< Ayyukan Manzanni 22 >
1 “’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
Brethren and fathers, hear my apology, which I make to you now.
2 Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
And when they heard, that he addressed them in the Hebrew dialect, they rather kept silence;
3 “Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
and he said, I am, indeed, a Jew, born at Tarsus, in Cilicia, but educated in this city, at the feet of Gamaliel, accurately instructed in the law of our fathers; being zealous for God, as you all are at this day:
4 Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
who persecuted this way to the death; binding both men and women, and delivering them into prisons:
5 kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
as also the high priest is my witness, and all the national senate: from whom also having received letters to the brethren, I went to Damascus; to bring those that were there bound, to Jerusalem, that they might be punished.
6 “Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
And it came to pass, that as I was on my journey, and was come nigh to Damascus, about noon, on a sudden a great light from heaven shone about me;
7 Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
and I fell to the ground, and heard a voice saying to me, Saul, Saul, why do you persecute me?
8 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
But I answered, Who art thou, Lord? And he said to me, I am Jesus the Nazarene, whom you persecute.
9 Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
And they that were with me saw the light, indeed, and were terrified; but they did not distinctly hear the voice of him that spoke to me.
10 “Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
And I said, Lord, what shall I do? And the Lord said to me, Arise, and go to Damascus, and there it shall be told you of all things, which are appointed for you to do.
11 Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
And as I could not see, by reason of the glory of that light; being led by those that were with me, I came to Damascus.
12 “Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
And one Ananias, a pious man according to the law, who had an honorable character amongst all the Jews at Damascus,
13 Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
coming to me, and standing by me, said to me, Brother Saul, look up. And in that very hour, I looked up on him.
14 “Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
And he said, The God of our fathers, has chosen you to know his will, and to see that righteous person, and to hear a voice from his mouth:
15 Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
because you shall be his witness, to all men, of those things, which you have seen and heard.
16 Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
And now, why do you delay? Arise, and be immersed, and wash away your sins, invoking his name.
17 “Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
And it came to pass, that when I was returned to Jerusalem, and was praying in the temple, I was in a trance:
18 na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
and I saw him, saying to me, Make haste, and depart quickly from Jerusalem; for they will not receive your testimony concerning me.
19 “Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
And I said, Lord, they know I was imprisoning, and scourging in the synagogues, them that believed in thee;
20 Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
and when the blood of Stephen thy martyr was shed, I also was standing by, and consenting, and kept the garments of those who slew him.
21 “Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
And he said to me, Go your way, for I will send you afar off to the Gentiles--
22 Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
And they heard him to this word, and they lifted up their voices, saying, Away with this fellow from the earth, for it is not fit that he should live.
23 Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
And as they were crying out, and were rending their garments, and casting dust into the air,
24 sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
the commander ordered that he should be brought into the castle, saying, that he should be put to the question by scourging, that he might know for what cause, they raised such an outcry against him.
25 Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
And as they binding him with thongs, Paul said to the centurion, who stood by, Is it lawful for you to scourge a man, who is Roman, and uncondemned.
26 Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
And the centurion hearing this, went and addressed the commander, saying, What are you about to do? for this man is a Roman.
27 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
And the commander came, and said to him, Tell me, are you a Roman? And he said, Yes.
28 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
And the commander answered, I obtained this freedom with a considerable sum of money. And Paul replied, But I was free born.
29 Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
They, therefore, who were about to have put him to the question, immediately departed from him: and the commander was afraid, when he knew that he was a Roman, and because he had bound him.
30 Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.
And on the next day, desiring to know certainly of what he was accused by the Jews, he loosed him; and commanded the chief priests, and all the Sanhedrim, to come together; and bringing Paul down, he set him before them.