< Ayyukan Manzanni 24 >
1 Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
Then, after five days, the high priest Ananias came down with some of the elders and a certain Tertullus, a speaker. And they went to the governor against Paul.
2 Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
And having summoned Paul, Tertullus began to accuse him, saying: “Most excellent Felix, since we have much peace through you, and many things may be corrected by your providence,
3 Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
we acknowledge this, always and everywhere, with acts of thanksgiving for everything.
4 Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
But lest I speak at too great a length, I beg you, by your clemency, to listen to us briefly.
5 “Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
We have found this man to be pestilent, to be inciting seditions among all the Jews in the entire world, and to be the author of the sedition of the sect of the Nazarenes.
6 har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
And he has even been attempting to violate the temple. And having apprehended him, we wanted him to be judged according to our law.
But Lysias, the tribune, overwhelming us with great violence, snatched him away from our hands,
8 Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
ordering his accusers to come to you. From them, you yourself will be able, by judging about all these things, to understand the reason that we accuse him.”
9 Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
And then the Jews interjected, saying that these things were so.
10 Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
Then, since the governor had motioned for him to speak, Paul responded: “Knowing that you have been the judge over this nation for many years, I will give an explanation of myself with an honest soul.
11 Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
For, as you may realize, it has only been twelve days since I went up to worship in Jerusalem.
12 Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
And they did not find me in the temple arguing with anyone, nor causing a rally of the people: neither in the synagogues, nor in the city.
13 Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
And they are not able to prove to you the things about which they now accuse me.
14 Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
But I confess this to you, that according to that sect, which they call a heresy, so do I serve my God and Father, believing all that is written in the Law and the Prophets,
15 ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
having a hope in God, which these others themselves also expect, that there will be a future resurrection of the just and the unjust.
16 Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
And in this, I myself always strive to have a conscience that is lacking in any offense toward God and toward men.
17 “Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
Then, after many years, I went to my nation, bringing alms and offerings and vows,
18 Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
through which I obtained purification in the temple: neither with a crowd, nor with a commotion.
19 Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
But certain Jews out of Asia are the ones who should have appeared before you to accuse me, if they have anything against me.
20 Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
Or let these ones here say if they have found in me any iniquity, while standing before the council.
21 sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
For while standing among them, I spoke out solely about this one matter: about the resurrection of the dead. It is about this that I am being judged today by you.”
22 Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
Then Felix, after having ascertained much knowledge about this Way, kept them waiting, by saying, “When Lysias the tribune has arrived, I will give you a hearing.”
23 Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
And he ordered a centurion to guard him, and to take rest, and not to prohibit any of his own from ministering to him.
24 Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
Then, after some days, Felix, arriving with his wife Drusilla who was a Jew, called for Paul and listened to him about the faith that is in Christ Jesus.
25 Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
And after he discoursed about justice and chastity, and about the future judgment, Felix was trembling, and he responded: “For now, go, but remain under guard. Then, at an opportune time, I will summon you.”
26 A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
He was also hoping that money might be given to him by Paul, and because of this, he frequently summoned him and spoke with him.
27 Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.
Then, when two years had passed, Felix was succeeded by Portius Festus. And since Felix wanted to show particular favor to the Jews, he left Paul behind as a prisoner.