< Ayyukan Manzanni 22 >

1 “’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
Hmaunawngha hoi a nupanaw, atu kai ni ka dei e lawk kahawicalah thai awh haw telah a dei navah,
2 Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
Hebru lawk hoi a dei e a thai awh navah hoe cing ati awh.
3 “Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
Pawl ni kai teh Cilicia ram Tarshish kho dawk ka khe e, Judah tami buet touh lah ka o. Hatei hete kho dawk ka roung teh, Gamaliel kut rahim vah mintoenaw e phung lawk hah kacaicalah ka kamtu niteh, sahnin nangmouh pueng Cathut hanelah na lung a tang awh e patetlah kai hai ka lung a tang van.
4 Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
Kai ni hete lam ka dawn e napui tongpa tet hoeh, ka pâkhi teh thongim thung ka pakhum teh, a due han ditouh ouk ka rektap toe.
5 kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
Hot patetlah vaihma kacue koehoi kamtawng teh, kacuenaw pueng teh, kai koe lah koung na kampangkhai awh. Kai ni hai ahnimanaw koe ca ka la teh, Damaskas kho e kaawm e, hote phung lah kâen e naw hah man vaiteh rektap hanelah Jerusalem hoi Damaskas lah ka cei.
6 “Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
Hatei Damaskas kho teng ka pha nah, kanîthun e tueng navah, kalvan hoi puenghoi ka ang e ni kai pet na kalup lah pheng a tue.
7 Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
Hahoi kai teh talai ka rawp teh, Sawl Sawl nang ni bangdawk maw, kai hah na rektap vaw telah na dei pouh e lawk ka thai.
8 “Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
Kai ni yah, Bawipa, nang teh apimaw telah ka pacei torei teh, kai teh nang ni na rektap e Nazareth kho e Jisuh doeh, telah na ti pouh.
9 Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
Kai hoi rei kaawm e naw ni angnae a hmu awh eiteh kai hanlah a dei e lawk teh thai awh hoeh.
10 “Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
Kai ni hai Bawipa, bang mouh ka sak han ka ti pouh navah, Bawipa ni thaw nateh Damaskas kho cet haw. Hawvah na sak hane kai ni na dei pouh han na ti pouh.
11 Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
Kai teh hote angnae bahu ni na tue torei teh ka mit a dawn toung dawkvah, rei kaawm e naw ni Damaskas kho na hrawi awh.
12 “Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
Hatnavah Cathut ka bari e Damaskas kho e min kamthang e Judah tami Ananias ni,
13 Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
kai koe a tho teh ka teng a kangdue. Ka nawngha Sawl na mit ang seh ati navah ka mit a ang.
14 “Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
Ahni ni mintoenaw e Cathut ngainae panue sak hanlah thoseh, tamikalan hmu thai nahane thoseh, ahnie lawk dei pouh hane thoseh, nang teh sut na hmoun toe.
15 Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
Nang teh na hmu e hoi na thai e pueng tami pueng e hmalah kapanuekkhaikung lah na o han a ti.
16 Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
Bangkongmaw atu rap na o. Thaw nateh Bawipa min kaw haw. Baptisma coe haw, na yonnae pâsu haw na ti pouh.
17 “Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
Hathnukkhu Jerusalem vah bout ka tho teh, bawkim thung ka ratoum lahun nah ka pouknae a mawm teh, Bawipa hah ka hmu.
18 na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
Bawipa ni kai hoi kâkuen e lawkpanuesaknae hah taminaw ni a dâw awh hoeh han dawkvah, Jerusalem vah rap awm laipalah karang tâcawt leih na ti pouh.
19 “Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
Kai nihaiyah, Bawipa Sinakok buet touh hoi buet touh koe ka cei teh nang na kayuemnaw ka theituk teh thawng ka pabo e a panue awh.
20 Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
Nang kampangkhai lah kaawm e Stiven hah a thei awh navah kai kama roeroe raw hnâbo lahoi ka sak teh, kathetnaw e khohna ka ring pouh kung lah ka o.
21 “Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
Hateiteh, Bawipa ni, Cet leih, ramhlanae koe kaawm e Jentelnaw koe kai ni na patoun han telah kai koe na ti pouh, telah a dei.
22 Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
Het totouh a dei e a thai pouh teh, hot patet e tami hah talai van hring hanelah kamcu hoeh, thet awh titeh lawk kacaipounglah a hram awh.
23 Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
Taminaw niyah hottelah a hramki awh teh, a khohnanaw hah a kahek awh teh, vaiphu kahlun lah a kahei awh
24 sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
Rom ransabawi kalen ni taminaw hah a kaw sak teh, ransaim thung kâen sak hanlah kâ a poe. Taminaw pueng ni bangkongmaw ahni hah telah a taran awh teh, telah a hram awh tie panue hane a ngai dawkvah, ruitaboung hoi hem vaiteh akungkhei hanelah kâ a poe.
25 Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
Ahni teh phaivuenrui hoi a katek awh hnukkhu, a teng kangdout e ransabawi hanlah nangmouh ni Rom tami buet touh heh akungkhei laipalah hemnae kâ na tawn a maw telah a pacei.
26 Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
Ransabawi ni hote lawk hah a thai toteh ransabawi kalen koe a cei teh, nang bangtelamaw ti han. Ahni ni kai teh Rom tami doeh na ti pouh.
27 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
Hahoi ransabawi kalen e teh Pawl koe a tho teh, kai koe na dei pouh haw, nang teh Rom tami na maw telah a pacei toteh ue a atipouh.
28 Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
Ransabawi kalen e ni kai teh, Rom tami lah o nahanelah tangka moikapap poe laihoi doeh ka o thai atipouh navah, Pawl ni, kai teh Rom tami lah ka khe atipouh.
29 Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
Hatdawkvah ahni akungkhei hane naw teh ahni koehoi karanglah a kâkhoe awh. Ransabawi kalen ni hai Pawl heh Rom tami lah ao e hah a panue toteh a pâkhi e hah a taki.
30 Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.
Atangtho vah ransabawi teh Judahnaw ni yon a pen awh e hah kamcengcairalah a panue han a ngai dawkvah, Pawl kateknae rathap hanelah kâ a poe. Vaihma kalennaw hoi lawkcengkungnaw pueng a kamkhueng sak. Pawl hah a kaw awh teh, ahnimae hmalah a kangdue sak awh.

< Ayyukan Manzanni 22 >