< Ayyukan Manzanni 19 >
1 Lokacin da Afollos yake a Korint, Bulus ya bi hanyar da ta ratsa ta Asiya ya zo Afisa. A can ya sadu da waɗansu almajirai,
And it came to pass, while Apollos was in Corinth, Paul having come through the upper regions came down into Ephesus: and found certain disciples,
2 sai ya tambaye, su ya ce, “Kun karɓi Ruhu Mai Tsarki sa’ad da kuka gaskata?” Suka amsa suka ce, “A’a, ba mu ma san akwai Ruhu Mai Tsarki ba.”
and said to them, Have you received the Holy Ghost, having believed? And they said to him, But we have not heard if the Holy Ghost is (given).
3 Saboda haka Bulus ya yi tambaya ya ce, “To, wace baftisma aka yi muku?” Suka ce, “Baftismar Yohanna.”
And he said, Into what then were you baptized? And they said, Into the baptism of John.
4 Bulus ya ce, “Ai, baftismar Yohanna, baftisma ce ta tuba. Ya ce wa mutane su gaskata a wani wanda yake zuwa bayansa, wato, Yesu.”
And Paul said, John baptized with the baptism of repentance, saying unto the people, that they should believe on the one coming after him, that is Jesus.
5 Da ji wannan, sai aka yi musu baftisma a cikin sunan Ubangiji Yesu.
And they, having heard, were baptized into the name of the Lord Jesus;
6 Da Bulus ya ɗibiya musu hannuwansa, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka musu, suka kuwa yi magana da harsuna, suka kuma yi annabci.
and Paul having laid his hands on them, the Holy Ghost came on them; and they continued to speak with tongues, and prophesy.
7 Mutane kuwa su wajen mutum goma sha biyu ne.
And they were all about twelve men.
8 Bulus ya shiga majami’a ya yi magana gabagadi a can na watanni uku, yana muhawwara yana kuma rinjayarsu game da mulkin Allah.
And having come into the synagogue, he preached boldly three months, expounding and persuading them as to the things concerning the kingdom of God.
9 Amma waɗansunsu suka taurara; suka ƙi su gaskata kuma a gaban jama’a suka yi baƙar magana game da Hanyar. Bulus kuwa ya bar su. Ya tafi tare da almajirai ya dinga tattaunawa da su kullum a babban ɗakin jawabi na Tirannus.
But when some were becoming hardened and disbelieving, speaking evil of the way in the presence of the multitude, departing from them he separated his disciples, daily expounding in the school of Tyrannus.
10 Wannan ya ci gaba har shekara biyu, sai da ya sa dukan Yahudawa da Hellenawa da suke zaune a lardin Asiya suka ji maganar Ubangiji.
And this took place two years; so that all dwelling in Asia heard the word of the Lord, both Jews and Greeks.
11 Allah ya yi ayyukan banmamakin da suka wuce misali ta hannu Bulus,
And God was working great miracles through the hands of Paul;
12 har ma ana kai hankicif da adikan da suka taɓa jikinsa wa marasa lafiya, suka kuwa warke daga cututtukansu mugayen ruhohi kuma suka rabu da su.
so that napkins and aprons were carried from his body and placed on the sick, and diseases departed from them, and evil spirits went out of them.
13 Waɗansu Yahudawa masu yawo gari-gari suna fitar da mugayen ruhohi suka yi ƙoƙari su yi amfani da sunan Ubangiji Yesu a kan waɗanda suke da aljanu. Suna cewa, “A cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa’azi, na umarce ku, ku fito.”
And certain ones of the itinerant Jewish exorcists undertook to call the name of the Lord Jesus, over those having evil spirits saying, I adjure you in the name of Jesus whom Paul is preaching.
14 ’Ya’ya bakwai maza na Sikeba, wani babban firist na Yahudawa, suna yin haka.
And there were certain seven sons of one Sceva, a Jewish high priest, doing this.
