< Ayyukan Manzanni 24 >
1 Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
Five days later, Ananias the high priest came down to Caesarea with some of the elders, and with an orator, named Tertullus. They laid information before the governor against Paul.
2 Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
So Paul was sent for, and then Tertullus began to accuse him, saying. "As it is owing to your excellency that we enjoy profound peace, and that the state of this nation,
3 Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
"owing to your wise care, has been improved in every respect and in every place, we accept it with profound thankfulness.
4 Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
"But not to weary you too much, I beg of your Excellency to listen to a few words from us.
5 “Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
"For we have found this fellow a pest, an inciter of insurrection among all the Jews of the empire, and a ringleader in the heresy of the Nazarenes.
6 har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
"He even tried to profane the Temple, but we arrested him.
"Then the chief captain, Lysias came and violently took him from us.
8 Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
From him you will be able, by examining Paul yourself, to learn the truth of all these charges we are bringing against him."
9 Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
The Jews also joined in the charge, maintaining that these were the facts.
10 Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
Then at a nod from the governor, Paul spoke. "Because I know that for many years you have been a judge in this nation, I feel encouraged to make my defense.
11 Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
"For you have it in your power to know that it is not more than twelve days ago that I went up to Jerusalem to worship;
12 Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
"and that neither in the Temple, nor in the synagogues, nor in the city, did they find me disputing with any man or stirring up a crowd.
13 Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
"Nor can they prove the charges which they are now bringing against me.
14 Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
"But this I confess to you, that I worship the God of our ancestors, according to the Way which they call a heresy, believing everything that is according to the Law, or is written in the Prophets,
15 ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
"and having hope toward God, which these also themselves look for, that there is to be a resurrection both of the just and the unjust.
16 Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
"Hence I too endeavor to have a conscience void of offense toward God and men alway.
17 “Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
"Now after many years I came to bring alms to my nation, and to offer sacrifices.
18 Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
"While I was thus engaged, they found me in the temple, purified, with no crowd and no uproar. But there were certain Asiatic Jews
19 Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
"who ought to have been here before you, and to have made accusations if they had anything against me.
20 Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
"Or let these men themselves say what fault they found, when I appeared before the Sanhedrin!
21 sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
"Unless it was for this one sentence which I uttered when I stood and cried, ‘It is for the resurrection of the dead that I am on my trial today before you.’"
22 Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
At this point Felix, who had a pretty accurate knowledge of the Way, adjourned the case, saying to the Jews, "When Lysias the tribune comes down, I will go carefully into the matter."
23 Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
And he gave orders to the centurion that Paul should be kept in custody, but treated with indulgence, and that his personal friends were not to be forbidden to minister to him.
24 Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
Some days later Felix came, with his wife Drusilla, a Jewess; he sent for Paul, and listened to him concerning the faith in Christ Jesus.
25 Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
And as he reasoned about morality, self-control, and the future judgment, Felix was terrified, and said, "For the present go on your way, and when I find a convenient season, I will send for you."
26 A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
He was hoping that Paul would give him money, and for this reason he used to send for him often to converse with him.
27 Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.
But after two full years Felix was succeeded by Porcius Festus, and because he wished to curry favor with the Jews, Felix left Paul still in prison.