< Ayyukan Manzanni 17 >

1 Da suka bi ta Amfifolis da Afolloniya, sai suka isa Tessalonika, inda akwai majami’ar Yahudawa.
And, travelling through Amphipolis and Apollonia, they came to Thessalonica, where was a synagogue of the Jews;
2 Kamar yadda ya saba, Bulus ya shiga majami’ar, ranakun Asabbaci uku ya yi ta yin muhawwara da su daga cikin Nassosi,
and, according to Paul’s custom, he went in unto them, and, for three sabbaths, reasoned with them from the Scriptures, —
3 yana musu bayani da tabbatarwa cewa dole Kiristi ya sha wahala ya kuma tashi daga matattu. Ya kuma ce, “Wannan Yesu da nake sanar muku shi ne Kiristi.”
opening up, and setting forth, that it was needful for, the Christ, to suffer, and to arise from among the dead; and [saying], This, is the Christ, —Jesus, whom, I, am declaring unto you.
4 Waɗansu Yahudawa suka amince suka kuma bi Bulus da Sila, haka ma Hellenawa da yawa masu tsoron Allah da kuma manyan mata ba kaɗan ba.
And, some from among them, were persuaded, and cast in their lot with Paul and Silas; also, of the devout Greeks, a great throng, and, of the chief women, not a few.
5 Amma Yahudawa suka yi kishi; saboda haka suka tattara’yan iska daga kasuwa, suka shirya wata ƙungiya, suka tā da tarzoma a birni. Suka ruga zuwa gidan Yason suna neman Bulus da Sila don su kawo su a gaban taron.
But the Jews, being, jealous, and taking unto themselves certain wicked men, of the rabble, and making a riot, were setting the city in an uproar; and, besieging the house of Jason, were seeking to lead them forth unto the populace, —
6 Amma da ba su same su ba, sai suka ja Yason da waɗansu’yan’uwa zuwa gaban mahukuntan birnin, suna ihu suna cewa, “Waɗannan mutanen da suke tā da fitina ko’ina a duniya sun iso nan,
and, not finding them, they began dragging Jason and certain brethren unto the city-rulers, shouting—They who have thrown the inhabited earth into confusion, the same, hither also, are come, —
7 Yason kuwa ya karɓe su a gidansa. Dukansu suna karya dokokin Kaisar, suna cewa akwai wani sarki, wanda ake kira Yesu.”
unto whom Jason hath given welcome; and, these all, contrary to the decrees of Caesar, are acting, —saying that there is another king, Jesus.
8 Da suka ji haka, sai hankalin taron da na mahukuntan birnin ya tashi.
And they troubled the multitude and the city-rulers, when they heard these things;
9 Sai suka sa Yason da sauran su biya kuɗin saki sa’an nan suka sallame su.
and, taking security from Jason and the rest, they let them go.
10 Da dare ya yi, sai’yan’uwa suka sallami Bulus da Sila su tafi Bereya. Da suka isa can, sai suka shiga majami’ar Yahudawa.
But, the brethren, straightway, during the night, sent away both Paul and Silas unto Beroea, who, indeed, arriving, unto the synagogue of the Jews, went off;
11 Bereyawa kuwa sun fi Tessalonikawa hankali, gama sun karɓi saƙon da marmari ƙwarai, suka kuma yi ta yin bincike Nassosi kowace rana su ga ko abin da Bulus ya faɗa gaskiya ne.
and, these, were more noble than those in Thessalonica, in that they welcomed the word with all readiness of mind, daily, searching the Scriptures, —whether these things could be so.
12 Yahudawa da yawa suka gaskata, haka ma waɗansu manyan matan Hellenawa da kuma mazan Hellenawa da yawa.
Many, therefore, from among them, believed, and, of the Grecian women of the higher class, and of men, not a few.
13 Da Yahudawan da suke a Tessalonika suka ji cewa Bulus yana wa’azin maganar Allah a Bereya, sai suka je can ma, suna zuga taro suna kuma tā da hankalinsu.
But, when the Jews from Thessalonica came to know that, in Beroea also, had the word of God been declared by Paul, they came thither also, stirring up and troubling the multitudes.
14 Nan da nan’yan’uwa suka sa Bulus yă tafi bakin teku, amma Sila da Timoti suka dakata a Bereya.
Howbeit, then, immediately, the brethren sent away, Paul, to be journeying as far as unto the sea; and both Silas and Timothy stayed behind, there.
15 Mutanen da suka raka Bulus kuwa suka kawo shi Atens sa’an nan suka dawo da umarnai wa Sila da Timoti cewa su zo wurinsa da gaggawa.
But, they who were conducting Paul, brought him as far as Athens, and, receiving a commandment unto Silas and Timothy, that with, all possible speed, they would come unto him, they departed.
16 Yayinda Bulus yake jiransu a Atens, ya damu ƙwarai da ya ga birnin cike da gumaka.
But, while, in Athens, Paul was expecting them, his spirit within him was being urged on, seeing how the city was given to idols.
17 Saboda haka ya yi ta muhawwara a majami’a da Yahudawa da kuma Hellenawa masu tsoron Allah, haka kuma da waɗanda yake tararwa a bakin kasuwa.
So then, he began reasoning in the synagogue with the Jews, and with them who worshipped; and, in the market-place, every day, with them who happened to be at hand.
18 Wata ƙungiyar Afikuriya da kuma masu bin ussan ilimin Sitoyik suka fara gardama da shi. Waɗansunsu suka ce, “Mene ne mai surutun nan yake ƙoƙarin faɗi?” Waɗansu suka ce, “Kamar yana wa’azin baƙin alloli ne.” Sun faɗa haka ne domin Bulus yana wa’azin labari mai daɗi game da Yesu da kuma tashin matattu.
