< Ayyukan Manzanni 2 >
1 Da ranar Fentekos ta yi, dukansu suna tare wuri ɗaya.
And in the day of the Pentecost being fulfilled, they were all with one accord at the same place,
2 Ba zato ba tsammani sai aka ji motsi kamar ta babbar iska tana hurowa daga sama ta kuma cika dukan gidan da suke zaune.
and there came suddenly out of the sky a sound as of a violent rushing wind, and it filled all the house where they were sitting,
3 Suka ga wani abin da ya yi kama da harsunan wuta, suka rarrabu suna kuma sassauka a kan kowannensu.
and there appeared to them divided tongues, as it were of fire; it also sat on each one of them,
4 Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka kuma fara magana da waɗansu harsuna yadda Ruhu ya sa suka iya.
and they were all filled with the Holy Spirit, and began to speak with other tongues, according as the Spirit was giving them to declare.
5 To, a Urushalima akwai Yahudawa masu tsoron Allah, daga kowace ƙasa a duniya.
And there were Jews dwelling in Jerusalem, devout men from every nation of those under the heaven,
6 Da suka ji wannan motsi, taro ya haɗu wuri ɗaya a ruɗe, domin kowannensu ya ji suna magana da yarensa.
and the rumor of this having come, the multitude came together, and was confounded, because they were, each one, hearing them speaking in his proper dialect,
7 Cike da mamaki, suka yi tambaya suna cewa, “Ashe, duk waɗannan mutane masu magana ba Galiliyawa ba ne?
and they were all amazed, and wondered, saying to one another, “Behold, are not all these who are speaking Galileans?
8 To, yaya kowannenmu yana ji suna yarensa?
And how do we hear, each in our proper dialect, in which we were born?
9 Fartiyawa, Medes da Elamawa; mazaunan Mesofotamiya, Yahudiya da Kaffadokiya, Fontus da Asiya,
Parthians, and Medes, and Elamites, and those dwelling in Mesopotamia, in Judea also, and Cappadocia, Pontus, and Asia,
10 Firjiya da Famfiliya, Masar da sassa Libiya kusa da Sairin; baƙi daga Roma
Phrygia also, and Pamphylia, Egypt, and the parts of Libya that [are] along Cyrene, and the strangers of Rome, both Jews and proselytes,
11 (Yahudawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci); Kiretawa da Larabawa, mun ji su suna shelar abubuwan banmamaki na Allah da yarenmu!”
Cretes and Arabians, we heard them speaking the great things of God in our tongues.”
12 A ruɗe kuma cike da mamaki, suka tambayi junansu cewa, “Mene ne wannan yake nufi?”
And they were all amazed, and were in doubt, saying to one another, “What would this wish to be?”
13 Duk da haka waɗansu suka yi musu ba’a suka ce, “Sun yi tatil da ruwan inabi ne.”
And others mocking said, “They are full of sweet wine”;
14 Sai Bitrus ya miƙe tsaye tare da Sha Ɗayan nan, ya ɗaga muryarsa ya yi wa taron jawabi ya ce, “’Yan’uwana Yahudawa da dukanku da kuke zama cikin Urushalima, bari in bayyana muku wannan, ku saurara da kyau ga abin da zan faɗa.
and Peter having stood up with the Eleven, lifted up his voice and declared to them: “Men—Jews, and all those dwelling in Jerusalem! Let this be known to you, and listen to my sayings,
15 Waɗannan mutane ba su bugu ba, kamar yadda kuka ɗauka. Yanzu ƙarfe tara na safe ne kawai!
for these are not drunken, as you take it up, for it is the third hour of the day.
16 A’a, ai, abin da aka yi magana ta bakin annabi Yowel ke nan cewa,
But this is that which has been spoken through the prophet Joel:
17 “Allah ya ce, ‘A kwanakin ƙarshe, zan zubo Ruhuna bisa dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, samarinku za su ga wahayoyi, dattawanku kuma za su yi mafarkai.