15 Wata rana mugun ruhu ya amsa musu ya ce, “Yesu kam na sani, Bulus kuma na sani, amma ku kuma su wane ne?”
But the evil spirit responding said to them, I know Jesus, and am acquainted with Paul; but who are you?
16 Sai mutumin da yake da mugun ruhun ya fāɗa musu ya sha ƙarfinsu duka. Ya yi musu dūkan tsiya har suka fita a guje daga gidan tsirara jini yana zuba.
And the man in whom was the evil spirit, leaping on them, domineering over both of them, prevailed against them, so that they fled out of that house naked and wounded.
17 Da Yahudawa da Hellenawan da suke zama a Afisa suka ji wannan labari sai duk tsoro ya kama su, aka kuwa darjanta sunan Ubangiji Yesu ƙwarai.
And this became known to all, both Jews and Greeks, dwelling at Ephesus; and fear fell upon them all, and the name of the Lord Jesus was magnified;
18 Da yawa cikin waɗanda suka gaskata yanzu suka zo a fili suka furta mugayen ayyukansu.
and many of those having believed came, confessing, and renouncing their practices.
19 Waɗansu masu yin sihiri suka kawo naɗaɗɗun littattafansu wuri ɗaya suka kuwa ƙone su a gaban jama’a. Sa’ad da aka lissafta yawan kuɗin naɗaɗɗun littattafan nan, sai jimillar ta kai darik dubu hamsin.
And many of those practicing curious arts, having brought their books, burnt them before all: and they estimated the price of them, and found it to be fifty thousand pieces of silver.
20 Ta haka maganar Ubangiji ta bazu ko’ina ta kuma yi ƙarfi.
Thus the word of the Lord increased and accumulated strength according to His power.
21 Bayan dukan wannan ya faru, sai Bulus ya yanke shawara ya ratsa Makidoniya da Akayya in za shi Urushalima. Ya kuma ce, “Bayan na tafi can, dole in ziyarci Roma ita ma.”
And when these things were fulfilled, Paul purposed in spirit, having traveled through Macedonia and Achaia, to go on into Jerusalem, saying that, After I am there it behooves me also to see Rome.
22 Sai ya aiki biyu daga cikin masu taimakonsa, Timoti da Erastus, zuwa Makidoniya, yayinda shi kuwa ya ɗan dakata a lardin Asiya.
And having sent two of those ministering to him, Timothy and Erastus, into Macedonia, himself spent the time in Asia.
23 Kusan wannan lokaci sai aka yi wani babban hargitsi game da wannan Hanyar.
And at that time there was no small commotion concerning the way.
24 Wani maƙerin azurfa, mai suna Demetiriyus wanda yake ƙera siffar ɗakunan tsafin Artemis da azurfa, ba ƙaramin ciniki yake kawo wa mutane masu sana’an nan ba.
For a certain Demetrius by name, a silversmith, making silver shrines of Diana, was bringing no small gain to the mechanics,
25 Sai ya tara su wuri ɗaya, tare da masu irin wannan sana’ar ya ce, “Ku jama’a, kun san muna samun kuɗin shiga sosai daga wannan sana’a.
whom having assembled and the laborers about such things, he said, Men, you know that it is from this work that prosperity is to us:
26 Kuma kuna ji kuna gani yadda Bulus ɗin nan ya shawo kan mutane da yawa ya kuma sa suka bauɗe a nan a Afisa da dukan lardin Asiya. Yana cewa alloli da mutum ya ƙera ba alloli ba ne ko kaɗan.
and you see and hear, that not only at Ephesus, but almost throughout all Asia, that this Paul having persuaded them has turned away a great multitude, saying that there are no gods made with hands.
27 Akwai hatsari, ba kawai cewa sana’armu za tă rasa sunanta mai daraja ba, amma za a yi banza da ɗakin tsafin Artemis alliyarmu mai girma, alliyar kanta wadda ake bauta a ko’ina a yankin Asiya da kuma duniya, za a raba ta da darajarta.”
And not only is this interest in danger to us to come into disrepute; but even the temple of the great goddess Diana to be considered for nought, and they are about even to despise the majesty of her, whom all Asia and the world worships.
