< Ayyukan Manzanni 2 >
1 Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya.
And when the day of Pentecost was fully come, they were all met together with one accord.
2 Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune.
And suddenly there was a sound from heaven as of a strong rushing wind, and it filled all the house where they were sitting.
3 Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu.
And there appeared unto them divided tongues, as it were of fire, and it sat upon each of them:
4 Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.
and they were all filled with the holy Spirit, and began to speak in other languages, as the Spirit gave them utterance.
5 To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya.
Now there were at Jerusalem Jews, devout men, from every nation under heaven.
6 Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa.
And when this rumor was spread, the multitude came together and were astonished; for every one heard them speaking in his own language.
7 Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne?
And they were all amazed and wondered, saying to one another, Behold, are not all these, that are speaking, Galileans?
8 To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa?
and how do we every one hear them in our own native tongue?
9 Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya,
Parthians and Medes and Elamites, and those that dwell in Mesopotamia, and Judea, and Capadocia, Pontus and Asia, Phrygia and Pamphylia,
10 Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma
Egypt and the parts of Libya about Cyrene, and strangers from Rome, Jews and proselytes,
11 (Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!”
Cretans and Arabians, we hear them speaking in our own tongues the wonderful works of God.
12 A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”
And they were all amazed and in doubt, saying one to another, What can this mean?
13 Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”
but others scoffing said, they are full of sweet wine.
14 Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa.
But Peter standing up with the eleven, raised his voice and said unto them, Ye men of Judea, and all ye that dwell at Jerusalem, be this known unto you, and listen to my words:
15 Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai!
for these men are not drunk, as ye suppose; for it is but the third hour of the day.
16 A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,
But this is that which was spoken of by the prophet Joel,
17 “Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe, zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, samarinku za su ga wahayoyi, dattawanku kuma za su yi mafarkai.
"And it shall come to pass in the last days (saith God) that I will pour out of my Spirit upon all flesh, and your sons and your daughters shall prophesy; and your young men shall see visions, and your old men shall dream dreams:
18 Kai, har ma a kan bayina, maza da mata, zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki, za su kuwa yi annabci.
yea and on my servants and on my handmaids, in those days, I will pour out of my Spirit, and they also shall prophesy.
19 Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama da alamu a nan ƙasa, jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
And I will give prodigies in the heaven, and signs upon the earth; blood, and fire, and smoky vapour.
20 Za a mai da rana duhu, wata kuma ya zama jini, kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
The sun shall be turned into darkness, and the moon into blood, before that great and illustrious day of the Lord come.
21 Kuma duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’
And whosoever shall call on the name of the Lord, shall be saved."
22 “Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani.
Ye men of Israel, hear these words; Jesus of Nazareth, a man approved of God among you, by miracles, and prodigies, and signs, which God wrought by Him in the midst of you,
23 An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye.
(as ye yourselves also know, ) Him being given up by the determinate counsel and fore-knowlege of God ye have taken, and by wicked hands have crucified and slain.
24 Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.
Whom God hath raised up again, having loosed the pains of death, because it was not possible that He should be held by it.
25 Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa, “‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana. Gama yana a hannuna na dama, ba zan jijjigu ba.
For David saith concerning Him, "I set the Lord always before me, for He is at my right hand, that I should not be moved: therefore my heart rejoiced, and my tongue was glad;
26 Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna, jikina kuma zai kasance da bege,
and my flesh shall rest in hope,
27 gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs )
that Thou wilt not leave my soul in the invisible state, nor suffer thine holy one to see corruption. (Hadēs )
28 Ka sanar da ni hanyoyin rai, za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’
Thou hast made known to me the ways of life; and Thou wilt fill me with joy by the light of thy countenance."
29 “’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau.
Men and brethren, allow me to speak with freedom to you concerning the patriarch David, that he is dead and buried, and his sepulchre is among us to this day.
30 Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa.
Therefore being a prophet; and knowing that God had sworn to him with an oath, that of the fruit of his loins, according to the flesh, he would raise up the Messiah, to sit on his throne;
31 Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs )
foreseeing this he spake of the resurrection of Christ, when he said, that his soul was not left in the invisible state, nor did his flesh see corruption. (Hadēs )
32 Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan.
This Jesus hath God raised up from the dead, of which we all are witnesses.
33 An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji.
Therefore being exalted by the right hand of God, and having received of the Father the promise of the holy Spirit, He hath poured forth this gift, which ye now see and hear.
34 Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
For David is not ascended into the heavens: but he himself says, "The Lord said to my Lord,
35 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
Sit thou at my right hand, till I make thine enemies thy footstool."
36 “Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”
Therefore let all the house of Israel know assuredly, that God hath made this very Jesus, whom ye crucified, both Lord and Christ.
37 Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”
Now when they heard this, they were pricked to the heart, and said unto Peter, and to the rest of the apostles, Brethren, what shall we do?
38 Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki.
And Peter said unto them, Repent and be baptized every one of you in the name of Jesus Christ, for the remission of your sins, and ye shall receive the gift of the holy Spirit:
39 Alkawarin dominku ne da’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”
for the promise is to you and to your children, yea and to all that are afar off, even as many as the Lord our God shall call.
40 Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.”
And with many other words did he press and exhort them, saying, Save yourselves from this perverse generation.
41 Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.
They therefore that received his word with readiness were baptized: and in that same day there were added unto them about three thousand souls.
42 Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a.
And they continued stedfast in the apostles doctrine, and fellowship, and in the breaking of bread, and in prayers.
43 Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa.
And fear came upon all the people: and many miracles and signs were wrought by the apostles.
44 Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare.
And all that believed were together, and had all things common.
45 Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
And they sold their possessions and goods, and distributed to all, according as any one had need.
46 Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya,
And continuing daily with one accord in the temple, and breaking bread from house to house, they partook of their food with gladness and simplicity of heart,
47 suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.
praising God, and having favor with all the people. And the Lord added to the church daily such as should be saved.