< Ayyukan Manzanni 19 >
1 Lokacin da Afollos yake a Korint, Bulus ya bi hanyar da ta ratsa ta Asiya ya zo Afisa. A can ya sadu da waɗansu almajirai,
And it came to pass, in Apollos' being in Corinth, Paul having gone through the upper parts, came to Ephesus, and having found certain disciples,
2 sai ya tambaye, su ya ce, “Kun karɓi Ruhu Mai Tsarki sa’ad da kuka gaskata?” Suka amsa suka ce, “A’a, ba mu ma san akwai Ruhu Mai Tsarki ba.”
he said unto them, 'The Holy Spirit did ye receive — having believed?' and they said unto him, 'But we did not even hear whether there is any Holy Spirit;'
3 Saboda haka Bulus ya yi tambaya ya ce, “To, wace baftisma aka yi muku?” Suka ce, “Baftismar Yohanna.”
and he said unto them, 'To what, then, were ye baptized?' and they said, 'To John's baptism.'
4 Bulus ya ce, “Ai, baftismar Yohanna, baftisma ce ta tuba. Ya ce wa mutane su gaskata a wani wanda yake zuwa bayansa, wato, Yesu.”
And Paul said, 'John, indeed, did baptize with a baptism of reformation, saying to the people that in him who is coming after him they should believe — that is, in the Christ — Jesus;'
5 Da ji wannan, sai aka yi musu baftisma a cikin sunan Ubangiji Yesu.
and they, having heard, were baptized — to the name of the Lord Jesus,
6 Da Bulus ya ɗibiya musu hannuwansa, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka musu, suka kuwa yi magana da harsuna, suka kuma yi annabci.
and Paul having laid on them [his] hands, the Holy Spirit came upon them, they were speaking also with tongues, and prophesying,
7 Mutane kuwa su wajen mutum goma sha biyu ne.
and all the men were, as it were, twelve.
8 Bulus ya shiga majami’a ya yi magana gabagadi a can na watanni uku, yana muhawwara yana kuma rinjayarsu game da mulkin Allah.
And having gone into the synagogue, he was speaking boldly for three months, reasoning and persuading the things concerning the reign of God,
9 Amma waɗansunsu suka taurara; suka ƙi su gaskata kuma a gaban jama’a suka yi baƙar magana game da Hanyar. Bulus kuwa ya bar su. Ya tafi tare da almajirai ya dinga tattaunawa da su kullum a babban ɗakin jawabi na Tirannus.
and when certain were hardened and were disbelieving, speaking evil of the way before the multitude, having departed from them, he did separate the disciples, every day reasoning in the school of a certain Tyrannus.
10 Wannan ya ci gaba har shekara biyu, sai da ya sa dukan Yahudawa da Hellenawa da suke zaune a lardin Asiya suka ji maganar Ubangiji.
And this happened for two years so that all those dwelling in Asia did hear the word of the Lord Jesus, both Jews and Greeks,
11 Allah ya yi ayyukan banmamakin da suka wuce misali ta hannu Bulus,
mighty works also — not common — was God working through the hands of Paul,
12 har ma ana kai hankicif da adikan da suka taɓa jikinsa wa marasa lafiya, suka kuwa warke daga cututtukansu mugayen ruhohi kuma suka rabu da su.
so that even unto the ailing were brought from his body handkerchiefs or aprons, and the sicknesses departed from them; the evil spirits also went forth from them.
13 Waɗansu Yahudawa masu yawo gari-gari suna fitar da mugayen ruhohi suka yi ƙoƙari su yi amfani da sunan Ubangiji Yesu a kan waɗanda suke da aljanu. Suna cewa, “A cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa’azi, na umarce ku, ku fito.”
And certain of the wandering exorcist Jews, took upon [them] to name over those having the evil spirits the name of the Lord Jesus, saying, 'We adjure you by Jesus, whom Paul doth preach;'
14 ’Ya’ya bakwai maza na Sikeba, wani babban firist na Yahudawa, suna yin haka.
and there were certain — seven sons of Sceva, a Jew, a chief priest — who are doing this thing;
15 Wata rana mugun ruhu ya amsa musu ya ce, “Yesu kam na sani, Bulus kuma na sani, amma ku kuma su wane ne?”
and the evil spirit, answering, said, 'Jesus I know, and Paul I am acquainted with; and ye — who are ye?'