28 Da suka ji haka, sai suka yi fushi ƙwarai suka fara ihu suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”
And hearing and being filled with rage, they continued to cry out, saying, Great is Diana of the Ephesians.
29 Jim kaɗan sai hayaniya ta tashi a dukan birnin. Sai mutane suka cafke Gayus da Aristarkus, abokan tafiyar Bulus daga Makidoniya, suka ruga da zuwa fili da nufi ɗaya.
And the city was filled with commotion: and they rushed of one accord into the theatre, seizing Gaius and Aristarchus, the Macedonians, the companions of Paul.
30 Bulus ya so ya bayyana a gaban taron, amma almajirai ba su bar shi ba.
And Paul wishing to go in unto the people, the disciples suffered him not;
31 Har waɗansu shugabannin lardin ma, abokan Bulus, suka aika masa suna roƙonsa kada yă kuskura ya shiga filin nan.
and certain ones of the Asiatic rulers, also being friends to him, having sent to him, continued to entreat him not to give himself up into the theatre.
32 Taron kuwa ya ruɗe. Waɗansu suna ihu suna ce abu kaza, waɗansu kuma wani abu dabam. Yawancin mutane kuma ba su ma san abin da ya sa suke a wurin ba.
Then indeed they continued to cry out some one thing, and some another: for the church was confused; and the most of them did not know on account of what they had come together.
33 Yahudawa suka tura Alekzanda gaba, sai waɗansu a taron suka riƙa yin masa ihu. Sai ya ɗaga hannu don a yi shiru don yă kāre kansa a gaban mutane.
And some from the crowd forced in Alexander, the Jews precipitating him forward; and Alexander, beckoning with his hand, wished to apologize to the people.
34 Amma sa’ad da suka gane shi mutumin Yahuda ne, sai duk suka yi ihu gaba ɗaya na kusa sa’a biyu, suna cewa, “Girma ta tabbata ga Artemis ta Afisawa!”
But recognizing that he is a Jew, there was one voice from all crying out about two hours, Great is Diana of the Ephesians.
35 Sai magatakardar birnin ya sa taron su yi shiru, sa’an nan ya ce, “Mutanen Afisa, ashe duk duniya ba tă san cewa birnin Afisa ce mai lura da haikalin Artemis mai girma da kuma siffarta da ya fāɗi daga sama ba?
And the city clerk having dismissed the multitudes, said, Ephesian men, for what one of men is there that does not know that the city of the Ephesians is a worshiper of the great goddess Diana, and of the statue having fallen down from Jupiter?
36 Saboda haka, da yake ba dama a yi mūsun wannan gaskiya, ya kamata ku natsu kada ku yi kome da garaje.
Therefore these things being unquestionable, it is necessary that you become calm, and do nothing rashly.
37 Kun kawo mutanen nan a nan, gashi kuwa ba su yi fashin haikali ba, ba su kuwa saɓa wa alliyarmu ba.
For you have led in these men, who are neither robbers of temples, nor are they blaspheming your goddess.
38 To, in haka ne, in Demetiriyus da abokan sana’arsa suna da wata magana game da wani ai, kotuna suna nan a buɗe, akwai kuma muƙaddasai. Suna iya kai ƙara.
If indeed therefore Demetrius, and the mechanics along with him, have a charge against any one, the courts are in session, and there are lawyers: let them implead one another.
39 In kuma akwai wani abu har yanzu da kuke so ku kawo, dole a daidaita shi a majalisa.
But if you are seeking something concerning other things, it shall be settled in the lawful church.
40 Yadda yake a yanzu, muna a hatsarin amsa zargin ta da hargitsi saboda abin da ya faru yau. Da yake ba za mu iya ba da dalilin da ya sa aka yi wannan hargitsi ba.”
For indeed we are in danger of prosecution for the disturbance this day, there being no cause concerning which we shall be able to give a reason for this uproar.
41 Bayan da ya faɗi haka, sai ya sallami taron.
And having said these things, he dismissed the church.