< Ayyukan Manzanni 2 >

1 Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya.
و چون روز پنطیکاست رسید، به یک دل در یکجا بودند.۱
2 Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune.
که ناگاه آوازی چون صدای وزیدن باد شدید از آسمان آمد و تمام آن خانه را که در آنجا نشسته بودند پر ساخت.۲
3 Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu.
وزبانه های منقسم شده، مثل زبانه های آتش بدیشان ظاهر گشته، بر هر یکی از ایشان قرار گرفت.۳
4 Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.
و همه از روح‌القدس پر گشته، به زبانهای مختلف، به نوعی که روح بدیشان قدرت تلفظ بخشید، به سخن‌گفتن شروع کردند.۴
5 To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya.
و مردم یهود دین دار از هر طایفه زیر فلک دراورشلیم منزل می‌داشتند.۵
6 Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa.
پس چون این صدابلند شد گروهی فراهم شده در حیرت افتادندزیرا هر کس لغت خود را از ایشان شنید.۶
7 Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne?
و همه مبهوت و متعجب شده به یکدیگر می‌گفتند: «مگر همه اینها که حرف می‌زنند جلیلی نیستند؟۷
8 To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa?
پس چون است که هر یکی از ما لغت خود را که در آن تولد یافته‌ایم می‌شنویم؟۸
9 Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya,
پارتیان و مادیان و عیلامیان و ساکنان جزیره و یهودیه و کپدکیا وپنطس و آسیا۹
10 Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma
و فریجیه و پمفلیه و مصر ونواحی لبیا که متصل به قیروان است و غربا از روم یعنی یهودیان و جدیدان۱۰
11 (Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!”
و اهل کریت و عرب اینها را می‌شنویم که به زبانهای ما ذکر کبریایی خدا می‌کنند.»۱۱
12 A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”
پس همه در حیرت و شک افتاده، به یکدیگر گفتند: «این به کجا خواهدانجامید؟»۱۲
13 Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”
اما بعضی استهزاکنان گفتند که «ازخمر تازه مست شده‌اند!»۱۳
14 Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa.
پس پطرس با آن یازده برخاسته، آواز خودرا بلند کرده، بدیشان گفت: «ای مردان یهود وجمیع سکنه اورشلیم، این را بدانید و سخنان مرافرا‌گیرید.۱۴
15 Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai!
زیرا که اینها مست نیستند چنانکه شما گمان می‌برید، زیرا که ساعت سوم از روزاست.۱۵
16 A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,
بلکه این همان است که یوئیل نبی گفت۱۶
17 “Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe, zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, samarinku za su ga wahayoyi, dattawanku kuma za su yi mafarkai.
که “خدا می‌گوید در ایام آخر چنین خواهدبود که از روح خود بر تمام بشر خواهم ریخت وپسران و دختران شما نبوت کنند و جوانان شما رویاها و پیران شما خوابها خواهند دید؛۱۷
18 Kai, har ma a kan bayina, maza da mata, zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki, za su kuwa yi annabci.
و برغلامان و کنیزان خود در آن ایام از روح خودخواهم ریخت و ایشان نبوت خواهند نمود.۱۸
19 Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama da alamu a nan ƙasa, jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
واز بالا در افلاک، عجایب و از پایین در زمین، آیات را از خون و آتش و بخار دود به ظهور آورم.۱۹
20 Za a mai da rana duhu, wata kuma ya zama jini, kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
خورشید به ظلمت و ماه به خون مبدل گرددقبل از وقوع روز عظیم مشهور خداوند.۲۰
21 Kuma duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’
وچنین خواهد بود که هر‌که نام خداوند را بخواند، نجات یابد.”۲۱
22 “Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani.
«ای مردان اسرائیلی این سخنان را بشنوید. عیسی ناصری مردی که نزد شما از جانب خدامبرهن گشت به قوات و عجایب و آیاتی که خدادر میان شما از او صادر گردانید، چنانکه خودمی دانید،۲۲
23 An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye.
این شخص چون برحسب اراده مستحکم و پیشدانی خدا تسلیم شد، شما به‌دست گناهکاران بر صلیب کشیده، کشتید،۲۳
24 Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.
