< Ayyukan Manzanni 18 >
1 Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
After these things, having departed from Athens, he arrived at Corinth.
2 A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
And upon finding a certain Jew named Aquila, born in Pontus, who had recently arrived from Italy with Priscilla his wife, (because Claudius had ordered all Jews to depart from Rome, ) he met with them.
3 da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
And because he was of the same trade, he lodged with them and was working. (Now they were tentmakers by trade.)
4 Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
And he was arguing in the synagogue on every Sabbath, introducing the name of the Lord Jesus. And he was persuading Jews and Greeks.
5 Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
And when Silas and Timothy had arrived from Macedonia, Paul stood firm in the Word, testifying to the Jews that Jesus is the Christ.
6 Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
But since they were contradicting him and blaspheming, he shook out his garments and said to them: “Your blood is on your own heads. I am clean. From now on, I will go to the Gentiles.”
7 Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
And moving from that place, he entered into the house of a certain man, named Titus the Just, a worshiper of God, whose house was adjoined to the synagogue.
8 Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
Now Crispus, a leader of the synagogue, believed in the Lord, with his entire house. And many of the Corinthians, upon hearing, believed and were baptized.
9 Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
Then the Lord said to Paul, through a vision in the night: “Do not be afraid. Instead, speak out and do not be silent.
10 Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
For I am with you. And no one will take hold of you, so as to do you harm. For many of the people in this city are with me.”
11 Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
Then he settled there for a year and six months, teaching the Word of God among them.
12 Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
But when Gallio was proconsul of Achaia, the Jews rose up with one accord against Paul. And they brought him to the tribunal,
13 Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
saying, “He persuades men to worship God contrary to the law.”
14 A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
Then, when Paul was beginning to open his mouth, Gallio said to the Jews: “If this were some matter of injustice, or a wicked deed, O noble Jews, I would support you, as is proper.
15 Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
Yet if truly these are questions about a word and names and your law, you should see to it yourselves. I will not be the judge of such things.”
16 Saboda haka ya kore su.
And he ordered them from the tribunal.
17 Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
But they, apprehending Sosthenes, a leader of the synagogue, beat him in front of the tribunal. And Gallio showed no concern for these things.
18 Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
Yet truly, Paul, after he had remained for many more days, having said goodbye to the brothers, sailed into Syria, and with him were Priscilla and Aquila. Now he had shaved his head in Cenchreae, for he had made a vow.
19 Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
And he arrived at Ephesus, and he left them behind there. Yet truly, he himself, entering into the synagogue, was disputing with the Jews.
20 Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
Then, although they were asking him to remain for a longer time, he would not agree.
21 Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
Instead, saying goodbye and telling them, “I will return to you again, God willing,” he set out from Ephesus.
22 Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
And after going down to Caesarea, he went up to Jerusalem, and he greeted the Church there, and then he descended to Antioch.
23 Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
And having spent some length of time there, he set out, and he walked in order through the region of Galatia and Phrygia, strengthening all the disciples.
24 Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
Now a certain Jew named Apollo, born at Alexandria, an eloquent man who was powerful with the Scriptures, arrived at Ephesus.
25 An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
He was learned in the Way of the Lord. And being fervent in spirit, he was speaking and teaching the things that are of Jesus, but knowing only the baptism of John.
26 Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
And so, he began to act faithfully in the synagogue. And when Priscilla and Aquila had heard him, they took him aside and expounded the Way of the Lord to him more thoroughly.
27 Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
Then, since he wanted to go to Achaia, the brothers wrote an exhortation to the disciples, so that they might accept him. And when he had arrived, he held many discussions with those who had believed.
28 Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.
For he was vehemently and publicly reproving the Jews, by revealing through the Scriptures that Jesus is the Christ.