< Ayyukan Manzanni 22 >
1 “’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
„Bratři a otcové, rád bych se před vámi obhájil.“
2 Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
Lidé byli překvapeni, že mluví jejich rodným jazykem, a tak tiše poslouchali. Pavel pokračoval:
3 “Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
„Jsem žid, narozený sice v Tarsu v Kilikii, ale vychován jsem byl zde v Jeruzalémě. Vám dobře známý učenec Gamaliel mě vyškolil přesně podle zákona našich otců a horlil jsem pro Boha, právě tak jako vy dnes.
4 Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
Víru v Ježíše Krista jsem nenáviděl k smrti. Dokonce jsem jeho vyznavače, muže i ženy, dával zatýkat a věznit.
5 kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
To mi může dosvědčit velekněz a celá velerada. Jednou mi také vydali pověřující listiny pro židovskou obec v Damašku a já jsem se tam vypravil, abych mezi nimi pozatýkal křesťany a dopravil je do Jeruzaléma k potrestání.
6 “Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
A poslyšte, co se stalo. Bylo kolem poledne a my jsme byli na dohled od damašských hradeb. Náhle se okolo mne rozzářilo oslnivé světlo, mnohem jasnější než polední slunce.
7 Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
Padl jsem na zem, když jsem uslyšel hlas: ‚Saule, Saule, proč mne pronásleduješ?‘
8 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
Ozval jsem se: ‚Kdo jsi, Pane?‘Slyšel jsem odpověď: ‚Já jsem Ježíš z Nazaretu a ty bojuješ proti mně.‘
9 Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
Moji průvodci byli tím světlem také oslněni, ale neslyšeli, že by ke mně někdo mluvil.
10 “Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
Zeptal jsem se: ‚Pane, co mám dělat?‘Ježíš mi odpověděl: ‚Teď vstaň a jdi do Damašku. Tam ti řeknou, jaký mám pro tebe úkol.‘
11 Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
Jas toho světla mne docela oslepil a tak jsem klopýtal do Damašku, veden za ruce svými průvodci.
12 “Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
Tam mne navštívil Ananiáš, zbožný ctitel zákona, kterého si židé v Damašku velice vážili.
13 Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
Přišel a řekl mi: ‚Bratře Saule, otevři oči!‘Tu se mi vrátil zrak a já ho uviděl.
14 “Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
Řekl ještě: ‚Tak to chtěl Bůh, abys konečně poznal jeho vůli, abys uviděl Božího Spravedlivého a uslyšel jeho vlastní hlas.
15 Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
Staneš se Ježíšovým svědkem celému světu a budeš všude vyprávět, co jsi viděl a slyšel.
16 Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
Neváhej, vyznej, že je tvým Pánem, dej se pokřtít na znamení, že jsi očištěn od hříchů.‘
17 “Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
Později, když jsem se vrátil do Jeruzaléma a modlil se v chrámu, měl jsem ještě jedno vidění.
18 na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
Viděl jsem Pána a slyšel jeho slova: ‚Nezdržuj se a rychle odejdi z Jeruzaléma. Tady nepřijmou tvoje svědectví o mně.‘
19 “Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
Ale já jsem odporoval: ‚Pane, tady jsem dával tvoje věrné věznit a bičovat v synagogách.
20 Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
Tady byla prolita první krev, krev tvého svědka Štěpána. Já byl při tom, souhlasil jsem s tím a hlídal jsem pláště těm, kdo ho kamenovali. Všichni to tu o mně vědí.‘
21 “Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
Pán mi však řekl: ‚Jen jdi, protože tě pošlu k pohanům.‘“
22 Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
Až potud dav Pavla pozorně poslouchal, ale zmínka o pohanech je znovu pobouřila. Začali mávat plášti, házeli na něho hrsti prachu a křičeli: „Pryč s tím zrádcem! Na smrt! Nemá tu co dělat!“
23 Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
24 sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
Velitel dal Pavla rychle odvést do pevnosti a nařídil, aby ho zbičovali a vyslechli; chtěl vědět, čím vzbudil tolik nenávisti.
25 Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
Už ho připoutali k bičovací lavici, když se Pavel obrátil k velícímu setníkovi: „Nemáte přece právo bičovat římského občana. Musím být postaven před řádný soud.“
26 Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
Důstojník dal přerušit přípravy, šel k veliteli a hlásil mu: „Stal se nějaký omyl, ten člověk prohlašuje, že je občanem Říma.“
27 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
Velitel s ním šel k Pavlovi a zeptal se: „Je pravda, že jsi římský občan?“„Ano, jsem, “odpověděl vězeň.
28 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
Velitel zapochyboval: „Vím z vlastní zkušenosti, že je to pěkně drahé. Kdepak bys na to vzal?“Pavel řekl: „Já jsem nic nekupoval, jsem občanem od narození.“
29 Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
Po tomto prohlášení vojáci odhodili důtky a spěšně jej odvazovali. Velitel měl obavy, protože se dopustil takového přehmatu vůči rodilému římskému občanu. Rozhodl se, že vyšetří, z čeho židé Pavla vlastně obviňují.
30 Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.
Na velitelovu žádost se nazítří sešla židovská velerada za předsednictví úřadujícího i minulého velekněze.