< Ayyukan Manzanni 18 >

1 Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint.
ᎾᏍᎩᏃ ᏄᎵᏍᏔᏂᏙᎸ ᏉᎳ ᎡᏗᏂᏱ ᎤᏓᏅᏒᎩ ᎪᎵᏂᏗᏱ ᏭᎷᏨᎩ.
2 A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su,
ᎤᏩᏛᎲᏃ ᎩᎶ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᏧᏏ ᎡᏈᎳ ᏧᏙᎢᏛ, ᏋᏗᏱ ᎤᏕᏅᎯ, ᎩᎳᎢ ᎤᎷᏦᏅᎯ ᎢᏓᎵ ᏅᏓᏳᎶᏒᎯ, ᎠᎴ ᎾᏍᏉ ᎤᏓᎵᎢ ᏈᏏᎳ ᏧᏙᎢᏛ, ᏅᏓᎦᎵᏍᏙᏗᏍᎬ ᏠᏗᏯ ᎤᏁᏨ ᏂᎦᏛ ᎠᏂᏧᏏ ᎶᎻ ᎤᎾᏓᏅᏍᏗᏱ, ᎾᏍᎩ ᏚᏩᏛᎯᎸᎩ.
3 da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su.
ᎤᏠᏱᏃ ᏧᎸᏫᏍᏓᏁᎯ ᎨᏒᎢ, ᎾᏍᎩ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᏂᏁᎸ ᎤᏪᏅᎩ, ᎠᎴ ᏚᎸᏫᏍᏓᏁᎸᎩ; ᏚᏂᎸᏫᏍᏓᏁᎲᏰᏃ ᏗᎦᎵᏦᏙᏗ ᏗᏃᏢᏍᎩ ᎨᏒᎢ.
4 Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.
ᏄᎾᏙᏓᏈᏒᏃ ᎠᏂᏧᏏ ᏧᏂᎳᏫᎢᏍᏗᏱ ᎦᏬᏂᏍᎬᎩ, ᎠᎴ ᏓᏍᏗᏰᏗᏍᎬᎩ ᎠᏂᏧᏏ ᎠᎴ ᎠᏂᎪᎢ.
5 Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi.
ᎿᎭᏉᏃ ᏌᏱᎳ ᎠᎴ ᏗᎹᏗ ᎤᏂᎷᏨ, ᎹᏏᏙᏂ ᏧᏂᎶᏒ, ᏉᎳ ᎤᏓᏅᏛ ᎤᏱᎸᏒᎩ, ᎠᎴ ᎾᏍᎩ ᎬᏂᎨᏒ ᏂᏚᏩᏁᎸᎩ ᎠᏂᏧᏏ ᏥᏌ ᎾᏍᎩ ᎦᎶᏁᏛ ᎨᏒᎢ.
6 Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”
ᎾᏍᎩᏃ ᎤᏂᏲᏍᏙᏔᏅ ᎠᎴ ᎤᏂᏐᏢᎢᏍᏔᏅ, ᎤᏄᏬ ᎤᏩᏣᎬᏅᎩ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎸᎩ; ᎢᏥᎩᎬ ᏗᏥᏍᎪᎵ ᎢᏨᏒ ᏕᏣᏓᏅᎵᏰᎡᏍᏗ, ᎠᏴ ᎥᏝ ᏯᏆᏓᏅᎵᏰᎥ; ᎿᎭᏉ ᎪᎯ ᎢᏳᏓᎴᏅᏛ ᏧᎾᏓᎴᏅᏛ ᏴᏫ ᏗᏁᎲ ᏮᏓᏥᎶᏏ.
7 Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada.
ᎾᎿᎭᏃ ᎤᏂᎩᏒ, ᏭᏴᎸᎩ ᎩᎶ ᎢᏳᏍᏗ ᎦᏁᎸ ᏣᏍᏓ ᏧᏙᎢᏛ, ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎠᏓᏙᎵᏍᏓᏁᎯ, ᎾᏍᎩ ᎦᏁᎸ ᏚᏓᏯᎸᎩ ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ.