And it will be in the last days, says God, I will pour out of My Spirit on all flesh, And your sons and your daughters will prophesy, And your young men will see visions, And your old men will dream dreams;
18 Kai, har ma a kan bayina, maza da mata, zan zubo Ruhuna a waɗancan kwanaki, za su kuwa yi annabci.
And also on My menservants, and on My maidservants, In those days, I will pour out of My Spirit, And they will prophesy;
19 Zan nuna abubuwan banmamaki a sararin sama da alamu a nan ƙasa, jini da wuta da kuma hauhawan hayaƙi.
And I will give wonders in the sky above, And signs on the earth beneath—Blood, and fire, and vapor of smoke,
20 Za a mai da rana duhu, wata kuma ya zama jini, kafin zuwa rana mai girma da kuma ta ɗaukaka ta Ubangiji.
The sun will be turned to darkness, And the moon to blood, Before the coming of the Day of the LORD—the great and conspicuous;
21 Kuma duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.’
And it will be, everyone who, if he may have called on the Name of the LORD, will be saved.
22 “Mutanen Isra’ila, ku saurari wannan. Yesu Banazare shi ne mutumin da Allah ya tabbatar muku ta wurin mu’ujizai, ayyukan banmamaki, da kuma alamu, waɗanda Allah ya yi a cikinku ta wurinsa, kamar yadda ku kanku kuka sani.
Men, Israelites! Hear these words: Jesus the Nazarene, a man approved of God among you by mighty works, and wonders, and signs, that God did through Him in the midst of you, according as also you yourselves have known,
23 An ba da wannan mutum gare ku bisa ga nufin Allah da kuma rigyasaninsa, ku kuma tare da taimakon mugayen mutane, kuka kashe shi ta wurin kafa shi a kan gicciye.
this One, by the determinate counsel and foreknowledge of God, being given out, having been taken by lawless hands, having been crucified—you slew,
24 Amma Allah ya tashe shi daga matattu, ya’yantar da shi daga azabar mutuwa, don ba ya yiwuwa mutuwa ta riƙe shi.
whom God raised up, having loosed the travails of death, because it was not possible for Him to be held by it;
25 Dawuda ya yi faɗi game da shi cewa, “‘Kullum ina ganin Ubangiji a gabana. Gama yana a hannuna na dama, ba zan jijjigu ba.
for David says in regard to Him: I foresaw the LORD always before me—Because He is on my right hand—That I may not be moved;
26 Saboda haka, zuciyata na farin ciki, harshena kuma na murna, jikina kuma zai kasance da bege,
Because of this was my heart cheered, And my tongue was glad, And yet—my flesh will also rest on hope,
27 gama ba za ka bar ni cikin kabari ba, ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka yă ruɓa ba. (Hadēs )
Because You will not leave my soul to Hades, Nor will You give Your Holy One to see corruption; (Hadēs )
28 Ka sanar da ni hanyoyin rai, za ka cika ni da farin ciki a gabanka.’
You made known to me ways of life, You will fill me with joy with Your countenance.
29 “’Yan’uwa, zan iya tabbatar muku gabagadi cewa kakanmu Dawuda ya mutu aka kuma binne shi, kabarinsa kuwa yana a nan har yă zuwa yau.
Men, brothers! It is permitted to speak with freedom to you concerning the patriarch David, that he both died and was buried, and his tomb is among us to this day;
30 Amma shi annabi ne ya kuma san abin da Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa zai ɗora ɗaya daga cikin zuriyarsa a kan gadon sarautarsa.
