< Ayyukan Manzanni 23 >

1 Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
And Paul, looking steadfastly, at the High-council, said—Brethren! I, in all good conscience have used my citizenship for God until this day.
2 Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
And, the High-priest, Ananias, ordered them that stood by him, to be smiting him on the mouth.
3 Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
Then, Paul, unto him, said—God is about to be smiting thee, thou whited wall! Dost, thou, then sit to judge me according to the law, and, unlawfully, orderest me to be smitten?
4 Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
And, they who stood by, said—The High-priest of God, dost thou revile?
5 Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
And Paul said—I was not aware, brethren, that he was high-priest; because it is written—Of a ruler of thy people, shalt thou not speak injuriously.
6 Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
But Paul, getting to know that, the one part, were Sadducees and, the other, Pharisees, began to cry aloud in the council—Brethren! I, am, a Pharisee, son of Pharisees: —Concerning a hope, even of a rising again of the dead, am I to be judged.
7 Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
And, as this he was saying, there arose a dissension of the Pharisees and Sadducees; and rent asunder was the throng.
8 (Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
For, Sadducees, say, there is no rising again, nor messenger, nor spirit, whereas, Pharisees, confess them both.
9 Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
And there arose a great outcry, and certain of the Scribes of the party of the Pharisees, standing up, began to strive, saying—Nothing bad, find we in this man; —but, if a spirit hath spoken unto him, or a messenger…
10 Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
And, great dissension arising, the captain, fearing lest Paul would be torn in pieces by them, ordered the troop to go down, and take him by force out of their midst, to bring him into the castle.
11 Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
But, on the following night, the Lord, standing over him, said—Be of good courage! for, as thou hast fully borne witness of the things concerning me in Jerusalem, so must thou, in Rome also, bear witness.
12 Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
And, when it became day, the Jews, forming a conspiracy, bound themselves under a curse, saying, that they would neither eat nor drink till they had slain Paul.
13 Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
And they were, more than forty, who, this sworn-confederacy, had formed.
14 Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
And they went unto the High-priests and Elders, and said—With a curse have we bound ourselves, to taste, nothing, until we have slain Paul.
15 Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
Now, therefore, do, ye, with the High-council, make it appear unto the captain, that he should bring him down unto you, as though about to ascertain more exactly the things that concern him; and, we, or ever he come near, are ready to kill him.
16 Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
But Paul’s sister’s son hearing of the lying-in-wait, happening to be near, and coming into the castle, —reported it unto Paul.
17 Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
And Paul, calling unto him one of the centurions, said—This young man, lead thou away unto the captain, for he hath somewhat to report unto him.
18 Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
He, therefore, taking him with him, brought him unto the captain, and saith—The prisoner Paul, calling me unto him, requested me to bring this young man unto thee, as having somewhat to tell thee.
19 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
And the captain, taking him by the hand, and going aside, began, privately, to ask—What is it which thou hast to report unto me?
20 Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
And he said—The Jews, have agreed to request thee, that, to-morrow, thou wouldst bring, Paul, down into the High-council, as though about to ascertain something, more exact, concerning him.
21 Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
Thou, therefore, do not be persuaded by them, for there are lying in wait for him, from among them, more than forty men, —who, indeed, have bound themselves under a curse, neither to eat nor drink, till they have killed him; and, now, are they ready, awaiting the promise, from thee.
22 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
the captain, therefore, dismissed the young man, charging him—Unto no one, divulge thou, that, these things, thou hast shewed unto me.
23 Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
And calling certain two of the centurions he said—Make ye ready two hundred soldiers, that they may journey as far as Caesarea, —and seventy horsemen, and two hundred spearmen, by the third hour of the night;
24 Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
beasts also provide, in order that, seating Paul thereon, they may bring him safely through unto Felix the governor.
25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
And he wrote a letter, after this form: —
26 Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
Claudius Lysias, unto the most excellent governor Felix, Joy!
27 Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
This man, having been apprehended by the Jews, and being about to be killed by them, I went down with the troop, and rescued; having learned that he was, a Roman.
28 Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
And, being minded to find out the cause for which they were accusing him, [I took him down into their High-council],
29 Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
whom I found to be accused concerning questions of their law, but, of nothing worthy of death or bonds, to be charged.
30 Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
But, when I was informed there would be a plot against the man, forthwith, I sent him unto thee, charging, his accusers also, to be speaking against him before thee.
31 Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
So the soldiers, according to their orders, taking up Paul, brought him by night unto Antipatris;
32 Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
and, on the morrow, leaving the horsemen to go on with him, returned to the castle, —
33 Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
and the others, entering into Caesarea, and delivering the letter unto the governor, set, Paul also, before him.
34 Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
And, when he had read it, and asked out of what province he was, and learned that he was from Cilicia,
35 sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.
I myself will hear thee in full, said he, whensoever, thine accusers also, are come; and gave orders that, in the palace of Herod, he should be kept under guard.

< Ayyukan Manzanni 23 >