< Ayyukan Manzanni 23 >

1 Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
פולוס נעץ את מבטו בחברי הסנהדרין ואמר:”אחים, תמיד חייתי לפני אלוהים במצפון נקי.“
2 Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
באותו רגע ציווה חנניה הכהן על האנשים שעמדו ליד פולוס לסטור לו על פיו.
3 Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
”יסטור לך אלוהים, קיר מסויד שכמוך!“קרא פולוס.”איזה מן שופט אתה? כיצד אתה יכול לשבת כאן ולשפוט אותי על־פי התורה, כשבאותו זמן אתה עצמך עובר על התורה, ומצווה להכות אותי?!“
4 Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
האנשים שעמדו קרוב לפולוס אמרו לו:”אתה מעליב את הכהן הגדול!“
5 Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
”אחי, אני מצטער“, התנצל פולוס.”לא ידעתי שזהו הכהן הגדול. הרי כתוב בתורה שאסור להעליב נשיא או שליט.“
6 Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
פתאום צץ רעיון במוחו של פולוס: הלא מחצית חברי הסנהדרין היו פרושים, ומחציתם – צדוקים. הוא קם על רגליו וקרא בקול:”אחי, אני פרוש בן פרוש, ועכשיו אתם שופטים אותי על־שום שאני מאמין בתחיית המתים!“
7 Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
דבריו אלה פילגו מיד את הסנהדרין לשניים, ועתה הייתה המחלוקת בין הפרושים ובין הצדוקים.
8 (Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
כי הפרושים האמינו בתחיית המתים ובקיומם של מלאכים ורוחות, ואילו הצדוקים כפרו בכל אלה.
9 Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
ההמולה הלכה וגברה, וסופרים אחדים – שהיו פרושים בעצמם – קמו ודיברו בזכותו של פולוס.”לא מצאנו כל אשמה באיש הזה!“צעקו.”אולי הקול שדיבר אליו בדרך לדמשק היה רוח או מלאך!“
10 Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
המתיחות גברה והוויכוח התלהט; הנוכחים החלו למשוך את פולוס – זה לכאן וזה לכאן. מפקד החטיבה פחד שיקרעו את פולוס לגזרים, ולכן ציווה על חייליו לקחת אותו משם בכוח הזרוע ולהחזירו למצודה.
11 Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
באותו לילה עמד האדון לצדו של פולוס ואמר לו:”חזק ואמץ, פולוס! כשם שהעדת עלי בפני תושבי ירושלים, כך תצטרך להעיד עלי גם בפני תושבי רומא!“
12 Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
לפנות בוקר התקבצו יחד למעלה מארבעים יהודים, ונדרו נדר שלא יאכלו ולא ישתו עד שיהרגו את פולוס.
13 Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
14 Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
הם הלכו אל ראשי הכוהנים ואל הזקנים וסיפרו להם על כך.
15 Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
”בקשו ממפקד החטיבה להחזיר את פולוס לבית־הדין“, אמרו.”העמידו פנים כאילו שאתם רוצים לשאול אותו עוד כמה שאלות, ואנחנו כבר נהרוג אותו בדרך.“
16 Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
אולם בן־אחותו של פולוס גילה במקרה את מזימתם, ומיהר אל המצודה כדי לדווח לפולוס על כך.
17 Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
פולוס קרא לאחד הקצינים ואמר:”קח את הנער הזה אל המפקד; יש לו משהו חשוב לספר לו.“
18 Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
הקצין לקח את הנער, הביאו אל המפקד והסביר:”פולוס האסיר קרא לי וביקש ממני להביא אליך את הנער הזה, כי יש לו משהו לומר לך.“
19 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
המפקד אחז בידו של הנער, הובילוהו הצידה ושאל:”מה אתה רוצה לומר לי?“
20 Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
”מחר מתכוננים היהודים לבקש ממך להחזיר את פולוס לסנהדרין, “סיפר הנער,”ביומרה שהם מעוניינים לשאול אותו שאלות נוספות.
21 Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
אולם אל תשמע בקולם! כי למעלה מארבעים איש אורבים לו בדרך, מוכנים להתנפל עליו ולהרוג אותו. הם נדרו נדר שלא יאכלו ולא ישתו עד שפולוס ימות. עתה הם מחכים שתענה בחיוב לבקשתם.“
22 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
”אל תאמר לאיש שסיפרת לי דברים אלה.“הזהירו המפקד, ושלחו לדרכו.
23 Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
לאחר מכן קרא המפקד לשני קצינים ופקד עליהם:”הכינו מאתיים חיילים לצאת לקיסריה הערב בשעה תשע! קחו אתכם מאתיים קשתים, ועוד שבעים פרשים חמושים. תנו לפולוס סוס רכיבה, והביאו אותו בשלום אל פליקס המושל.“
24 Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
הוא שלח בידם את המכתב הבא אל פליקס:
26 Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
”מאת: קלודיוס לוסיאס.”אל: הוד מעלתו המושל פליקס.”שלום וברכה!
27 Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
”אדם זה נתפס על־ידי היהודים, והם כמעט הרגו אותו. אולם משנודע לי שהוא אזרח רומאי, שלחתי מיד חיילים להצילו מידם.
28 Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
הבאתי אותו למשפט לפני בית־המשפט העליון של היהודים, כדי לדעת מה עשה.
29 Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
עד מהרה נוכחתי לדעת שהאשמותיהם מתייחסות רק לאמונה היהודית, ולא למעשה פלילי שדינו מאסר או מוות,
30 Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
אך כשנודע לי שיהודים רוצים להרוג אותו, החלטתי לשלחו אליך ולומר למאשימיו להביא את טענותיהם לפניך.“
31 Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
החיילים מילאו את הפקודה ולקחו את פולוס בלילה למבצר אנטיפטרוס.
32 Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
למחרת בבוקר חזרו החיילים למצודה בירושלים, והשאירו את פולוס עם הפרשים כדי שייקחו אותו לקיסריה.
33 Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
בהגיעם לקיסריה הביאו את פולוס לפני המושל, ומסרו לו את המכתב.
34 Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
פליקס קרא את המכתב ושאל את פולוס למוצאו.”אני מקיליקיה“, ענה פולוס.
35 sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.
”אשמע את המקרה שלך במלואו כאשר יגיעו לכאן גם מאשימיך“, אמר לו המושל, וציווה לשמור עליו בכלא שבארמון המלך הורדוס.

< Ayyukan Manzanni 23 >