16 Sai mutumin da yake da mugun ruhun ya fāɗa musu ya sha ƙarfinsu duka. Ya yi musu dūkan tsiya har suka fita a guje daga gidan tsirara jini yana zuba.
And the man, in whom was the evil spirit, leaping upon them, and having overcome them, prevailed against them, so that naked and wounded they did flee out of that house,
17 Da Yahudawa da Hellenawan da suke zama a Afisa suka ji wannan labari sai duk tsoro ya kama su, aka kuwa darjanta sunan Ubangiji Yesu ƙwarai.
and this became known to all, both Jews and Greeks, who are dwelling at Ephesus, and fear fell upon them all, and the name of the Lord Jesus was being magnified,
18 Da yawa cikin waɗanda suka gaskata yanzu suka zo a fili suka furta mugayen ayyukansu.
many also of those who did believe were coming, confessing and declaring their acts,
19 Waɗansu masu yin sihiri suka kawo naɗaɗɗun littattafansu wuri ɗaya suka kuwa ƙone su a gaban jama’a. Sa’ad da aka lissafta yawan kuɗin naɗaɗɗun littattafan nan, sai jimillar ta kai darik dubu hamsin.
and many of those who had practised the curious arts, having brought the books together, were burning [them] before all; and they reckoned together the prices of them, and found [it] five myriads of silverlings;
20 Ta haka maganar Ubangiji ta bazu ko’ina ta kuma yi ƙarfi.
so powerfully was the word of God increasing and prevailing.
21 Bayan dukan wannan ya faru, sai Bulus ya yanke shawara ya ratsa Makidoniya da Akayya in za shi Urushalima. Ya kuma ce, “Bayan na tafi can, dole in ziyarci Roma ita ma.”
And when these things were fulfilled, Paul purposed in the Spirit, having gone through Macedonia and Achaia, to go on to Jerusalem, saying — 'After my being there, it behoveth me also to see Rome;'
22 Sai ya aiki biyu daga cikin masu taimakonsa, Timoti da Erastus, zuwa Makidoniya, yayinda shi kuwa ya ɗan dakata a lardin Asiya.
and having sent to Macedonia two of those ministering to him — Timotheus and Erastus — he himself stayed a time in Asia.
23 Kusan wannan lokaci sai aka yi wani babban hargitsi game da wannan Hanyar.
And there came, at that time, not a little stir about the way,
24 Wani maƙerin azurfa, mai suna Demetiriyus wanda yake ƙera siffar ɗakunan tsafin Artemis da azurfa, ba ƙaramin ciniki yake kawo wa mutane masu sana’an nan ba.
for a certain one, Demetrius by name, a worker in silver, making silver sanctuaries of Artemis, was bringing to the artificers gain not a little,
25 Sai ya tara su wuri ɗaya, tare da masu irin wannan sana’ar ya ce, “Ku jama’a, kun san muna samun kuɗin shiga sosai daga wannan sana’a.
whom, having brought in a crowd together, and those who did work about such things, he said, 'Men, ye know that by this work we have our wealth;
26 Kuma kuna ji kuna gani yadda Bulus ɗin nan ya shawo kan mutane da yawa ya kuma sa suka bauɗe a nan a Afisa da dukan lardin Asiya. Yana cewa alloli da mutum ya ƙera ba alloli ba ne ko kaɗan.
and ye see and hear, that not only at Ephesus, but almost in all Asia, this Paul, having persuaded, did turn away a great multitude, saying, that they are not gods who are made by hands;
27 Akwai hatsari, ba kawai cewa sana’armu za tă rasa sunanta mai daraja ba, amma za a yi banza da ɗakin tsafin Artemis alliyarmu mai girma, alliyar kanta wadda ake bauta a ko’ina a yankin Asiya da kuma duniya, za a raba ta da darajarta.”
and not only is this department in danger for us of coming into disregard, but also, that of the great goddess Artemis the temple is to be reckoned for nothing, and also her greatness is about to be brought down, whom all Asia and the world doth worship.'