therefore, being a prophet, and knowing that God swore to him with an oath, out of the fruit of his loins, according to the flesh, to raise up the Christ, to sit on his throne,
31 Ganin abin da yake gaba, ya yi magana a kan tashin Kiristi daga matattu cewa, ba a bar shi a kabari ba, jikinsa kuma bai ruɓa ba. (Hadēs )
having foreseen, he spoke concerning the resurrection of the Christ, that His soul was not left to Hades, nor did His flesh see corruption. (Hadēs )
32 Allah ya tashe wannan Yesu zuwa rai, mu kuwa duk shaidu ne ga wannan.
God raised up this Jesus, of which we are all witnesses;
33 An ɗaukaka shi zuwa ga hannun dama na Allah, ya karɓi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga Uba, ya kuma zubo abin da yanzu kuke gani kuke kuma ji.
then having been exalted at the right hand of God—also having received the promise of the Holy Spirit from the Father—He poured forth this which you now see and hear;
34 Gama Dawuda bai hau zuwa sama ba, duk da haka ya ce, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
for David did not go up into the heavens, and he says himself: The LORD says to my Lord, Sit at My right hand,
35 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
Until I make Your enemies Your footstool;
36 “Saboda haka bari dukan Isra’ila su tabbatar da wannan. Allah ya mai da wannan Yesu, da kuka gicciye, Ubangiji da kuma Kiristi.”
assuredly, therefore, let all the house of Israel know that God made Him both Lord and Christ—this Jesus whom you crucified.”
37 Sa’ad da mutane suka ji wannan, sai suka soku a zuci sai suka ce wa Bitrus da sauran manzanni, “’Yan’uwa, me za mu yi?”
And having heard, they were pricked to the heart; they also say to Peter and to the rest of the apostles, “What will we do, men, brothers?”
38 Bitrus ya amsa, “Ku tuba a kuma yi muku baftisma, kowannenku a cikin sunan Yesu Kiristi domin gafarar zunubanku. Za ku kuwa karɓi kyautar Ruhu Mai Tsarki.
And Peter said to them, “Convert, and each of you be immersed on the Name of Jesus Christ, for forgiveness of sins, and you will receive the gift of the Holy Spirit,
39 Alkawarin dominku ne da’ya’yanku da kuma dukan waɗanda suke da nesa, domin dukan waɗanda Ubangiji Allahnmu zai kira.”
for the promise is to you and to your children, and to all those far off, as many as the LORD our God will call.”
40 Da waɗansu kalmomi masu yawa ya gargaɗe su; ya kuma roƙe su cewa, “Ku ceci kanku daga wannan lalataccen zamani.”
Also with many more other words he was testifying and exhorting, saying, “Be saved from this perverse generation”;
41 Waɗanda suka yarda da saƙonsa kuwa aka yi musu baftisma, a ranar kuwa yawansu ya ƙaru da mutum kusan dubu uku.
then those, indeed, who gladly received his word were immersed, and there were added on that day, as it were, three thousand souls,
42 Suka ba da kansu ga koyarwar manzanni da kuma ga zumunci, ga gutsuttsura burodin da kuma ga addu’a.
and they were continuing steadfastly in the teaching of the apostles, and the fellowship, and the breaking of the bread, and the prayers.
43 Kowa ya cika da tsoro, manzannin kuwa suka aikata abubuwan banmamaki da alamu masu yawa.
And fear came on every soul, also many wonders and signs were being done through the apostles,
44 Dukan masu bi suna tare, suna kuma mallakar kome tare.
and all those believing were at the same place, and had all things common,
45 Suka dinga sayar da ƙaddarorinsu da kayayyakinsu, suka ba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
and they were selling the possessions and the goods, and were parting them to all, according as anyone had need.
46 Kowace rana suka ci gaba da taruwa a filin haikali. Suka gutsuttsura burodi a gidajensu suna cin abinci tare da farin ciki da zuciya ɗaya,
Also continuing daily with one accord in the temple, also breaking bread at every house, they were partaking of food in gladness and simplicity of heart,
47 suna yabon Allah suna kuma samun tagomashin dukan mutane. Ubangiji kuwa ya ƙara yawansu kowace rana na waɗanda suke samun ceto.
praising God, and having favor with all the people, and the LORD was adding those being saved every day to the Assembly.