< Ayyukan Manzanni 20 >

1 Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
YA anae bumasta y atboroto, jaagang si Pablo y disipulo sija, ya anae jaaconsejo ya jadingo, mapos para Masedonia.
2 Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
Ya anae jajanagüe inanaco ayo sija na lugat, ya janae sija megae na consejo, mapos malag Gresia.
3 inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
Ya sumaga güije tres meses, ya manananggaja para ucone ni y Judios, anae maudae gui batco ya janao para Siria, jajaso na utalo guato Masedonia.
4 Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
Ya maosgaejon asta Asia, si Sopater patgon Pirro guiya Berea, yan iya Tesalónica, si Aristarcho yan si Segundo, yan si Gayo guiya Derbe, yan si Timoteo: ya iya Asia, si Tiquico yan si Trófimo.
5 Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
Este sija manjanao finena, ya janananggajam Troas,
6 Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
Ya despues di y pan sinlibadura, manmaudaejam gui batco desde Filipos, infatoigüe sija guiya Troas gui mina sinco na jaane; ya mañagajam güije siete na jaane.
7 A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
Ya y finenana na jaane gui semana, anae mandaña y disipulo para umaipe y pan, si Pablo japredica guiya sija, sa esta güe listo para ujanao gui inagpaña: ya sisigueja di manpredica asta y tatalopuenge.
8 Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
Ya megae na candet gui sanjilo na cuatto anae estabajam na mandadaña.
9 Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
Ya estaba güije un patgon na taotao na y naanña si Eutico, na matatachong sanjilo gui un bentana, ya guesmaego; ya y inanaco y prinedican Pablo, matomba gui maegoña, ya podong desde y mina tres na piso, ya anae majatsa matae.
10 Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
Ya tumunog papa si Pablo ya dumimo gui jiloña, ya jatogtog ilegña: Chamiyo ninafañachatsaga, sa y linâlâña gaegueja gui sanjalomña.
11 Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
Ya anae cajulo talo, jaipe y pan ya mañocho, ya cumuentos asta qui manana; ya ayonae jumanao.
12 Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
Ya lâlâ patgon na taotao, ya ti didide ninafanmagof.
13 Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
Ya manmaposjam para y batco, ya manmaudaejam guato Asos, sa para ayo nae inquene si Pablo: sa taegüije matagoña, ya malagoñaja ufamocat.
14 Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
Ya anae manasodajam Asos, inquene güe, ya manmatojam Mitilene.
15 Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
Ya desde ayo, manmaudaejam gui batco, ya manmatojam gui inagpaña na jaane gui menan Chio, ya y inagpaña talo güije na jaane, manmatojam Samo, ya mañagajam Trogilio; ya y inagpaña na jaane, manjanaojam para Mileto.
16 Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
Sa si Pablo malagoña umaudae gui batco para Efeso, sa ti malago jagasta y tiempo guiya Asia; sa inalulula, na mano y ninasiñaña, na ufato Jerusalem gui jaanen y Pentecostes.
17 Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
Ya desde Mileto manago guato Efeso na ufanmaagange y manamco gui guimayuus.
18 Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
Ya anae manmato guiya güiya, ilegña nu sija: Injatingo desde y finenenana na jaane anae matoyo Asia, jafa manaemanojit todo y tiempo,
19 Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
Jusetbe y Señot contodo y inimitde na jinaso, yan y minegae lago, yan y tentasion sija ni y manmato guiya guajo pot y ninanggan y Judios.
20 Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
Ya jaftaemano ti maañao yo jusangane jamyo todo y mauleg para jamyo, lao jufanue jamyo yan jufanagüe jamyo, gui publico yan gui guima yan guma.
21 Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
Junamatungo gui Judios yan y Griego sija locue, y sinetsot para as Yuus, yan y jinenggue para y Señotta as Jesucristo.
22 “Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
Ya pago, estagüe y Espiritu na janajanaoyo para Jerusalem, ti jutungo jafa ufanmato guiya guajo güije.
23 Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
Esteja y Espiritu Santo janae yo testimonio na gui cada siudad, ilegña, na y guinede yan y pinite ufañaga guiya guajo.
24 Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
Lao taya güine na güinaja unacalamtenyo, ni ti junaguaguan y linâlâjo para guajo, lao guefmalago yo na junafunjayan y chechojo, yan y obligasionjo ni y juresibe gui Señot Jesus, para junamatungo y ebangelion y grasian Yuus.
25 “Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
Ya pago, estagüe na jutungo jamyo todos, ya ni uno guiya jamyo ni y anae guinin jupredica y raenon Yuus, ulinie y matajo mas.
26 Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
Enao na jucone jamyo para testigo pago na jaane, na guajo gasgasyo guinin todo y jâgâ y taotao sija.
27 Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
Sa trabia ti munjajayan junatungo jamyo todo ni y pinagat Yuus.
28 Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
Guefadaje jamyo, yan todo y manada ni y ninafanmagas jamyo ni y Espiritu Santo, para inapasto inetnon mangilisyano iyon Yuus, ni y jafajan ni y jâgâñaja.
29 Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
Sa jujatungo este, na despues di jumanaoyo, y manaelaye sija na lobo ufanjalom gui entalomiyo, ya ti unasobbla y manada.
30 Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
Ya iya jamyo locue nae ufangajulo sija taotao na jasasangan y manaelaye na güinaja sija, para ufanmangone disipulo sija para udalalag sija.
31 Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
Enaomina adaje, ya injaso na pot tres años, ti pumaparayo jusangane cada uno parejoja jaane yan puenge cumacasaoyo.
32 “To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
Ya pago mañelujo, jutayuyute jamyo as Yuus, yan y sinangan y grasiaña, ni y siña manjinatsa jamyo julo, yan infanninae erensianmiyo yan todo ayo sija y manafangasgas.
33 Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
Sa taya jucodisia ni jaye na taotao, salape pat oro, pat magago.
34 Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
Ya jamyo, intingo este sija na canae y sumesetbeyo gui nesesidajo, yan ayo sija y mangachochongjo.
35 Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
Esta junae jamyo mauleg na ejemplo gui todosija, jaftaemano ya guaja obligasionmiyo na inadaje y manaemetgot yan injaso y sinangan y Señot Jesus, ni y ilegña: Mas dichoso y mannae qui y manresibe.
36 Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
Ya anae munjayan jasangan taegüine, dumimo papa ya manmanayuyut todos.
37 Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
Ya todosija mananges ya matogtog y agâgâ Pablo ya machico.
38 Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.
Ya ninafansenpinite todos pot y sinanganña, na ti ujalie y mataña mas. Ya maosgaejon gui jinanaoña asta y batco.

< Ayyukan Manzanni 20 >