28 Da suka ji haka, sai suka yi fushi ƙwarai suka fara ihu suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”
And they having heard, and having become full of wrath, were crying out, saying, 'Great [is] the Artemis of the Ephesians!'
29 Jim kaɗan sai hayaniya ta tashi a dukan birnin. Sai mutane suka cafke Gayus da Aristarkus, abokan tafiyar Bulus daga Makidoniya, suka ruga da zuwa fili da nufi ɗaya.
and the whole city was filled with confusion, they rushed also with one accord into the theatre, having caught Gaius and Aristarchus, Macedonians, Paul's fellow-travellers.
30 Bulus ya so ya bayyana a gaban taron, amma almajirai ba su bar shi ba.
And on Paul's purposing to enter in unto the populace, the disciples were not suffering him,
31 Har waɗansu shugabannin lardin ma, abokan Bulus, suka aika masa suna roƙonsa kada yă kuskura ya shiga filin nan.
and certain also of the chief men of Asia, being his friends, having sent unto him, were entreating him not to venture himself into the theatre.
32 Taron kuwa ya ruɗe. Waɗansu suna ihu suna ce abu kaza, waɗansu kuma wani abu dabam. Yawancin mutane kuma ba su ma san abin da ya sa suke a wurin ba.
Some indeed, therefore, were calling out one thing, and some another, for the assembly was confused, and the greater part did not know for what they were come together;
33 Yahudawa suka tura Alekzanda gaba, sai waɗansu a taron suka riƙa yin masa ihu. Sai ya ɗaga hannu don a yi shiru don yă kāre kansa a gaban mutane.
and out of the multitude they put forward Alexander — the Jews thrusting him forward — and Alexander having beckoned with the hand, wished to make defence to the populace,
34 Amma sa’ad da suka gane shi mutumin Yahuda ne, sai duk suka yi ihu gaba ɗaya na kusa sa’a biyu, suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”
and having known that he is a Jew, one voice came out of all, for about two hours, crying, 'Great [is] the Artemis of the Ephesians!'
35 Sai magatakardar birnin ya sa taron su yi shiru, sa’an nan ya ce, “Mutanen Afisa, ashe duk duniya ba tă san cewa birnin Afisa ce mai lura da haikalin Artemis mai girma da kuma siffarta da ya fāɗi daga sama ba?
And the public clerk having quieted the multitude, saith, 'Men, Ephesians, why, who is the man that doth not know that the city of the Ephesians is a devotee of the great goddess Artemis, and of that which fell down from Zeus?
36 Saboda haka, da yake ba dama a yi mūsun wannan gaskiya, ya kamata ku natsu kada ku yi kome da garaje.
these things, then, not being to be gainsaid, it is necessary for you to be quiet, and to do nothing rashly.
37 Kun kawo mutanen nan a nan, gashi kuwa ba su yi fashin haikali ba, ba su kuwa saɓa wa alliyarmu ba.
'For ye brought these men, who are neither temple-robbers nor speaking evil of your goddess;
38 To, in haka ne, in Demetiriyus da abokan sana’arsa suna da wata magana game da wani ai, kotuna suna nan a buɗe, akwai kuma muƙaddasai. Suna iya kai ƙara.
if indeed, therefore, Demetrius and the artificers with him with any one have a matter, court [days] are held, and there are proconsuls; let them accuse one another.
39 In kuma akwai wani abu har yanzu da kuke so ku kawo, dole a daidaita shi a majalisa.
'And if ye seek after anything concerning other matters, in the legal assembly it shall be determined;
40 Yadda yake a yanzu, muna a hatsarin amsa zargin ta da hargitsi saboda abin da ya faru yau. Da yake ba za mu iya ba da dalilin da ya sa aka yi wannan hargitsi ba.”
for we are also in peril of being accused of insurrection in regard to this day, there being no occasion by which we shall be able to give an account of this concourse;'
41 Bayan da ya faɗi haka, sai ya sallami taron.
and these things having said, he dismissed the assembly.