که خدا دردهای موت را گسسته، او را برخیزانیدزیرا محال بود که موت او را در بند نگاه دارد،۲۴
25 Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa, “‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana. Gama yana a hannuna na dama, ba zan jijjigu ba.
زیرا که داود درباره وی می‌گوید: “خداوند راهمواره پیش روی خود دیده‌ام که به‌دست راست من است تا جنبش نخورم؛۲۵
26 Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna, jikina kuma zai kasance da bege,
از این سبب دلم شادگردید و زبانم به وجد آمد بلکه جسدم نیز در امیدساکن خواهد بود؛۲۶
27 gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs g86)
زیرا که نفس مرا در عالم اموات نخواهی گذاشت و اجازت نخواهی داد که قدوس تو فساد را ببیند. (Hadēs g86)۲۷
28 Ka sanar da ni hanyoyin rai, za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’
طریقهای حیات را به من آموختی و مرا از روی خود به خرمی سیرگردانیدی.”۲۸
29 “’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau.
«ای برادران، می‌توانم درباره داود پطریارخ با شما بی‌محابا سخن گویم که او وفات نموده، دفن شد و مقبره او تا امروز در میان ماست.۲۹
30 Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa.
پس چون نبی بود و دانست که خدا برای او قسم خوردکه از ذریت صلب او بحسب جسد، مسیح رابرانگیزاند تا بر تخت او بنشیند،۳۰
31 Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs g86)
درباره قیامت مسیح پیش دیده، گفت که نفس او در عالم اموات گذاشته نشود و جسد او فساد را نبیند. (Hadēs g86)۳۱
32 Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan.
پس همان عیسی را خدا برخیزانید و همه ما شاهد برآن هستیم.۳۲
33 An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji.
پس چون به‌دست راست خدا بالابرده شد، روح‌القدس موعود را از پدر یافته، این را که شما حال می‌بینید و می‌شنوید ریخته است.۳۳
34 Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
زیرا که داود به آسمان صعود نکرد لیکن خودمی گوید “خداوند به خداوند من گفت بر دست راست من بنشین۳۴
35 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
تا دشمنانت را پای انداز توسازم.”۳۵
36 “Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”
پس جمیع خاندان اسرائیل یقین بدانندکه خدا همین عیسی را که شما مصلوب کردیدخداوند و مسیح ساخته است.»۳۶
37 Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”
چون شنیدند دلریش گشته، به پطرس وسایر رسولان گفتند: «ای برادران چه کنیم؟»۳۷
38 Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki.
پطرس بدیشان گفت: «توبه کنید و هر یک ازشما به اسم عیسی مسیح بجهت آمرزش گناهان تعمید گیرید و عطای روح‌القدس را خواهیدیافت.۳۸
39 Alkawarin dominku ne da’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”
زیرا که این وعده است برای شما وفرزندان شما و همه آنانی که دورند یعنی هرکه خداوند خدای ما او را بخواند.»۳۹
40 Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.”
و به سخنان بسیار دیگر، بدیشان شهادت داد و موعظه نموده، گفت که «خود را از این فرقه کجرو رستگارسازید.»۴۰
41 Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.
پس ایشان کلام او را پذیرفته، تعمیدگرفتند و در همان روز تخمین سه هزار نفر بدیشان پیوستند۴۱
42 Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a.
و در تعلیم رسولان ومشارکت ایشان و شکستن نان و دعاها مواظبت می‌نمودند.۴۲
43 Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa.
و همه خلق ترسیدند و معجزات وعلامات بسیار از دست رسولان صادر می‌گشت.۴۳
44 Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare.
و همه ایمانداران با هم می‌زیستند و درهمه‌چیز شریک می‌بودند۴۴
45 Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
و املاک و اموال خود را فروخته، آنها را به هر کس به قدراحتیاجش تقسیم می‌کردند.۴۵
46 Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya,
و هر روزه درهیکل به یکدل پیوسته می‌بودند و در خانه‌ها نان را پاره می‌کردند و خوراک را به خوشی وساده دلی می‌خوردند.۴۶
47 suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.
و خدا را حمد می‌گفتندو نزد تمامی خلق عزیز می‌گردیدند و خداوند هرروزه ناجیان را بر کلیسا می‌افزود.۴۷

< Ayyukan Manzanni 2 >