< Ayyukan Manzanni 18 >

1 Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
Après cela, Paul partit d'Athènes et se rendit à Corinthe.
2 A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
Il trouva un Juif nommé Aquila, originaire du Pont, qui venait d'arriver d'Italie avec sa femme Priscille, car Claude avait ordonné à tous les Juifs de quitter Rome. Il vint chez eux,
3 da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
et, comme il exerçait le même métier, il habitait avec eux et travaillait, car ils étaient fabricants de tentes.
4 Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
Il faisait des discours dans la synagogue tous les sabbats et persuadait Juifs et Grecs.
5 Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
Lorsque Silas et Timothée furent descendus de Macédoine, Paul, poussé par l'Esprit, témoigna aux Juifs que Jésus était le Christ.
6 Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
Comme ils s'opposaient à lui et blasphémaient, il secoua ses vêtements et leur dit: « Que votre sang retombe sur vos têtes! Je suis pur. Désormais, j'irai vers les païens! »
7 Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
Il partit de là et entra dans la maison d'un homme nommé Justus, adorateur de Dieu, dont la maison était voisine de la synagogue.
8 Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
Crispus, le chef de la synagogue, crut au Seigneur avec toute sa maison. Beaucoup de Corinthiens, après avoir entendu cela, crurent et furent baptisés.
9 Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
Le Seigneur dit à Paul, la nuit, dans une vision: « Ne crains pas, mais parle et ne te tais pas;
10 Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
car je suis avec toi, et personne ne t'attaquera pour te faire du mal, car j'ai beaucoup de monde dans cette ville. »
11 Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
Il demeura là un an et six mois, enseignant la parole de Dieu au milieu d'eux.
12 Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
Mais, lorsque Gallion fut proconsul d'Achaïe, les Juifs, d'un commun accord, se soulevèrent contre Paul et l'amenèrent devant le tribunal,
13 Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
en disant: « Cet homme persuade les hommes d'adorer Dieu contrairement à la loi. »
14 A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
Comme Paul allait ouvrir la bouche, Gallion dit aux Juifs: « S'il s'agissait en effet d'une affaire de mal ou de crime, vous les Juifs, il serait raisonnable que je vous supporte;
15 Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
mais s'il s'agit de questions de mots et de noms et de votre propre loi, regardez vous-mêmes. Car je ne veux pas être juge de ces questions. »
16 Saboda haka ya kore su.
Il les chassa donc du tribunal.
17 Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
Alors tous les Grecs se saisirent de Sosthène, le chef de la synagogue, et le battirent devant le tribunal. Gallio ne se souciait d'aucune de ces choses.
18 Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
Paul, ayant séjourné encore plusieurs jours après cela, prit congé des frères, et s'embarqua de là pour la Syrie, avec Priscille et Aquila. Il se rasa la tête à Cenchrées, car il avait fait un vœu.
19 Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
Il arriva à Éphèse, où il les laissa, mais il entra lui-même dans la synagogue et discuta avec les Juifs.
20 Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
Lorsqu'ils lui demandèrent de rester plus longtemps avec eux, il refusa;
21 Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
mais, prenant congé d'eux, il dit: « Je dois absolument célébrer la fête qui vient à Jérusalem, mais je reviendrai chez vous si Dieu le veut. » Puis il partit d'Éphèse.
22 Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
Après avoir débarqué à Césarée, il monta et salua l'assemblée, puis il descendit à Antioche.
23 Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
Après y avoir passé quelque temps, il partit et traversa la région de la Galatie et de la Phrygie, pour établir tous les disciples.
24 Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
Or, un Juif nommé Apollos, de race alexandrine, homme éloquent, vint à Éphèse. Il était versé dans les Écritures.
25 An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
Cet homme avait été instruit dans la voie du Seigneur; et, fervent d'esprit, il parlait et enseignait avec exactitude les choses concernant Jésus, bien qu'il ne connût que le baptême de Jean.
26 Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
Il se mit à parler avec assurance dans la synagogue. Mais Priscille et Aquila, l'ayant entendu, le prirent à part et lui expliquèrent plus exactement la voie de Dieu.
27 Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
Lorsqu'il eut décidé de passer en Achaïe, les frères l'encouragèrent, et ils écrivirent aux disciples de le recevoir. Lorsqu'il fut arrivé, il aida beaucoup ceux qui avaient cru par la grâce;
28 Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.
car il réfutait avec force les Juifs, démontrant publiquement par les Écritures que Jésus était le Christ.

< Ayyukan Manzanni 18 >