< Ayyukan Manzanni 16 >

1 Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
and came to Derbe and Lystra; and, behold, a certain disciple was there, whose name was Timothy, the son of a believing Jewess, but of a Grecian father;
2 ’Yan’uwa a Listira da Ikoniyum sun yi magana mai kyau ƙwarai a kansa.
who had an honorable character given by the brethren in Lystra and Iconium.
3 Bulus ya so ya ɗauke shi a tafiyar, saboda haka ya yi masa kaciya, domin Yahudawan da suke da zama a wurin, don duk sun san cewa mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
Him Paul would have to go forth with him: and took and circumcised him, on account of the Jews who were in those places: for they all knew his father, that he was a Greek.
4 Yayinda suke tafiya daga gari zuwa gari, suka dinga ba da shawarwarin da manzanni da dattawa a Urushalima suka zartar domin mutane su kiyaye.
And as they passed through the cities, they delivered to their custody the decrees, which were determined by the Apostles and elders that were at Jerusalem.
5 Saboda haka ikkilisiyoyi suka ginu cikin bangaskiya suka kuma yi girma suka yi ta ƙaruwa kowace rana.
The congregations, therefore, were confirmed in the faith, and increased in number daily.
6 Bulus da abokan tafiyarsa suka zazzaga dukan yankin Firjiya da Galatiya, don Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin wa’azi a lardin Asiya.
And they went through Phrygia, and the region of Galatia, and being forbidden by the Holy Spirit to speak the word in Asia;
7 Da suka isa kan iyakar Misiya, suka yi ƙoƙari su shiga Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yarda musu ba.
when they were come to Mysia, they attempted to go to Bithynia; but the spirit did not permit them.
8 Saboda haka suka ratsa Misiya suka zo Toruwas.
And passing by Mysia, they went down to Troas.
9 Da dare Bulus ya ga wahayin wani mutumin Makidoniya yana tsaye yana roƙonsa cewa, “Ka zo Makidoniya ka taimake mu.”
And a vision appeared to Paul in the night: There stood a certain Macedonia, entreating him, and saying, Come over to Macedonia, and help us.
10 Bayan Bulus ya ga wahayin, muka shirya nan take mu tashi zuwa Makidoniya, mun tabbata cewa, Allah ya kira mu mu yi musu wa’azin bishara.
And as soon as he had seen this vision, we immediately endeavored to go to Macedonia; assuredly inferring, that the Lord had called us to declare the gospel to them.
11 Daga Toruwas muka tashi zuwa teku muka kuma shiga jirgin ruwa muka miƙe kai tsaye zuwa Samotiras, kashegari kuma muka nufi Neyafolis.
Setting sail, therefore, from Troas, we ran directly to Samothracia; and the next day to Neapolis;
12 Daga can muka tafi Filibbi, wata babbar alkaryar Roma wadda kuma take babban birni a gundumar Makidoniya. Muka zauna a can kwanaki masu yawa.
and came thence to Philippi, which is a city of the first part of Macedonia, a colony: and we continued in this city for some days.
13 A Asabbaci, muka fita ƙofar birnin zuwa bakin kogi, inda muke tsammani za mu sami wurin yin addu’a. Muka zauna muka fara yin wa matan da suka taru a can magana.
And on the Sabbath day we went out of the city to the side of the river, according to the custom, where was an oratory; and sitting down, we spoke to the women that were assembled there.
14 Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.
And a certain woman named Lydia, a seller of purple, of the city of Thyatira, a worshiper of God, heard the discourse: whose heart the Lord opened to attend to the things which were spoken by Paul.
15 Da aka yi mata baftisma tare da iyalin gidanta, sai ta gayyace mu zuwa gidanta. Ta ce, “In kun amince ni mai bi ce cikin Ubangiji, sai ku zo ku sauka a gidana.” Sai ta kuwa rinjaye mu.
And when she was immersed, with her family, she entreated us, saying, If you have judged me to be faithful to the Lord, enter into my house, and continue there. And she compelled us.
16 Wata rana muna tafiya zuwa wurin yin addu’a, sai muka sadu da wata baranya mai ruhun aljani mai duba. Takan samo wa mutanenta kuɗi da yawa, duban da take yi.
Now it came to pass, that as we were going to the oratory, we were met by a certain maid-servant that had a spirit of divination, who brought her owners much gain by prophesying:
17 Wannan yarinya kuwa ta bi Bulus da kuma sauranmu, tana ihu tana cewa, “Waɗannan mutane bayin Allah Mafi Ɗaukaka ne, suna sanar da ku hanyar ceto.”
the same, following after Paul and us, cried out, These men are the servants of the Most High God, who declare to you the way of salvation.
18 Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.
And this she did for several days. But Paul, being grieved, turned and said to the spirit, I charge you, in the name of Jesus Christ, to go out of her. And it went out that very hour.
19 Da iyayengijin baranyar suka ga hanyar samun kuɗinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila suka ja su zuwa cikin kasuwa don su fuskanci hukuma.
But when her owners saw that the hope of their gain was gone; laying hold of Paul and Silas, they dragged them to the market place, to the magistrates:
20 Sai suka kawo su a gaban alƙalai suka ce, “Waɗannan Yahudawa ne, suna kuma birkitar mana da gari,
and having brought them to the generals of the army, they said, These men, who are Jews, mightily disturb our city;
21 ta wurin koyar da al’adun da ba daidai ba ne mu Romawa mu karɓa ko mu aikata.”
and teach customs, which it is not lawful for us to receive and practice, being Romans.
