< Ayyukan Manzanni 22 >

1 “’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
„I Mænd, Brødre og Fædre! hører nu mit Forsvar over for eder!‟
2 Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
Men da de hørte, at han talte til dem i det hebraiske Sprog, holdt de sig end mere stille. Og han siger:
3 “Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
„Jeg er en jødisk Mand, født i Tarsus i Kilikien, men opfostret i denne Stad, oplært ved Gamaliels Fødder efter vor Fædrenelovs Strenghed og nidkær for Gud, ligesom I alle ere i Dag.
4 Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
Og jeg forfulgte denne Vej indtil Døden, idet jeg lagde baade Mænd og Kvinder i Lænker og overgav dem til Fængsler,
5 kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
som ogsaa Ypperstepræsten vidner med mig og hele Ældsteraadet, fra hvem jeg endog fik Breve med til Brødrene i Damaskus og rejste derhen for ogsaa at føre dem, som vare der, bundne til Jerusalem, for at de maatte blive straffede.
6 “Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
Men det skete, da jeg var undervejs og nærmede mig til Damaskus, at ved Middag et stærkt Lys fra Himmelen pludseligt omstraalede mig.
7 Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
Og jeg faldt til Jorden og hørte en Røst, som sagde til mig: Saul! Saul! hvorfor forfølger du mig?
8 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
Men jeg svarede: Hvem er du, Herre? Og han sagde til mig: Jeg er Jesus af Nazareth, som du forfølger.
9 Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
Men de, som vare med mig, saa vel Lyset, men hørte ikke hans Røst, som talte til mig.
10 “Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
Men jeg sagde: Hvad skal jeg gøre, Herre? Men Herren sagde til mig: Staa op og gaa til Damaskus; og der skal der blive talt til dig om alt, hvad der er bestemt, at du skal gøre.
11 Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
Men da jeg havde mistet Synet ved Glansen af hint Lys, blev jeg ledet ved Haanden af dem, som vare med mig, og kom saaledes ind i Damaskus.
12 “Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
Men en vis Ananias, en Mand, gudfrygtig efter Loven, som havde godt Vidnesbyrd af alle Jøderne, som boede der,
13 Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
kom til mig og stod for mig og sagde: Saul, Broder, se op! Og jeg saa op paa ham i samme Stund.
14 “Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
Men han sagde: Vore Fædres Gud har udvalgt dig til at kende hans Villie og se den retfærdige og høre en Røst af hans Mund.
15 Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
Thi du skal være ham et Vidne for alle Mennesker om de Ting, som du har set og hørt.
16 Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
Og nu, hvorfor tøver du? Staa op, lad dig døbe og dine Synder aftvætte, idet du paakalder hans Navn!
17 “Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
Og det skete, da jeg var kommen tilbage til Jerusalem og bad i Helligdommen, at jeg faldt i Henrykkelse
18 na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
og saa ham, idet han sagde til mig: Skynd dig, og gaa hastigt ud af Jerusalem, thi de skulle ikke af dig modtage Vidnesbyrd om mig.
19 “Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
Og jeg sagde: Herre! de vide selv, at jeg fængslede og piskede trindt om i Synagogerne dem, som troede paa dig,
20 Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
og da dit Vidne Stefanus's Blod blev udgydt, stod ogsaa jeg hos og havde Behag deri og vogtede paa deres Klæder, som sloge ham ihjel.
21 “Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
Og han sagde til mig: Drag ud; thi jeg vil sende dig langt bort til Hedninger.‟
22 Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
Men de hørte paa ham indtil dette Ord, da opløftede de deres Røst og sagde: „Bort fra Jorden med en saadan! thi han bør ikke leve.‟
23 Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
Men da de skrege og reve Klæderne af sig og kastede Støv op i Luften,
24 sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
befalede Krigsøversten, at han skulde føres ind i Borgen, og sagde, at man med Hudstrygning skulde forhøre ham, for at han kunde faa at vide, af hvad Aarsag de saaledes raabte imod ham.
25 Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
Men da de havde udstrakt ham for Svøberne, sagde Paulus til den hosstaaende Høvedsmand: „Er det eder tilladt at hudstryge en romersk Mand, og det uden Dom?‟
26 Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
Men da Høvedsmanden hørte dette, gik han til Krigsøversten og meldte ham det og sagde: „Hvad er det, du er ved at gøre? denne Mand er jo en Romer.‟
27 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
Men Krigsøversten gik hen og sagde til ham: „Sig mig, er du en Romer?‟ Han sagde: „Ja.‟
28 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
Og Krigsøversten svarede: „Jeg har købt mig denne Borgerret for en stor Sum.‟ Men Paulus sagde: „Jeg er endog født dertil.‟
29 Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
Da trak de, som skulde til at forhøre ham, sig straks tilbage fra ham. Og da Krigsøversten fik at vide, at han var en Romer, blev ogsaa han bange, fordi han havde bundet ham.
30 Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.
Men den næste Dag, da han vilde have noget paalideligt at vide om, hvad han anklagedes for af Jøderne, løste han ham og befalede, at Ypperstepræsterne og hele Raadet skulde komme sammen, og han førte Paulus ned og stillede ham for dem.

< Ayyukan Manzanni 22 >