< Ayyukan Manzanni 20 >
1 Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
Mipyopyongano mpoyalapwa, Paulo walabunganya beshikwiya. Mpwalamba maswi akubayuminisha, walabalaya walaya ku Makedoniya.
2 Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
Walapitana mubimpansha byonse kaya kuyuminisha beshikwiya, kupitila mukukambauka maswi a Lesa, mpaka walashika ku Gilisi.
3 inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
Uko walekalako myenshi itatu. Mpwalikulibambila bulwendo bwa kuya ku Siliya mubwato, walanyumfwa kwambeti, Bayuda balapangananga sha kumushina. Pacebo ico, walayeyeti enga akupitila ku Makedoniya.
4 Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
Paulo walaya pamo ne bantu aba; Sopatulo mwanendi Pailasi waku Beleya ne Alisitako ne Sekunda, ba ku Tesalonika ne Gayo waku Debe ne Timoti ne Tukiko kayi ne Tulofimo ba micimpansha ca Asiya.
5 Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
Aba balatanguna kushika ku Tulowa, nkobali kutupembelela.
6 Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
Mpobwalapita busuba bwakusekelela shinkwa wabula cishikufufumusha, ne njafwe twalanyamuka ne bwato kufuma ku Filipi. Panyuma pa kwenda bulwendo bwa masuba asanu twalashika ku Tulowa, uko nkotwalabacana. Twalekalako masuba asanu ne abili.
7 A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
Lino pa busuba butanshi bwa nsondo, mpotwalabungana pamo kulya mulalilo wakwanukilapo Mwami Yesu, Paulo walatatika kwambila bantu mpaka pakati pa mashiku, pakwinga walikuyanda kufumako mumene mene.
8 Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
Mwalikuba mimuni ingi mucipinda capelu ca ng'anda njetwalikuba twabunganamo.
9 Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
Mutuloba naumbi musepela lina lyakendi Yutika, walikuba wekalila pa cipense, walatatika kushinshila. Pakwinga Paulo walapitilisha kwamba cindi citali, muntuyu walona tulo, walawa panshi kufuma pelu palupingwe lwabutatu, balacana wafwa.
10 Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
Popelapo Paulo walaseluka panshi, ne kulambalala pamubili wa mutuloba uyu, ne kumufukata. Paulo walabambila bantu balikubapo, “Kamutapenga sobwe, ni muyumi.”
11 Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
Kufumapo Paulo walabwelela mucipinda capelu mung'anda. Walalya mulalilo wakwanukilapo Mwami Yesu pamo ne beshikwiya bonse balikubapo. Walabandika nabo cindi citali. Walafumako kumaca lisuba kalili pepi kupula.
12 Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
Usa mutuloba balamutwala kung'anda kucomwabo kali muyumi ntaa! Neco bonse balekalika myoyo.
13 Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
Popelapo twalatanguna kuya ku Asosi mu bwato. Pakwinga walatwambileti tukakumanine ku Asosi kwambeti nkoti akatantile mu bwato motwalikuba, pakwinga nendi walenda lwa musansa kuya ku Asosi.
14 Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
Mpwalatucana ku Asosi, walatanta mu bwato motwalikuba ne kuya pamo ku Mitileni.
15 Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
Busuba bwakonkapo twalashika pepi ne Kiyosi. Twalenda mpaka twalashika ku Samo. Busuba bwalakonkapo twalashika ku Mileto.
16 Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
Pakwinga Paulo walayeya kupita kumbali kwa munshi wa Efenso, kwambeti katataya cindi citali mu cimpansha ca Asiya. Walikuba wengana pakwinga walikuyandeti na kacikonsheka, akabenga mu Yelusalemu kabutana bushika busuba bwa Pentekosite.
17 Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
Mpwalikuba pa Mileto, Paulo walatuma muntu ku Efenso kuya kubakuwa bamakulene ba mubungano.
18 Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
Mpobalashika walabambileti, “Amwe mucinshi cena ncendalikwikala ne kusebensa pacindi ncendalikuba pamo ne njamwe, kufuma pa busuba mbondalashika mu cimpansha ca Asiya.
