept, and have a measure of liberty, and to be hindering, none, of his own from waiting upon him.
24 Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
And, after certain days, Felix having arrived, with Drusilla his own wife, who was, a Jewess, he sent for Paul, and heard him concerning the faith, respecting Christ Jesus.
25 Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
And, as he was reasoning of righteousness, and self-control, and the judgment to come, Felix, becoming greatly afraid, answered—For the present, be going thy way, and, when I find an opportunity, I will send for thee, —
26 A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
at the same time, also hoping that, money, would be given him by Paul; wherefore also, the more frequently sending for him, he used to converse with him.
27 Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.
When, however, two years, were completed, Felix, was succeeded, by Porcius Festus, and Felix, wishing to gain favour with the Jews, left Paul bound.