8 Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.
ᏟᏍᏆᏃ ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ ᏄᎬᏫᏳᏒ ᎠᏥᎦᏘᏗᏍᏗ ᎤᏬᎯᏳᏅᎩ ᎤᎬᏫᏳᎯ, ᎠᎴ ᏂᎦᏛ ᏚᏓᏘᎾᎥᎢ, ᎤᏂᏣᏘᏃ ᎪᎵᏂᏗᏱ ᎠᏁᎯ ᎤᎾᏛᎦᏅ ᎤᏃᎯᏳᏅᎩ; ᎠᎴ ᏕᎨᎦᏬᎥᎩ.
9 Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru.
ᎤᎬᏫᏳᎯᏃ ᎯᎠ ᏄᏪᏎᎴ ᏉᎳ ᏒᏃᏱ ᎤᏁᎳᏫᏎᎲᎢ; ᏞᏍᏗ ᏱᏍᎦᎢᎮᏍᏗ, ᎯᏂᎨᏍᏗᏉᏍᎩᏂ ᎠᎴ ᏞᏍᏗ ᎡᎳᏪ ᏨᏅᎩ,
10 Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.”
ᎠᏴᏰᏃ ᏕᎬᎦᎿᎭᏩᏗᏙᎭ, ᎠᎴ ᎥᏝ ᎩᎶ ᏱᏙᎨᏣᏘᎷᎦ ᎤᏐᏅ ᎪᎱᏍᏗ ᏨᏁᏗᏱ, ᎤᏂᏣᏔᏰᏃ ᏴᏫ ᎠᏂ ᎦᏚᎲ ᏓᎩᎧᎭ.
11 Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.
ᎾᎿᎭᏃ ᏑᏕᏘᏴᏛ ᏑᏓᎵᏃ ᎢᏯᏅᏙ ᎤᏪᏙᎸᎩ, ᏓᏕᏲᎲᏍᎬᎩ ᎧᏃᎮᏛ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏤᎵᎦ ᎾᎿᎭᎠᏁᎲᎢ.
12 Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu.
ᎨᎵᏲᏃ ᏂᎯᏳ ᎡᎧᏯ ᎠᏥᎦᏘᏗᏍᏛᎢ, ᎠᏂᏧᏏ ᏌᏉ ᎢᎦᎦᏛ ᎬᏩᏁᎷᎩᎡᎸᎩ ᏉᎳ, ᎠᎴ ᎬᏩᏘᏃᎸ ᏗᎫᎪᏙᏗᏱ ᎦᏍᎩᎸᎢ,
13 Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”
ᎯᎠ ᏄᏂᏪᏒᎩ; ᎯᎠ ᎾᏍᎩ ᏓᏍᏗᏰᏗᎭ ᏴᏫ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎠᎾᏓᏙᎵᏍᏓᏁᎲ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᎤᏂᏲᏍᏙᏗᏱ.
14 A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku.
ᎿᎭᏉᏃ ᏉᎳ ᏛᏍᏚᎢᏏᏒᎩ ᎠᎰᎵ, ᎨᎵᏲ ᎯᎠ ᏂᏚᏪᏎᎸᎩ ᎠᏂᏧᏏ; ᎢᏳᏃ ᎤᏲ ᎢᏳᏛᏁᎸᎯ ᏱᎩ, ᎠᎴ ᎤᏍᎦᏅᏨᎯ ᏱᎩ, ᎢᏥᏧᏏ, ᏚᏳᎪᏛ ᏱᎩ ᎢᏨᏯᏛᏓᏍᏓᏁᏗᏱ.
15 Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.”
