< Ayyukan Manzanni 23 >

1 Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
and Paul looking earnestly at the sanhedrim, said, "Brethren, I have lived in all good conscience before God even to this day:"
2 Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
but the high priest Ananias ordered those that stood next him, to smite him on the mouth.
3 Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
Then said Paul to him, "God will smite thee, thou whited wall: dost thou sit to judge me according to the law, and contrary to the law commandest me to be smitten?"
4 Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
But they that stood by said, Revilest thou God's high-priest?
5 Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
And Paul said, I was not aware, brethren, that it was the high-priest: for it is written, Thou shalt not speak evil of the ruler of thy people.
6 Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
But Paul, knowing that the one part were sadducees, and the other pharisees, cried out in the sanhedrim, "Brethren, I am a pharisee, the son of a pharisee: for the hope of a resurrection of the dead I am now prosecuted."
7 Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
Upon his saying this, there rose a contention between the pharisees and the sadducees; and the people were divided.
8 (Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
For the sadducees say that there is no resurrection, nor angel, nor spirit; but the pharisees acknowledge both.
9 Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
So there was a great clamor: and the scribes that were of the party of the pharisees rose up and contended, saying, We find no evil in this man; but if a spirit or an angel hath spoken to him, let us not fight against God.
10 Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
But as there arose much contention, the tribune fearing least Paul should be torn in pieces by them, ordered a party of soldiers to go down, and take him by force out of the midst of them, and to bring him into the castle.
11 Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
And the following night, the Lord standing by him said, Paul, be of good courage; for as thou hast testified concerning me at Jerusalem, so must thou also bear testimony at Rome.
12 Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
And when it was day, some of the Jews, having formed a conspiracy, bound themselves with a curse, saying, that they would neither eat nor drink till they had killed Paul.
13 Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
And they were more than forty that had made this oath:
14 Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
who came to the chief priests and the elders, and said, "We have bound ourselves by a curse to eat nothing till we have killed Paul.
15 Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
Now therefore do ye with the rest of the sanhedrim signify to the tribune, that he would bring him down to you to-morrow, as if you would examine more accurately some things concerning him: and we are ready to dispatch him before he come near you."
16 Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
But Paul's sister's son, hearing of the ambush, came and entered into the castle, and told Paul.
17 Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
Then Paul called one of the centurions to him, and said, Introduce this young man to the tribune; for he hath something to tell him.
18 Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
So he took him and brought him to the tribune, and said, Paul the prisoner called me to him, and desired me to introduce this young man unto thee, as having something to say to thee.
19 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
And the tribune took him by the hand, and retiring into a private apartment asked him, What is it which thou hast to tell me?
20 Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
And he said, The Jews have agreed to desire thee, that thou wouldest bring down Paul to-morrow to the council, as if they would inquire something more strictly concerning him.
21 Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
But do not thou comply with them: for there lie in wait for him more than forty men of them, who have bound themselves with a curse neither to eat nor drink till they have killed him: and they are now ready, waiting for an order from thee.
22 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
Then the tribune dismissed the young man, charging him, Tell no one that thou hast discovered these things to me.
23 Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
And he called two of the centurions to him, and said, Get ready two hundred soldiers to go to Cesarea, and seventy horsemen, and two hundred spearmen, by the third hour of the night.
24 Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
And provide beasts, that they may set Paul on and bring him safe to Felix the governor.
25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
And he wrote a letter to this effect:
26 Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
Claudius Lysias to the most excellent governor Felix sendeth greeting.
27 Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
This man being seized by the Jews, and about to be killed by them, I came upon them with some soldiers and rescued him: for I understand that he is a Roman.
28 Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
But desiring to know the cause for which they accused him, I brought him down into their council:
29 Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
and I found he was accused about questions of their law, but had no charge against him deserving death or bonds.
30 Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
But an ambush, which was going to be laid for the man by the Jews, being discovered to me, immediately I sent him to thee, telling his accusers also to say before thee what they had against him. Farewell.
31 Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
The soldiers therefore, according to the orders given them, took up Paul, and brought him by night to Antipatris.
32 Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
And the next day they returned to the castle, leaving the horsemen to go with him;
33 Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
who, when they came into Cesarea, and delivered the epistle to the governor, presented Paul also before him.
34 Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
And when the governor had read the letter, and asked of what province he was; being informed that he was of Cilicia, he said,
35 sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.
I will hear thee, when thine accusers are also come. And he ordered him to be kept in Herod's palace.

< Ayyukan Manzanni 23 >