< Ayyukan Manzanni 18 >
1 Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
And after these things Paul having separated from Athens, he came to Corinth.
2 A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
And having found a certain Jew named Aquila, a man of Pontus by origin, who recently came from Italy, and his wife Priscilla, because Claudius arranged for all the Jews to separate from Rome, he came to them.
3 da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
And because he was of the same craft, he abode with them, and was working, for they were of the tentmakers craft.
4 Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
And he was discoursing in the synagogue every sabbath, and was persuading Jews and Greeks.
5 Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
And when both Silas and Timothy came down from Macedonia, Paul was being held by the Spirit, fully testifying to the Jews, Jesus the Christ.
6 Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
But when they opposed and slandered him, having shaken out his clothes, he said to them, Your blood is upon your heads. I am clean. From henceforth I will go to the Gentiles.
7 Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
And having departed from there, he went into the house of a certain man named Justus, who worships God, whose house was adjoining the synagogue.
8 Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
And Crispus, the synagogue ruler, believed in the Lord with his whole household, and many of the Corinthians who heard believed, and were immersed.
9 Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
And the Lord spoke to Paul by a vision at night, Fear not, but speak, and be not silent,
10 Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
because I am with thee, and no man will lay upon thee to harm thee, because many people are for me in this city.
11 Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
And he remained a year and six months, teaching the word of God among them.
12 Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
But Gallio being proconsul of Achaia, the Jews with one accord attacked Paul and brought him to the judgment seat,
13 Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
saying, This man is persuading men to worship God against the law.
14 A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
But when Paul was going to open his mouth, Gallio said to the Jews, If therefore indeed it were some crime or evil reckless deed, O ye Jews, I would have tolerated you according to the matter.
15 Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
But if it is an issue about a word and names and the law from you, look ye yourselves, for I do not intend to be a judge of these things.
16 Saboda haka ya kore su.
And he drove them from the judgment seat.
17 Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
But all the Greeks, having taken Sosthenes the synagogue ruler, were beating him in front of the judgment seat. And Gallio was not going to judge, even of these things.
18 Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
But Paul, who still remained considerable days with the brothers, having separated, sailed away to Syria (and with him Priscilla and Aquila), having shaved his head in Cenchrea, for he had a vow.
19 Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
And he came to Ephesus and left behind those there, but having entered into the synagogue himself, he discoursed with the Jews.
20 Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
And when they asked him to remain on more time with them, he did not consent,
21 Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
but separated from them, having said, I must definitely keep the coming feast at Jerusalem, but I will return again to you, God willing. And he launched from Ephesus.
22 Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
And after coming down to Caesarea, having gone up and greeted the church, he went down to Antioch.
23 Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
And after spending some time, he departed, passing through the region of Galatia and Phrygia, successively, strengthening all the disciples.
24 Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
Now a certain Jew named Apollos, an Alexandrian by origin, an eloquent man, came to Ephesus, being mighty in the scriptures.
25 An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
This was a man who was instructed in the way of the Lord. And being fervent in the Spirit, he was speaking and teaching accurately the things about the Lord, knowing only the immersion of John.
26 Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
And this man began to speak boldly in the synagogue, but when Aquila and Priscilla heard him, they took him aside, and expounded to him the way of God more accurately.
27 Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
And when he intended to pass through into Achaia, the brothers wrote, having encouraged the disciples to receive him, who, when he arrived, assisted much those who believed through the grace.
28 Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.
For he forcibly refuted the Jews in public, demonstrating by the scriptures Jesus to be the Christ.