22 Sai taron suka fāɗa wa Bulus da Sila gaba ɗaya, alƙalan kuwa suka yi umarni a tuɓe su a kuma yi musu dūka.
And the populace rose up together against them; and the generals tearing off their garments, commanded them to be beaten with rods.
23 Bayan an yi musu bulala sosai, sai aka jefa su cikin kurkuku, aka umarci mai gadin kurkukun yă tsare su da kyau.
And when they had laid many stripes upon them, they cast them into prison, charging the jailor to keep them safely.
24 Da karɓan irin umarnan nan, sai ya sa su can cikin ɗakin kurkuku na ciki-ciki, kuma ya ɗaura ƙafafunsu a turu.
Who, having received such a strict charge, threw them into the inner prison, and secured their feet fast in the stocks.
25 Wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu’a suna rera waƙoƙi ga Allah, sauran’yan kurkuku kuwa suna sauraronsu.
But at midnight, Paul and Silas having prayed, sung a hymn to God: and the prisoners heard them.
26 Ba zato ba tsammani sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa har tushen ginin kurkukun ya jijjiga. Nan da nan sai duk ƙofofin kurkukun suka bubbuɗe, sarƙoƙin kowa kuma suka ɓaɓɓalle.
And, on a sudden, there was a great earthquake, so that the foundations of the prisoner were shaken: and immediately all the doors were opened, and the bonds of all the prisoners were loosed.
27 Mai gadin kurkukun ya farka daga barci, sa’ad da ya ga ƙofofin kurkukun a buɗe, sai ya zāre takobinsa yana shirin kashe kansa domin ya ɗauka’yan kurkukun sun gudu.
And the jailor, awaking out of his sleep, and seeing the doors of the prison opened, drew his sword, and was going to kill himself, supposing that the prisoners were fled.
28 Amma Bulus ya yi ihu ya ce, “Kada ka yi wa kanka lahani! Dukanmu muna nan!”
But Paul cried out, with a loud voice, saying, Do yourself no harm, for we are all here.
29 Mai gadin kurkukun ya kira a kawo fitilu, ya ruga ciki ya fāɗi yana rawan jiki a gaban Bulus da Sila.
And he called for lights, and sprung in; and, being in a tremor, fell down before Paul and Silas;
30 Sai ya fito da su waje ya kuma tambaye su ya ce, “Ranku yă daɗe, me zan yi domin in sami ceto?”
and, bringing them out, he said, O Sirs, what must I do to be saved?
31 Suka amsa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”
And they said, Believe in the Lord Jesus Christ, and you shall be saved, and your house.
32 Sa’an nan suka yi masa maganar Ubangiji shi da kuma dukan sauran da suke a gidansa.
And they spoke to him the word of the Lord, and to all that were in his house.
33 A wannan sa’a na daren, mai gadin kurkukun ya ɗauke su ya wanke musu raunukansu; nan take aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.
And taking them, that very hour of the night, he washed their stripes; and was immediately immersed, himself, and all his.
34 Sai mai gadin kurkukun ya kawo su cikin gidansa ya ba su abinci; ya kuwa cika da murna don yă gaskata da Allah, shi da dukan iyalinsa.
And having brought them into his house, he spread the table before them: and believing in the God, with all his house, he was transported with joy.
35 Da gari ya waye, sai alƙalan suka aika ma’aikatansu wajen mai gadin kurkukun da umarni cewa, “Ka saki mutanen nan.”
And when it was day, the magistrates sent the sergeants, saying, Dismiss those men.
36 Sai mai gadin kurkukun ya gaya wa Bulus cewa, “Alƙalai sun ba da umarni a sake ku kai da Sila. Yanzu sai ku tafi. Ku sauka lafiya.”
And the keeper of the prison told these things to Paul, The generals have sent that you may be dismissed; now, therefore, go out, and pursue your journey in peace.
37 Amma Bulus ya ce wa ma’aikatan, “Sun yi mana dūka a fili ba tare da shari’a ba, ko da yake mu’yan ƙasar Roma ne, suka kuma jefa mu cikin kurkuku. Yanzu suna so su fitar da mu a ɓoye? A’a! Sai dai su zo da kansu su rako mu waje.”
But Paul said to them, They have beaten us, who are Romans, publicly and uncondemned, and have cast us into prison; and do they now thrust us out privately? By no means: but let them come themselves, and conduct us out.
38 Sai ma’aikatan suka faɗa wa alƙalan wannan, da suka ji cewa Bulus da Sila Romawa ne, sai suka ji tsoro.
And the sergeants reported these words to the generals. And when they had heard that they were Romans, they were afraid:
39 Sai suka zo don su roƙe su, suka yi musu rakiya daga kurkukun, suna roƙonsu su bar birnin.
and they came and comforted them; and conducting them out, requested that they would depart from the city.
40 Bayan Bulus da Sila suka fita daga kurkukun, sai suka tafi gidan Lidiya, inda suka sadu da’yan’uwa suka kuma ƙarfafa su. Sa’an nan suka tafi.
And coming out of the prison, they entered into the house of Lydia: and when they had seen the brethren, they comforted them, and departed.

< Ayyukan Manzanni 16 >