< Ayyukan Manzanni 16 >

1 Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
Paul [and Silas] to Derbe [city and visited the believers there]. Next [they went to] Lystra [city]. A believer whose name was Timothy lived there. His mother was a Jewish believer, but his father was a Greek.
2 ’Yan’uwa a Listira da Ikoniyum sun yi magana mai kyau ƙwarai a kansa.
The believers in Lystra and Iconium said good things about Timothy,
3 Bulus ya so ya ɗauke shi a tafiyar, saboda haka ya yi masa kaciya, domin Yahudawan da suke da zama a wurin, don duk sun san cewa mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
and Paul wanted to take Timothy with him [when he went] to other places, so he circumcised Timothy. [He did that so that] the Jews who lived in those places [would accept Timothy], because they knew that his non-Jewish father [had not allowed him to be circumcised] {[anyone to circumcise his son]}.
4 Yayinda suke tafiya daga gari zuwa gari, suka dinga ba da shawarwarin da manzanni da dattawa a Urushalima suka zartar domin mutane su kiyaye.
[So Timothy went with Paul and Silas] and they traveled to many other towns. [In each town] they told [the] believers the rules that had been decided by the apostles and elders in Jerusalem {that the apostles and elders in Jerusalem had decided} that [non-Jewish] believers should obey.
5 Saboda haka ikkilisiyoyi suka ginu cikin bangaskiya suka kuma yi girma suka yi ta ƙaruwa kowace rana.
[God was helping] the believers in those towns to trust more strongly [in the Lord Jesus], and every day more people became believers.
6 Bulus da abokan tafiyarsa suka zazzaga dukan yankin Firjiya da Galatiya, don Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin wa’azi a lardin Asiya.
Paul and his companions wanted/planned to enter Asia [province] preach the message [about Jesus] there, but they were prevented by the Holy Spirit {the Holy Spirit prevented them} [from going there. So] they traveled through Phrygia and Galatia [provinces].
7 Da suka isa kan iyakar Misiya, suka yi ƙoƙari su shiga Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yarda musu ba.
They arrived at the border of Mysia [province] and they wanted to go [north] Bithynia [province]. But [again] the Spirit of Jesus showed them that they should not [go there].
8 Saboda haka suka ratsa Misiya suka zo Toruwas.
So they went through Mysia [province] and arrived at Troas, a [port city. I, Luke, joined them there].
9 Da dare Bulus ya ga wahayin wani mutumin Makidoniya yana tsaye yana roƙonsa cewa, “Ka zo Makidoniya ka taimake mu.”
That night [God gave] Paul a vision in which he saw a man [who was a native] of Macedonia [province]. He was standing [some distance away], and he was earnestly calling to Paul, “[Please] come over [here] to Macedonia and help us!”
10 Bayan Bulus ya ga wahayin, muka shirya nan take mu tashi zuwa Makidoniya, mun tabbata cewa, Allah ya kira mu mu yi musu wa’azin bishara.
[The next morning] we [(exc)] immediately got ready to go to Macedonia, because we believed that God had called us to [go and] preach the good message to the people there.
11 Daga Toruwas muka tashi zuwa teku muka kuma shiga jirgin ruwa muka miƙe kai tsaye zuwa Samotiras, kashegari kuma muka nufi Neyafolis.
So we [(exc)] got on a ship in Troas and sailed across [the sea] Samothrace [Island. We spent the night there], and the next day [we sailed again across the sea and arrived] at Neapolis [port/town].
12 Daga can muka tafi Filibbi, wata babbar alkaryar Roma wadda kuma take babban birni a gundumar Makidoniya. Muka zauna a can kwanaki masu yawa.
Then we [left Neapolis and] went [by land] to Philippi. It was a very important city in Macedonia [province, where many] Roman citizens lived. We stayed in Philippi several days.
13 A Asabbaci, muka fita ƙofar birnin zuwa bakin kogi, inda muke tsammani za mu sami wurin yin addu’a. Muka zauna muka fara yin wa matan da suka taru a can magana.
On the first (Sabbath/Jewish day of rest) [after we(exc) arrived], we went outside the city gate [down] to the river. We had heard [someone say] that [Jewish] people gathered to pray there. [When we arrived there, we saw] some women who had gathered [to pray]. So we sat down and began to tell them [the message about Jesus].
14 Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.
A woman whose name was Lydia was one of those who were listening [to Paul. She was a non-Jewish woman], from Thyatira [city, who bought and] sold [expensive] purple cloth. She had accepted what the Jews believe about God. The Lord [God] caused her to pay attention to the message that Paul preached, and she believed it. [The members of her household also heard the good message and believed in Jesus] [MTY].