But, certain both of the Epicurean and of the Stoic philosophers, were encountering him; and some were saying—What might this picker-up-of-scraps wish to be saying? And, others—Of foreign demons, he seemeth to be a declarer: because, of Jesus and the Resurrection, he was announcing the joyful tidings.
19 Sai suka ɗauke shi suka kawo shi wurin taron Areyofagus, inda suka ce masa, “Ko za mu san mene ne sabon koyarwan nan ya ƙunsa da kake yi?
And so, laying hold of him, they brought him up, to the Hill of Mars, saying—Can we get to know what this new teaching is, which, by thee, is being spoken.
20 Kana kawo mana ra’ayoyin da suke baƙo a gare mu, kuma muna so mu san mene ne suke nufi.”
For, certain foreign things, art thou bringing into our hearing: We are minded to get to know, therefore, what these things please to be!
21 (Duk Atenawa da baƙin da suke zama a can suna zaman kashe wando ne kawai kuma ba abin da suke yi sai dai taɗi da kuma jin sababbin ra’ayoyi.)
Now, all Athenians and the sojourning foreigners, unto nothing else, were devoting their leisure, than to be telling or hearing, something newer.
22 Sai Bulus ya miƙe tsaye a tsakiyar taron Areyofagus ya ce, “Ya ku mutanen Atens! Na dai lura cewa ta kowace hanya ku masu addini ne ƙwarai.
And Paul taking his stand in the midst of the Hill of Mars, said—Ye men of Athens! In every way, how unusually reverent of the demons ye are, I perceive.
23 Gama sa’ad da nake zagawa, na lura da kyau da abubuwan da kuke bauta wa, har ma na tarar da wani bagade da wannan rubutu, Ga Allahn da ba a sani ba. To, abin nan da kuke yi wa sujada a matsayin abin da ba ku sani nan ba shi ne zan sanar da ku.
For, passing through, and carefully observing your objects of devotion, I found an altar also, in which was inscribed—Unto an Unknown God. What, therefore, not knowing, ye reverence, the same, do, I, declare unto you.
24 “Allahn da ya halicci duniya da kome da yake cikinta shi ne Ubangijin sama da ƙasa, ba ya kuma zama a haikalin da aka gina da hannuwa.
The God that made the world and all things that are therein, the same, being, Lord, of heaven and earth, not in hand-made shrines, doth dwell,
25 Ba a kuma yin masa hidima da hannun mutum, sai ka ce mai bukatan wani abu, domin shi kansa ne ke ba wa dukan mutane rai da numfashi da kuma kome.
nor, by human hands, is waited upon, as though in want of anything, himself, giving unto all life and breath and all things;
26 Daga mutum ɗaya, ya halicci kowace al’ummar mutane, don su zauna a duk duniya; shi ne kuma ya ƙaddara lokuta bisa ga tsarinsu da kuma inda za su kasance.
he made also, of one, every nation of men to dwell upon all the face of the earth, —marking out fitting opportunities, and the bounds of their dwelling place,
27 Allah ya yi wannan domin mutane su neme shi mai yiwuwa kuma su lalluba su same shi, ko da yake ba shi da nisa daga kowannenmu.
that they might be seeking God—if, after all, indeed, they might feel after him and find him, —although, in truth, he is already not far from any one of us.
28 ‘Gama a cikinsa ne muke rayuwa muke motsi muka kuma kasance.’ Yadda waɗansu mawaƙanku suka ce, ‘Mu zuriyarsa ce.’
For, in him, we live and move and are: as, even some of your own poets, have said—For, his offspring also, we are.
29 “Saboda haka da yake mu zuriyar Allah ce, kada mu yi tsammani cewa kamannin Allah yana kama da zinariya ko azurfa ko dutse, siffar da mutum ya ƙago ta wurin dabararsa.
Being, then, offspring, of God, we ought not to be supposing that, unto gold or silver or stone, graven by art and device of man, the Divine, is like.
30 A dā Allah ya kawar da Allah ya kawar da kai ga zamanin jahilci, amma yanzu ya umarci dukan mutane a ko’ina su tuba.
The times of ignorance, therefore, overlooking, God, as things now are, is charging all men everywhere to repent,
31 Gama ya sa ranar da zai yi wa duniya shari’a da adalci ta wurin mutumin da ya naɗa. Ya riga ya ba da tabbacin wannan ga dukan mutane ta wurin tā da shi daga matattu.”
inasmuch as he hath appointed a day, in which he is about to be judging the habitable earth in righteousness, by a man whom he hath pointed out, —offering faith unto all, by raising him from among the dead?
32 Sa’ad da suka ji maganar tashin matattu, waɗansunsu suka yi tsaki, amma waɗansu suka ce, “Muna so mu ƙara jin ka a kan wannan batu.”
Now, when they heard of raising the dead, some, indeed, began to mock, while, others, said—We will hear thee, concerning this, even again.
33 Da wannan, Bulus ya bar Majalisar.
Thus, Paul, came forth out of their midst.
34 Waɗansu mutane kima suka zama mabiyan Bulus suka kuwa gaskata. A cikinsu kuwa akwai Diyonasiyus ɗan Majalisar Areyofagus, haka kuma wata mace mai suna Damaris, da waɗansu dai haka.
But, certain persons, joining themselves unto him, believed; among whom were even Dionysius the Mars-hill judge, and a woman by name Damaris, and others with them.

< Ayyukan Manzanni 17 >