19 Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
Ndalasebensela Mwami Yesu mwakulicepesha, nacimbi cindi ndalikulila misoshi cebo ca masunko ngobalikundetela Bayuda mpobalikupangana sha kushina.
20 Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
Mucinshi kwambeti paliya cintu nacikaba cimo, calikuyandika kumunyamfwa ncondalamusoleka, nsombi ndalakambauka ne kumwiyisha makani alambanga sha Yesu, pabantu bangi kayi ne kung'anda ne ng'anda.”
21 Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
Ndalikubacenjesha Bayuda ne bantu bamishobo naimbi, kwambeti belela kusandukila kuli Lesa, ne kushoma Mwami wetu Yesu.
22 “Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
Cebo cakunyumfwila Mushimu Uswepa, pacino cindi ndenga ku Yelusalemu, nomba nkandicinshi ceti cikenshike kuli njame.
23 Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
Ncenjinshowa ni cakwambeti, mu minshi yonse Mushimu Uswepa ulancenjeshengeti, mapensho ne kusungwa mujele kulampembelenga.
24 Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
Nkandasakamananga sha buyumi bwakame sobwe, ncendayandishishinga ni kupwisha ncito njalampa Mwami Yesu, kukambauka Mulumbe Waina ulambanga sha luse ulo luli cipo ca Lesa.
25 “Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
Ndalapitana muli njamwe mwense, kanja kukambauka makani a Bwami bwa Lesa, nomba lino ndicinshi kwambeti nteti mukambonepo sobwe.
26 Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
Neco ndamwambilishinga busuba bwalelo, kwambeti na nabambi mulikoto lyenu ili bakonongeke ntewo mulandu wakame sobwe.
27 Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
Pakwinga paliya cintu naba cimo ncendalamusoleka sobwe. Ndalamwambila byonse mbyalayandanga Lesa.
28 Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
Mwelela kulilama cena mobene, ne kulama cena likoto lya bantu abo Mushimu Uswepa ngowalamupeti mubembelenga. Kamwembelanga cena bantu mu mubungano wa Lesa, abo mbwalapulusheti babe bakendi kupitila mu lufu lwa Mwanendi.
29 Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
Ndicinshi kwambeti ame ndakafumapo pa likoto lyenu, baumpe bakalu nibakese pakati penu, beti bakabule nkumbo ne likoto lya bantu bali mu mubungano.
30 Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
Kayi mu likoto lyenu mobene, nimukapunduke bantu beshikwiyisha bya bwepeshi ne kukwelela bangi kulubasu kwabo, kwambeti babakonkele.
31 Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
Neco, cetukani! Kamwingashilangeti kwa byaka bitatu ndalikumwiyisha mwense munshi ne mashiku, kandila misoshi.
32 “To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
Cakupwililisha, ndamubikinga mu makasa a Lesa, ne mu makani alambanga sha luse lwakendi, elela kumwibaka ne kumupa colwe ico Lesa ncabikila bantu bakendi bonse.
33 Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
Ndiya ku kumbwapo mali, nambi cakufwala camuntu uliyense sobwe.
34 Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
Mobene mucinshi cena kwambeti ndalikusebensa ne makasa akame, kucana byonse byali kuyandika pabuyumi bwakame ne kunyamfwilishako baname mbondalikuba nabo.
35 Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
Mubintu byonsebi ndalamubonesha kwambeti, kusebensa ne ngofu mbuli ncendalikusebensa, inga tunyamfwako abo balefuka. Cindi conse kamwanukanga maswi ngalamba Mwami Yesu, akwambeti, “Kupa kukute kuleta colwe, kupita kutambula.”
36 Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
Mpwalapwisha kwamba, bantu bonse balikuba pamo ne Paulo, balasuntama ne kupaila kuli Lesa.
37 Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
Bonse bali kabalila mwakompolola mpobalamukumbatila Paulo, ne kumushonshonta pakulayana.
38 Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.
Calabapa kungumana ni maswi ngalambeti nteti bakamubonepo kayi. Kufumapo balamushindikila kwalikuba bwato.