ᎢᏳᏍᎩᏂ ᎧᏁᏨᎯ ᎠᎴ ᎪᎱᏍᏗ ᏚᏙᎥ ᎠᎴ ᏗᎧᎿᎭᏩᏛᏍᏗ ᎢᏣᏤᎵᎦ ᎧᏃᎮᏗ ᏱᎩ, ᎢᏨᏒ ᏗᏥᎸᏫᏍᏓᏏ, ᎥᏝᏰᏃ ᎾᏍᎩ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᏴ ᏱᏙᎦᎫᎪᏓ.
16 Saboda haka ya kore su.
ᏚᎨᎯᏙᎸᎩᏃ ᏗᎫᎪᏙᏗᏱ ᎦᏍᎩᎸᎢ.
17 Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.
ᎿᎭᏉᏃ ᏂᎦᏛ ᎠᏂᎪᎢ ᎤᏂᏂᏴᎲ ᏐᏍᏗᏂ ᎠᏂᏧᏏ ᏧᏂᎳᏫᎢᏍᏗᏱ ᏄᎬᏫᏳᏒ ᎠᏥᎦᏘᏗᏍᏗ, ᎤᏂᎵᎥᏂᎸᎩ ᎢᎬᏱᏢ ᏗᎫᎪᏙᏗᏱ ᎦᏍᎩᎸᎢ. ᎨᎵᏲᏃ ᎥᏝ ᏳᎦᏌᏯᏍᏔᏁ ᎾᏍᎩ ᏄᏍᏗᏕᎬᎢ.
18 Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi.
ᏉᎳᏃ ᎠᏏ ᎤᏬᎯᏨᎩ ᎤᏪᏙᎸᎩ; ᎿᎭᏉᏃ ᏚᏲᎵᎸ ᎠᎾᏓᏅᏟ, ᏥᏳᎯ ᏭᏣᏅᎩ ᏏᎵᏱ ᏭᎶᏒᎩ; ᎠᎴ ᎾᏍᏉ ᏈᏏᎳ ᎠᎴ ᎡᏈᎳ ᎬᏩᏍᏓᏩᏛᏒᎩ, ᎤᎵᏍᏙᏰᎲᎯ ᎨᏒᎩ ᏒᏟᏯ ᎢᏴᏛ, ᎤᏁᎳᏅᎯᏰᏃ ᎤᏚᎢᏍᏓᏁᎸᎯ ᎨᏒᎩ.
19 Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa.
ᎡᏈᏌᏃ ᏭᎷᏨᎩ ᎠᎴ ᎾᎿᎭᏚᏩᏕᎲᎩ, ᎤᏩᏒᏍᎩᏂ ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ ᏭᏴᎸᎩ ᎠᎴ ᏚᏬᏁᏔᏅᎩ ᎠᏂᏧᏏ.
20 Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara’yan kwanaki da su, bai yarda ba.
ᎬᏩᏔᏲᏎᎸᏃ ᎤᏬᎯᎢᏍᏗᏱ ᏧᏪᎳᏗᏓᏍᏗᏱ ᎥᏝ ᏳᏬᎯᏳᏁᎢ;
21 Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa.
ᏚᏲᎵᎸᏉᏍᎩᏂ ᎯᎠ ᏄᏪᏒᎩ; ᎠᏎ ᎠᎩᏍᏆᏂᎪᏙᏗ ᏥᎷᏏᎵᎻ ᎯᎠ ᏗᎵᏍᏓᏴᏗᏱ ᏨᏛᏍᏆᎸᎯ. ᎠᏎᏃ ᏔᎵᏁ ᏛᏨᏩᏛᎯᎵ, ᎢᏳᏃ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏏᏳ ᏳᏰᎸᏅ. ᎡᏈᏌᏃ ᏥᏳᎯ ᏭᏣᏅᎩ.
22 Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.
ᏏᏌᎵᏱᏃ ᎤᏚᎩᏒ, ᎠᎴ ᏧᎾᏁᎶᏗ ᎤᎾᏓᏡᎬ ᏫᏚᏲᎵᎸ, ᎥᏘᎣᎩ ᏭᎶᏒᎩ.
