< Ayyukan Manzanni 23 >
1 Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
And Paul, earnestly beholding the council, said, Men, brethren, I have lived in all good conscience before God until this day.
2 Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
And the high priest Ananias commanded them that stood by him, to strike him on the mouth.
3 Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
Then said Paul to him, God shall smite thee, [thou] whited wall: for sittest thou to judge me according to the law, and commandest me to be smitten contrary to the law?
4 Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
And they that stood by, said, Revilest thou God's high priest?
5 Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
Then said Paul, I knew not, brethren, that he is the high priest: for it is written, Thou shalt not speak evil of the ruler of thy people.
6 Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
But when Paul perceived that the one part were Sadducees, and the other Pharisees, he cried out in the council, Men, brethren, I am a Pharisee, the son of a Pharisee: concerning the hope and resurrection of the dead I am called in question.
7 Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
And when he had so said, there arose a dissension between the Pharisees and the Sadducees: and the multitude was divided.
8 (Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
For the Sadducees say that there is no resurrection, neither angel, nor spirit: but the Pharisees confess both.
9 Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
And there arose a great cry: and the scribes [that were] of the Pharisees' part arose, and contended, saying, We find no evil in this man: but if a spirit or an angel hath spoken to him, let us not fight against God.
10 Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
And when there arose a great dissension, the chief captain, fearing lest Paul would have been pulled in pieces by them, commanded the soldiers to go down, and to take him by force from among them, and to bring [him] into the castle.
11 Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
And the night following the Lord stood by him, and said, Be of good cheer, Paul: for as thou hast testified concerning me in Jerusalem, so must thou bear testimony also at Rome.
12 Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
And when it was day, certain of the Jews banded together, and bound themselves under a curse, saying, that they would neither eat nor drink till they had killed Paul.
13 Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
And they were more than forty who had made this conspiracy.
14 Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
And they came to the chief priests and elders, and said, We have bound ourselves under a great curse, that we will eat nothing until we have slain Paul.
15 Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
Now therefore ye with the council signify to the chief captain, that he bring him down to you to-morrow, as though ye would inquire something more perfectly concerning him: and we, before he shall come near, are ready to kill him.
16 Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
And when the son of Paul's sister heard of their lying in wait, he went and entered into the castle, and told Paul.
17 Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
Then Paul called one of the centurions to [him], and said, Bring this young man to the chief captain: for he hath a certain thing to tell him.
18 Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
So he took him, and brought [him] to the chief captain, and said, Paul the prisoner called me to [him], and prayed me to bring this young man to thee, who hath something to say to thee.
19 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
Then the chief captain took him by the hand, and went [with him] aside privately, and asked [him], What is that thou hast to tell me?
20 Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
And he said, The Jews have agreed to desire thee, that thou wouldst bring down Paul to-morrow into the council, as though they would inquire somewhat concerning him more perfectly.
21 Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
But do not thou yield to them: for there are of them who lie in wait for him more than forty men, who have bound themselves with an oath, that they will neither eat nor drink till they have killed him: and now they are ready, looking for a promise from thee.
22 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
So the chief captain [then] let the young man depart, and charged [him], [See thou] tell no man that thou hast shown these things to me.
23 Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
And he called to [him] two centurions, saying, Make ready two hundred soldiers to go to Cesarea, and seventy horsemen, and spearmen two hundred, at the third hour of the night;
24 Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
And provide [for them] beasts, that they may set Paul on, and bring [him] safe to Felix the governor.
25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
And he wrote a letter after this manner:
26 Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
Claudius Lysias, to the most excellent governor Felix, [sendeth] greeting.
27 Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
This man was taken by the Jews, and would have been killed by them: then I came with a body of soldiers, and rescued him, having understood that he was a Roman.
28 Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
And when I would have known the cause for which they accused him, I brought him forth into their council:
29 Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
Whom I perceived to be accused of questions of their law, but to have nothing laid to his charge worthy of death, or of bonds.
30 Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
And when it was told to me that the Jews laid wait for the man, I sent forthwith to thee, and gave commandment to his accusers also, to say before thee what [they had] against him. Farewell.
31 Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
Then the soldiers, as it was commanded them, took Paul, and brought [him] by night to Antipatris.
32 Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
On the morrow they left the horsemen to go with him, and returned to the castle:
33 Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
Who, when they came to Cesarea, and delivered the epistle to the governor, presented Paul also before him.
34 Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
And when the governor had read [the letter], he asked of what province he was. And when he understood that [he was] of Cilicia,
35 sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.
I will hear thee, said he, when thy accusers also have come. And he commanded him to be kept in Herod's judgment-hall.