< Ayyukan Manzanni 20 >

1 Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
Jitia gondugol to khotom hoise, Paul chela khan ke mati anise aru taikhan ke samjai dise, aru taikhan ke bhidai kori kene tai Macedonia te jai jaise.
2 Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
Titia tai utu desh khan paar kori kene khotom huwa pichete, tai Greece te ahi jaise.
3 inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
Aru tai ta te tin mohina thakise aru ta te pora Syria te jabole thakise, kintu Yehudi khan taike morai dibole thaka jani kene, Macedonia phale pora he wapas jabole bhabi loise.
4 Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
Aru Berea manu Sopater laga chokra, aru Thessalonica pora Aristarchus aru Secundus aru Derbe pora Gaius aru Timothy aru Asia pora Tychicus aru Trophimus taikhan tai logote jaise.
5 Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
Kintu eitu khan amikhan age te jai kene Troas te rukhi thakise.
6 Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
Aru khomir nahala roti laga utsov din pichete amikhan Philippi pora naw te uthi kene pans din pichete Troas te taikhan logot ponchise, aru saat din tak ta te thakise.
7 A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
Titia hapta laga prothom din jitia biswasi chela khan eke loge mili kene roti bhangai sele. Paul dusra dinte jabole thakise, etu karone tai taikhan logot adha rati tak kotha kori thakise.
8 Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
Upor kamra kot te amikhan joma thakisele ta te bisi saaki khan jolai rakhise.
9 Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
Aru Eutychus koi kene jawan ekjon khirki te bohi thakise, aru Paul bisi deri kotha koi thaka pora, tai ghumai kene tin tola upor pora nichete girikena morise.
10 Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
Kintu Paul niche jai kene tai usorte tai laga gaw ke lamba korise, aru taike dhurise. Aru tai koise, “Bhoi nokoribi, kelemane tai laga jibon etiya bhi tai logot he ase.”
11 Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
Titia tai aru upor jai kene roti bhangai khaise aru phojur tak kotha kori thakise, aru etu pichete jai jaise.
12 Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
Aru taikhan utu chokra jinda pa karone ekdom shanti paise.
13 Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
Titia amikhan naw pora Assos te jaise, aru ta te pora naw te Paul ke uthabole thakise, kelemane tai nije pora he tai berai kene jabo koise, aru tai he eneka kori bole amikhan ke koise.
14 Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
Aru tai Assos te ahi amikhan ke lok paise, aru amikhan taike uthaikene Mitylene te ahi jaise.
15 Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
Aru ta te pora naw te uthi kene dusra din Chios usorte ahi jaise, utu din amikhan Samos ponchise, aru Tragyllium te thaki kene dusra din Miletus te ahi Jaise.
16 Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
Kelemane Paul Asia te homoi phelabo mon kora nai, tai naw pora Ephesus paar kori bole mon korise, kelemane parile Pentecost din tai Jerusalem te thakibo mon kori kene tara-tari kori thakisele.
17 Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
Tai Miletus pora khobor pathai kene Ephesus girja laga bura khan ke matise.
18 Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
Aru jitia taikhan tai logot ahise, tai koise, “Moi juntu din pora Asia te ahise, utu prothom din pora kineka moi tumi logote thakise, apnikhan jani ase.”
19 Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
Moi nomrota korise aru suku pani girikena aru Yehudi khan pora chalak kori kene moike dukh di thakile bhi moi Probhu laga sewa kori thakise.
20 Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
Aru moi apnikhan ke sikha khan te, manu usorte nohoile ghor te hoilebi tumi bhal nimite kaam nakori kene chari diya nai.
21 Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
Yehudi aru Yehudi hobi, moi taikhan ke mon ghurai kene Isor phale ahibole aru Jisu ke biswas kori bole sikhai ahise.
22 “Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
Aru sabi, etiya moi Atma laga kotha mani kene Jerusalem te jai ase hoilebi ta te moi logote ki hobo moi najane.
23 Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
Juntu sheher te jaile bhi Pobitro Atma pora ami laga gawah koridi thakise, aru khali bandha aru dukh he moike rukhi ase koi kene.
24 Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
Kintu moi nijor jibon karone eku chinta nathaki, kintu Probhu Jisu pora ji kaam moike kori bole dise, utu Isor anugrah laga susamachar ke khushi pora manu ke jonai dibole aru etu pura kori bole he bhabi thake.
25 “Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
Aru sabi, moi jani ase, moi Isor rajyo kotha loi kene sob jagate prochar koribo, aru apnikhan etiya pora ami laga chehera aru nadikhibo.
26 Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
Etu moi aji apnikhan ke sakhi di ase, moi ekjon golti nathaka manu laga khun phale hoile golti nai.
27 Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
Kelemane Isor laga itcha phale sob kotha moi apuni khan ke koi diya hoise.
28 Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
Etu karone apnikhan nije bhi hoshiar thakibi aru Pobitro Atma pora apnikhan ke sabole mer khan dise. Hoshiar pora Isor laga girja ke roikhya koribi, jintu Isor Tai Nijor laga bacha khun pora kinise.
29 Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
Kelemane moi jani ase moi juwa pichete rong kutta khan tumi laga majote ahibo, aru tumikhan ke nacharibo jun khan etiya bisi ase.
30 Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
Aru moi jani ase tumikhan nijor bhitor pora bhi misa kowa ulabo aru biswasi khan ke taikhan phale kori loi lobo.
31 Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
Karone hoshiar koi kene thakibi, aru bhabona koribi, moi tin saal tak rati din suku pani girai kene sob manu ke sikhaise.
32 “To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
Aru bhai khan moi etiya apnikhan ke di ase, Isor aru tai anugrah laga kotha juntu pora tumikhan ke uthidibo pare aru sapha kori diya khan logote milaikena tai laga miras pabo thaka khan ase.
33 Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
Moi kun laga suna, chandi, kapra khan lalos kora nohoi.
34 Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
Apnikhan jani ase, moi nijor hath pora sewa kori kene nijor aru jun moi logot thakise, taikhan ke ki lage sob kori ahise.
35 Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
Moi apnikhan ke sob rasta sikhai dise, kineka sewa kori kene dukhia khan ke modot koribo lage, aru Probhu Jisu kotha monte bhabona kori bole, juntu Tai nijor pora koise: “Lu-a pora to diya jon he bisi asishit ase.”
36 Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
Aru jitia tai etu kotha koi diya hoise, tai athukari kene taikhan logote prathana kori loise.
37 Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
Titia taikhan sob bisi kandise, aru Paul ke dhori kene taike chuma dise.
38 Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.
Taikhan bisi mon dukh huwa to Paul laga kotha karone hoise, aru kitia bhi tai laga chehera nadikhibo kowa karone, aru taikhan taike loijai kene jahaaj tak punchai dise.

< Ayyukan Manzanni 20 >