< Ayyukan Manzanni 22 >
1 “’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
«Mes frères et mes pères, «Écoutez ce que j'ai maintenant à vous dire pour me justifier»
2 Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
— (quand on l'entendit parler en hébreu, on redoubla d'attention) —
3 “Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
il continua: «Je suis un Juif, né à Tarse, en Cilicie, mais j'ai été élevé dans cette ville-ci, j'ai fait mes études aux pieds de Gamaliel, dans toute la rigueur de la Loi de nos pères; j'ai été plein de zèle pour la cause de Dieu, comme vous l'êtes tous aujourd'hui.
4 Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
Cette secte, je l'ai persécutée à mort; j'ai chargé de chaînes, j'ai jeté en prison hommes et femmes,
5 kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
comme peuvent l'attester le grand-prêtre et le Sanhédrin tout entier. Car c'est d'eux que j'ai reçu des lettres pour nos frères de Damas, et j'y allai pour amener prisonniers à Jérusalem ceux que j'y trouverais et les faire punir.
6 “Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
J'étais en chemin et j'approchais de Damas, quand tout à coup, vers midi, une vive lumière venue du ciel brilla autour de moi,
7 Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
je tombai par terre et j'entendis une voix qui me disait: «Saul, Saul, pourquoi me persécutes-tu?»
8 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
— Je répondis: «Qui es-tu, Seigneur?» — La voix me dit: «Je suis Jésus de Nazareth que tu persécutes.»
9 Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
— Ceux qui étaient avec moi avaient vu la lumière, mais n'avaient pas entendu la voix de celui qui me parlait.
10 “Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
Je dis alors: «Que dois-je faire, Seigneur?» et le Seigneur me répondit: «Relève-toi, rends-toi à Damas, et là on te dira tout ce que tu as l'ordre de faire.»
11 Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
— Comme je n'y voyais pas (la lumière m'avait ébloui), mes compagnons me prirent par la main et me menèrent à Damas.
12 “Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
Un certain Hananias, homme pieux et fidèle à la Loi, estimé de tous les résidents juifs,
13 Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
vint se présenter à moi et me dit: «Saul, mon frère, regarde», — et immédiatement je le vis.
14 “Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
Puis il me dit: «Le Dieu de nos pères t'a prédestiné à connaître sa volonté, à voir le Juste et à entendre les paroles de sa bouche;
15 Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
car tu seras son témoin auprès de tous les hommes, témoin de ce que tu as vu et entendu.
16 Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
Et maintenant pourquoi tarderais-tu? Lève-toi, reçois le baptême et purifie-toi de tes péchés en invoquant son nom.»
17 “Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
De retour à Jérusalem, comme j'étais en prière au Temple, je tombai en extase,
18 na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
et je le vis qui me disait: «Hâte-toi de partir, sors au plus vite de Jérusalem, car ils n'accepteront pas le témoignage que tu me rends.»
19 “Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
Et je lui dis: «Seigneur, il savent eux-mêmes que j'ai fait emprisonner et flageller dans les synagogues ceux qui croient en toi,
20 Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
et quand ils ont versé le sang, d'Étienne, ton témoin, j'étais là, présent, j'applaudissais, je gardais les vêtements des bourreaux»;
21 “Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
et il me dit: «Va, car je t'enverrai au loin vers les païens.»
22 Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
On l'avait écouté jusque-là, mais, à ce mot, les clameurs recommencèrent: «A mort, cet homme! il ne faut pas lui laisser la vie!»
23 Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
Ils vociféraient, ôtaient leurs vêtements, faisaient voler la poussière.
24 sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
Le tribun commanda alors de le faire entrer dans la Forteresse et de le mettre à la question pour savoir la vraie cause de tous ces cris contre lui.
25 Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
Comme on l'avait déjà attaché au poteau pour recevoir les coups de lanières, Paul dit au centurion qui commandait: «Vous est-il permis de flageller un citoyen romain qui n'est pas même condamné?»
26 Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
A ces paroles, le centurion alla en référer au tribun: «Que vas-tu faire? lui dit-il, cet homme est citoyen romain.»
27 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
Le tribun vint à Paul et lui dit: «Réponds-moi, es-tu citoyen romain?» — «Oui», lui dit Paul.
28 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
Le tribun repartit: «Moi, j'ai dépensé une somme considérable pour avoir ce titre.» — «Et moi, lui répliqua Paul, je l'ai par ma naissance.»
29 Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
Les exécuteurs s'écartèrent immédiatement, et le tribun commença à avoir peur, voyant qu'il avait fait mettre aux fers un citoyen romain.
30 Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.
Le lendemain, voulant savoir positivement quels griefs articulaient les Juifs, il lui fit ôter les fers et donna ordre de convoquer le haut sacerdoce et le Sanhédrin en entier; puis il amena Paul et le fit comparaître devant eux.