< Ayyukan Manzanni 18 >

1 Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
After these things, Paul departed from Athens, and came to Corinth;
2 A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
and finding a certain Jew named Aquila, born in Pontus, who had lately come from Italy, with Priscilla his wife, because Claudius had commanded all Jews to depart from Rome, he went to them;
3 da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
and because he was of the same trade, he made his home with them, and worked: for by trade they were tent-makers.
4 Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
But on every sabbath, he reasoned in the synagogue, and persuaded the Jews and the Greeks.
5 Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
And when Silas and Timothy came from Macedonia, Paul was roused in spirit, and earnestly testified to the Jews, that the Christ was Jesus.
6 Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
But when they set themselves in opposition, and reviled, he shook his clothing, and said to them: Your blood be upon your own head; I am clean. Henceforth I will go to the Gentiles.
7 Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
And he departed thence, and went into the house of a certain man named Justus, who worshiped God, and whose house joined the synagogue.
8 Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
But Crispus, the ruler of the synagogue, believed on the Lord, with all his house; and many of the Corinthians hearing, believed, and were immersed.
9 Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
And the Lord spoke to Paul by a vision in the night: Fear not; but speak, and be not silent;
10 Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
for I am with you, and no one shall make an assault upon you, to injure you; for I have many people in this city.
11 Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
And he remained there a year and six months, teaching the word of God among them
12 Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
But while Gallio was proconsul of Achaia, the Jews, with one mind, suddenly came upon Paul, and brought him to the judgment-seat,
13 Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
saying: This man persuades men to worship God contrary to the law.
14 A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
But when Paul was about to open his mouth, Gallio said to the Jews: If it were a matter of injustice, or of wicked mischief, O Jews, I would, with reason, bear with you:
15 Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
but if it is a question about a word, and names, and your law, see to it yourselves: for I will not be a judge of these tilings.
16 Saboda haka ya kore su.
And he drove them from the judgment-seat.
17 Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
And all the Greeks took Sosthenes, the ruler of the synagogue, and beat him before the judgment-seat. And Gallio cared for none of these things.
18 Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
And Paul, having remained many days longer, took leave of the brethren, and sailed to Syria, and with him Priscilla and Aquila, having shorn his head in Cenchrea; for he had a vow.
19 Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
And he came to Ephesus, and left them there; but he himself went into the synagogue, and reasoned with the Jews.
20 Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
And though they besought him to remain with them a longer time, he did not consent,
21 Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
but took leave of them, saying: I must, by all means, keep this coming feast in Jerusalem: but I will return to you, if God be willing. And he sailed from Ephesus,
22 Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
and having landed at Cæsarea, and gone up and saluted the church, he went down to Antioch.
23 Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
And having spent some time there, he departed, and went through the region of Galatia and Phrygia in order, strengthening all the disciples.
24 Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
And a certain Jew, named Apollos, an Alexandrian by birth, an eloquent man, and mighty in the Scriptures, came to Ephesus.
25 An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
He was instructed in the way of the Lord; and, being fervent in spirit, he spoke and taught accurately the things of the Lord, knowing only the immersion of John.
26 Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
And he began to speak boldly in the synagogue. But when Aquila and Priscilla heard him, they took him, and taught him the way of God more accurately.
27 Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
And when he wished to pass into Achaia, the brethren, exhorting him, wrote to the disciples to receive him. And when he had come, he gave much help to the believers, through the grace conferred on him.
28 Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.
For, with great strength, he utterly confounded the Jews publicly, showing, by the Scriptures, that the Christ was Jesus.

< Ayyukan Manzanni 18 >