23 Bayan ya yi’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.
ᏰᎵᏃ ᎤᏬᎯᏨ ᎤᏪᏙᎸ, ᎤᏂᎩᏒᎩ, ᎠᎴ ᎨᎴᏏᏱ ᎠᎴ ᏈᏥᏱ ᎣᏍᏛ ᎤᏱᎸᏒᎩ ᎤᏪᏐᎸᎩ, ᏓᎵᏂᎪᎯᏍᏗᏍᎬᎩ ᏂᎦᏛ ᎠᏃᎯᏳᎲᏍᎩ
24 Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi.
ᎩᎶᏃ ᎢᏳᏍᏗ ᎠᏧᏏ ᎠᏉᎳ ᏧᏙᎢᏛ, ᎡᎵᎩᏱ ᎤᏛᏒᎯ, ᎠᏏᎾᏍᏛ ᎤᏬᏂᎯᏍᏗᏱ, ᎠᎴ ᏗᎦᎸᏉᏗ ᎪᏪᎵ ᏗᏏᎾᏍᏛ, ᎡᏈᏌ ᎤᎷᏨᎩ.
25 An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani.
ᎾᏍᎩ ᎯᎠ ᎠᎨᏲᏅᎯ ᎨᏒᎩ ᎤᎬᏫᏳᎯ ᎤᏅᏅᎢ, ᎠᎴ ᎤᎵᏂᎩᏛ ᎨᏒ ᎤᏓᏅᏛᎢ, ᎧᏃᎮᏍᎬᎩ ᎠᎴ ᏓᏕᏲᎲᏍᎬᎩ ᎾᏑᎵᎪᎬᎾ ᎤᎬᏫᏳᎯ ᎤᏤᎵ ᎤᎬᏩᎵ ᎨᏒᎢ, ᏣᏂ ᎤᏤᎵ ᏗᏓᏬᏍᏗ ᎤᏩᏒ ᎠᎦᏔᎲᎩ.
26 Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.
ᎾᏍᎩ ᎤᎴᏅᎲᎩ ᎾᏍᎦᎢᎲᎾ ᎤᏬᏂᏒᎩ ᏗᎦᎳᏫᎢᏍᏗᏱ. ᎾᏍᎩᏃ ᎡᏈᎳ ᎠᎴ ᏈᏏᎳ ᎤᎾᏛᎦᏁᎸ ᎤᏂᏯᏅᎲᎩ, ᎠᎴ ᎤᏟ ᎢᏲᏍᏛ ᏚᏃᏏᏌᏁᎸᎩ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏤᎵ ᎦᏅᏅᎢ.
27 Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata.
ᎤᏚᎸᎲᏃ ᎡᎧᏯ ᎤᏪᏅᏍᏗᏱ, ᎠᎾᏓᏅᏟ ᎤᏃᏪᎳᏅᎩ ᏗᏂᏔᏲᏎᎸᎩ ᎠᏃᎯᏳᎲᏍᎩ ᏗᎬᏩᏓᏂᎸᎢᏍᏗᏱ; ᎾᏍᎩᏃ ᏭᎷᏨ, ᎤᏣᏘ ᏚᏍᏕᎸᎲᎩ ᎤᏁᎳᏅᎯ ᎤᏓᏙᎵᏣᏛ ᎢᏳᏩᏂᏌᏛ ᎤᏃᎯᏳᏅᎯ.
28 Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.
ᎤᎵᏂᎩᏛᏯᏰᏃ ᎦᏬᏂᏍᎬ ᎬᏗᏍᎬ ᎤᏃᎯᏳᏗᏱ ᏄᏩᏁᎸᎩ ᎠᏂᏧᏏ ᏕᎦᎳᏫᎥᎢ, ᏗᎦᎸᏉᏗ ᎪᏪᎵ ᏕᎬᏗᏍᎬᎢ ᎬᏂᎨᏒ ᏂᎬᏁᎲ ᏥᏌ ᎾᏍᎩ ᎦᎶᏁᏛ ᎨᏒᎢ.

< Ayyukan Manzanni 18 >