< Ayyukan Manzanni 22 >

1 “’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
Brethren and fathers, hear my defense, which I now make before you.
2 Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
When they heard that he spoke to them in the Hebrew language, they kept the greater silence. And he said:
3 “Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
I am a Jew, born in Tarsus of Cilicia, yet educated in this city, at the feet of Gamaliel, and instructed according to the strict discipline of the law of our fathers, being zealous for God, as you all are this day.
4 Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
And I persecuted this way to the death, binding and delivering into prison both men and women,
5 kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
as the chief priest and the whole body of elders will testify for me. From them I also received letters to the brethren, and went to Damascus, to bring those, also, who were there, bound to Jerusalem, that they might be punished.
6 “Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
But it came to pass, that, as I was on my journey, and was drawing near to Damascus, about midday, there suddenly shone from heaven a great light round about me;
7 Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
and I fell to the ground, and heard a voice saying to me, Saul, Saul, why do you persecute me?
8 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
And I answered, Who art thou Lord? And he said to me, I am Jesus the Nazarene, whom you persecute.
9 Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
They who were with me saw the light, and were afraid, but did not understand the voice of him who spoke to me.
10 “Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
And I said, What shall I do, Lord? And the Lord said to me, Arise, and go into Damascus, and there you shall be told of all things that are appointed for you to do.
11 Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
And as I could not see for the glory of that light, I was led by the hand by those who were with me, and went into Damascus.
12 “Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
And one Ananias, a devout man according to the law, who had a good report from all the Jews that dwelt there,
13 Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
came to me, and standing by me, said, Brother Saul, receive your sight. And the same hour I looked upon him.
14 “Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
And he said, The God of our fathers has chosen you, that you should know his will, and see the Just One, and hear the voice of his mouth;
15 Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
for you shall be his witness to all men of what you have seen and heard.
16 Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
And now, why do you delay? Arise, and be immersed, and wash away your sins, calling on the name of the Lord.
17 “Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
And it came to pass, after I had returned to Jerusalem, and while I was praying in the temple, that I was in a trance,
18 na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
and saw him saying to me, Make haste, and depart quickly from Jerusalem, for they will not receive your testimony concerning me.
19 “Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
And I said, Lord, they themselves know that I threw into prison, and scourged, in every synagogue, those who believed on thee;
20 Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
and that when the blood of Stephen, thy witness, was shed, I also stood by and approved, and kept the clothing of those who slew him.
21 “Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
And he said to me, Depart, for I will send you far off to the Gentiles.
22 Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
And they heard him to this word, and lifted up their voice, saying: Away with such a man from the earth! for it is not fit that he should live.
23 Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
And as they were crying out, and tossing off their clothes, and throwing dust into the air,
24 sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
the officer commanded him to be led into the fortress, and gave orders that he should be examined by scourging, that he might know for what cause they so cried out against him.
25 Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
But Paul said to the centurion who stood by, as he caused him to be bent forward to the straps: Is it lawful for you to scourge a man who is a Roman, and uncondemned?
26 Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
And when the centurion heard that, he went out and told it to the officer, saying: What are you about to do? for this man is a Roman.
27 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
And the officer came and said to him: Tell me, are you a Roman? He answered: Yes.
28 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
And the officer answered: With a great Bum did I purchase this citizenship. And Paul replied: But I was born a citizen.
29 Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
Then, those who were about to examine him, immediately departed from him. And the officer was afraid, when he learned that he was a Roman, and because he had bound him.
30 Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.
And, on the next day, wishing to know certainly why he was accused by the Jews, he loosed him, and commanded the chief priests and all the Sanhedrim to meet together. And he brought Paul down, and placed him before them.

< Ayyukan Manzanni 22 >