15 Da aka yi mata baftisma tare da iyalin gidanta, sai ta gayyace mu zuwa gidanta. Ta ce, “In kun amince ni mai bi ce cikin Ubangiji, sai ku zo ku sauka a gidana.” Sai ta kuwa rinjaye mu.
After [Paul and Silas] baptized Lydia and the others who lived in her house [MTY] {After Lydia and the others who lived in her house were baptized}, she invited us to [go and stay in] her home. She said, “You [(pl)] know that I [now] believe in the Lord [Jesus], so [please] come and stay in my house.” She persuaded us [to do that, so we(exc) stayed there].
16 Wata rana muna tafiya zuwa wurin yin addu’a, sai muka sadu da wata baranya mai ruhun aljani mai duba. Takan samo wa mutanenta kuɗi da yawa, duban da take yi.
Another day, while we [(exc)] were going to the place where people regularly gathered to pray, we met a young woman who was a slave. An evil spirit was enabling her to be a ventriloquist and to tell people what would happen [to them]. People paid a lot of money to [the men who were] her owners, in return for her telling them things that [she said] would happen [to them].
17 Wannan yarinya kuwa ta bi Bulus da kuma sauranmu, tana ihu tana cewa, “Waɗannan mutane bayin Allah Mafi Ɗaukaka ne, suna sanar da ku hanyar ceto.”
This young woman followed Paul and the rest of us. She continually shouted, “These men serve the God who is the greatest [of all gods]! They are telling you how ([God] can save you [so that he will not punish you/to be] saved)”
18 Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.
She continued to do that for many days. Finally Paul became irritated. So he turned [toward the young woman] and rebuked the evil spirit [that was in her. He said], “By the authority [MTY] of Jesus Christ, I command you [(sg)] to come out of this young woman!” Right away the evil spirit left her.
19 Da iyayengijin baranyar suka ga hanyar samun kuɗinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila suka ja su zuwa cikin kasuwa don su fuskanci hukuma.
And then her owners realized that she could no longer earn money for them [because she could no longer predict what would happen to people, so they were angry]. They grabbed Paul and Silas and forcefully took them to the public square, to [the place where] the government authorities and [a lot of other people were gathered].
20 Sai suka kawo su a gaban alƙalai suka ce, “Waɗannan Yahudawa ne, suna kuma birkitar mana da gari,
The owners [of the young woman] brought Paul and Silas to the city officials and told them, “These men are Jews, and they are greatly troubling [the people in] [MTY] our city.
21 ta wurin koyar da al’adun da ba daidai ba ne mu Romawa mu karɓa ko mu aikata.”
They are teaching that we [(inc)] should follow customs that our laws do not allow us Romans to consider [to be correct] or to obey!”
22 Sai taron suka fāɗa wa Bulus da Sila gaba ɗaya, alƙalan kuwa suka yi umarni a tuɓe su a kuma yi musu dūka.
Many of the crowd joined [those who were accusing] Paul and Silas, and started beating them. Then the [Roman] authorities commanded [soldiers] to tear the shirts off Paul and Silas and to beat them [with rods/sticks].
23 Bayan an yi musu bulala sosai, sai aka jefa su cikin kurkuku, aka umarci mai gadin kurkukun yă tsare su da kyau.
[So the soldiers] beat Paul and Silas vigorously [with rods]. After that, they [took them and] shoved them into the prison. They told the jailer that he should lock them up securely.
24 Da karɓan irin umarnan nan, sai ya sa su can cikin ɗakin kurkuku na ciki-ciki, kuma ya ɗaura ƙafafunsu a turu.
[Because the officials] had [commanded] him [to do that], the jailer shoved Paul and Silas into the cell that was farthest inside. [There, he made them sit down on the floor/ground and stretch out their legs]. Then he fastened their ankles in [grooves] between two large wooden beams, [so that Paul and Silas could not move their legs].
25 Wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu’a suna rera waƙoƙi ga Allah, sauran’yan kurkuku kuwa suna sauraronsu.
About midnight, Paul and Silas were praying [aloud] and praising God by singing hymns. The [other] prisoners were listening attentively to them.
26 Ba zato ba tsammani sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa har tushen ginin kurkukun ya jijjiga. Nan da nan sai duk ƙofofin kurkukun suka bubbuɗe, sarƙoƙin kowa kuma suka ɓaɓɓalle.
Suddenly there was a very strong earthquake. It shook the entire jail [SYN] and its foundation [SYN]. [The earthquake caused] all the doors [of the jail] to open suddenly, and [caused] all the chains that fastened the prisoners to fall off.
27 Mai gadin kurkukun ya farka daga barci, sa’ad da ya ga ƙofofin kurkukun a buɗe, sai ya zāre takobinsa yana shirin kashe kansa domin ya ɗauka’yan kurkukun sun gudu.
