< Ayyukan Manzanni 23 >
1 Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
Paul fixed his eyes on the Council, and began: ‘Brothers, for my part, I have always ordered my life before God, with a clear conscience, up to this very day.’
2 Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
At this, the high priest Ananias ordered the men standing near to strike him on the mouth;
3 Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
Paul turned to him and said: ‘God will strike you, you whitewashed wall! Are you sitting there to try me in accordance with law, and yet, in defiance of law, order me to be struck?’
4 Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
The people standing near said to Paul, ‘Do you know that you are insulting God’s high priest?’
5 Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
‘I did not know, brothers, that it was the high priest,’ said Paul, ‘for scripture says – “Of the ruler of your people you should speak no ill”.’
6 Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
Noticing that some of those present were Sadducees and others Pharisees, Paul called out in the Council, ‘Brothers, I am a Pharisee and a son of Pharisees. It is on the question of hope for the dead and of their resurrection that I am on my trial.’
7 Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
As soon as he said this, a dispute arose between the Pharisees and the Sadducees; and there was a sharp division of opinion among those present.
8 (Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
(For Sadducees say there is no such thing as a resurrection, and that there is neither angel nor spirit, while Pharisees believe in both.)
9 Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
So a great uproar ensued, and some of the Teachers of the Law belonging to the Pharisees’ party stood up and hotly protested, ‘We find nothing whatever wrong in this man. Suppose a spirit did speak to him, or an angel…’
10 Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
The dispute was becoming so violent, that the commanding officer, fearing that Paul would be torn in pieces between them, ordered the Guard to go down and rescue him from them, and take him into the Fort.
11 Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
That night the Lord came and stood by Paul, and said, ‘Courage! You have borne witness for me in Jerusalem and you must bear witness in Rome also.’
12 Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
In the morning some Jewish men combined together, and took an oath that they would not eat or drink until they had killed Paul.
13 Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
There were more than forty in the plot;
14 Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
and they went to the chief priests and the elders, and said, ‘We have taken a solemn oath not to touch food until we have killed Paul.
15 Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
So we want you now, with the consent of the Council, to suggest to the commanding officer that he should bring Paul down before you, as though you intended to go more fully into his case; but, before he comes here, we will be ready to make away with him.’
16 Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
However, the son of Paul’s sister, hearing of the plot, went to the Fort, and on being admitted, told Paul about it.
17 Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
Paul called one of the garrison centurion and asked him to take the lad to the commanding officer, as he had something to tell him.
18 Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
The centurion went with the lad to the commanding officer, and said, ‘The prisoner Paul called me and asked me to bring this lad to you, as he has something to tell you.’
19 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
The commanding officer took the lad by the hand, and, stepping aside, asked what it was he had to tell him.
20 Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
‘Some men have agreed,’ answered the lad, ‘to ask you to bring Paul down before the Council tomorrow, on the plea of your making further inquiry into his case.
21 Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
But do not let them persuade you, for more than forty of them are lying in wait for him, who have taken an oath that they will not eat or drink, until they have made away with him; and they are at this very moment in readiness, counting on your promise.’
22 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
The commanding officer then dismissed the lad, cautioning him not to mention to anybody that he had given him that information.
23 Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
Then he called two Captains, and ordered them to have two hundred soldiers ready to go to Caesarea, as well as seventy troopers and two hundred lancers, by nine o’clock that night,
24 Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
and to have horses ready for Paul to ride, so that they might take him safely to Felix, the Governor.
25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
He also wrote a letter along these lines:
26 Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
“Claudius Lysias sends his compliments to His Excellency Felix the Governor.
27 Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
The man whom I send with this had been seized by some Jews, and was on the point of being killed by them, when I came upon them with the force under my command, and rescued him, as I learned that he was a Roman citizen.
28 Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
Wanting to know exactly the ground of the charges they made against him, I brought him before their Council,
29 Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
when I found that their charges were connected with questions of their own Law, and that there was nothing alleged involving either death or imprisonment.
30 Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
Having, however, information of a plot against the man, which was about to be put into execution, I am sending him to you at once, and I have also directed his accusers to prosecute him before you.”
31 Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
The soldiers, in accordance with their orders, took charge of Paul and conducted him by night to Antipatris;
32 Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
and on the next day, leaving the troopers to go on with him, they returned to the Fort.
33 Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
On arriving at Caesarea, the troopers delivered the letter to the Governor, and brought Paul before him.
34 Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
As soon as Felix had read the letter, he enquired to what province Paul belonged, and, learning that he came from Cilicia, he said,
35 sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.
‘I will hear all you have to say as soon as your accusers have arrived.’ And he ordered Paul to be kept under guard in Herod’s Government house.