The jailer woke up and saw that the doors of the jail were open. He thought that the prisoners had escaped. So he pulled out his sword in order to kill himself, [because he knew that the officials would kill him if the prisoners escaped].
28 Amma Bulus ya yi ihu ya ce, “Kada ka yi wa kanka lahani! Dukanmu muna nan!”
Paul [saw the jailer and] shouted to him, “Do not harm yourself! We [(exc) prisoners] are all here!”
29 Mai gadin kurkukun ya kira a kawo fitilu, ya ruga ciki ya fāɗi yana rawan jiki a gaban Bulus da Sila.
The jailer shouted [to someone] to bring torches/lanterns, [and after they brought them], he rushed into the jail and knelt down in front of Paul and Silas. [He was very afraid, so] much so that he was trembling/shaking.
30 Sai ya fito da su waje ya kuma tambaye su ya ce, “Ranku yă daɗe, me zan yi domin in sami ceto?”
Then he brought Paul and Silas out [of the jail] and asked: “Sirs, what do I need to do to be saved [from being punished for my sins]?”
31 Suka amsa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”
[They answered], “Trust in [what] the Lord Jesus [has done for you], and you will be saved {[God] will save you}, and the others who live in [MTY] your house will [also] be saved [if they believe in Jesus].”
32 Sa’an nan suka yi masa maganar Ubangiji shi da kuma dukan sauran da suke a gidansa.
Then the jailer took Paul and Silas into his house, washed their wounds, and gave them a meal. [He woke up all the people in his house, and] Paul and Silas told all of them the message about the Lord [Jesus. They all believed in him]. Immediately [after that, the jailer and all his family were baptized] {[Paul and Silas] baptized the jailer and all his family}. They were very happy, because now they all believed in God.
33 A wannan sa’a na daren, mai gadin kurkukun ya ɗauke su ya wanke musu raunukansu; nan take aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.
34 Sai mai gadin kurkukun ya kawo su cikin gidansa ya ba su abinci; ya kuwa cika da murna don yă gaskata da Allah, shi da dukan iyalinsa.
35 Da gari ya waye, sai alƙalan suka aika ma’aikatansu wajen mai gadin kurkukun da umarni cewa, “Ka saki mutanen nan.”
The next morning, the [Roman] officials commanded [some] police officers [to go to the jail to say to the jailer], “[Our bosses] say, ‘Let those [two] prisoners go [now]!’”
36 Sai mai gadin kurkukun ya gaya wa Bulus cewa, “Alƙalai sun ba da umarni a sake ku kai da Sila. Yanzu sai ku tafi. Ku sauka lafiya.”
[After the officers went and told that to] the jailer, he [went and] told Paul, “The [Roman] authorities have sent a message [(sg)] saying that I should release you [(sg)] and Silas [from prison]. So you [two] can leave [the jail] now. Now you can go peacefully!”
37 Amma Bulus ya ce wa ma’aikatan, “Sun yi mana dūka a fili ba tare da shari’a ba, ko da yake mu’yan ƙasar Roma ne, suka kuma jefa mu cikin kurkuku. Yanzu suna so su fitar da mu a ɓoye? A’a! Sai dai su zo da kansu su rako mu waje.”
But Paul said to the police officers, “The authorities [commanded men to] beat us in front of a crowd before [those authorities] had learned if we [(exc)] had done anything wrong! Then they [ordered men to] shove us into jail! [But that was not legal, because] we [(exc)] are Roman citizens! And now they want [RHQ] to send us away secretly! We will not accept that! Those [Roman] officials must come themselves and [tell us that they are sorry], and take us out [of jail].”
38 Sai ma’aikatan suka faɗa wa alƙalan wannan, da suka ji cewa Bulus da Sila Romawa ne, sai suka ji tsoro.
So the police officers [went and] told the city authorities [what Paul had said]. When those authorities heard that Paul and Silas were Roman citizens, they were afraid [that someone would report to more important officials what they had done, and as a result they would be punished] {[those officials would punish them]}.
39 Sai suka zo don su roƙe su, suka yi musu rakiya daga kurkukun, suna roƙonsu su bar birnin.
So the city authorities came to Paul and Silas and told them that they were sorry for what they had done to them. The authorities brought them out of the jail, and repeatedly asked them to leave the city [soon].
40 Bayan Bulus da Sila suka fita daga kurkukun, sai suka tafi gidan Lidiya, inda suka sadu da’yan’uwa suka kuma ƙarfafa su. Sa’an nan suka tafi.
After Paul and Silas left the jail, they went to Lydia’s house. There they met with her and the [other] believers. They encouraged the believers [to continue trusting in the Lord Jesus], and then the two apostles left [Philippi].

< Ayyukan Manzanni 16 >