< Ayyukan Manzanni 15 >
1 Waɗansu mutane suka gangara daga Yahudiya zuwa Antiyok suna kuma koya wa’yan’uwa cewa, “Sai ko an yi muku kaciya bisa ga al’ada da Musa ya koyar, in ba haka ba, ba za ku sami ceto ba.”
And certain having come down from Judea, were teaching the brothers, “If you are not circumcised after the custom of Moses, you are not able to be saved”;
2 Wannan ya kai Bulus da Barnabas suka shiga babban gardama da muhawwara da su. Saboda haka aka naɗa Bulus da Barnabas tare da waɗansu masu bi, su haura zuwa Urushalima don su ga manzanni da dattawa a kan wannan magana.
there having been, therefore, not a little dissension and debate to Paul and Barnabas with them, they arranged for Paul and Barnabas, and certain others of them, to go up to the apostles and elders to Jerusalem about this question;
3 Ikkilisiya ta raka su suka tafi, yayinda suke ratsawa ta Funisiya da Samariya, suka ba da labari yadda Al’ummai suka tuba. Wannan labarin ya sa dukan’yan’uwa suka yi murna ƙwarai.
they indeed, then, having been sent forward by the assembly, were passing through Phoenicia and Samaria, declaring the conversion of the nations, and they were causing great joy to all the brothers.
4 Sa’ad da suka isa Urushalima, sai ikkilisiya da manzanni da kuma dattawa suka marabce su, sai suka ba su rahoton dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu.
And having come to Jerusalem, they were received by the assembly, and the apostles, and the elders; they also declared as many things as God did with them;
5 Sai waɗansu daga cikin masu bin da suke na ƙungiyar Farisiyawa suka miƙe tsaye suka ce, “Dole ne a yi wa Al’ummai kaciya a kuma bukace su su yi biyayya da dokokin Musa.”
and there rose up certain of those of the sect of the Pharisees who believed, saying, “It is required to circumcise them, to command them also to keep the Law of Moses.”
6 Sai manzanni da dattawa suka taru don su duba maganar.
And there were gathered together the apostles and the elders, to see about this matter,
7 Bayan aka yi muhawwara da sosai, sai Bitrus ya miƙe tsaye ya yi musu jawabi ya ce, “’Yan’uwa, kun san cewa a kwanakin baya Allah ya yi zaɓe a cikinku don Al’ummai su ji daga leɓunana saƙon bishara su kuma gaskata.
and there having been much disputing, Peter having risen up said to them, “Men, brothers, you know that from former days God made choice among us, through my mouth, for the nations to hear the word of the good news, and to believe;
8 Allah, wanda ya san zuciya, ya nuna cewa ya karɓe su ta wurin ba su Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya ba mu.
and the heart-knowing God bore them testimony, having given to them the Holy Spirit, even as also to us,
9 Bai nuna bambanci tsakaninmu da su ba, gama ya tsarkake zukatansu ta wurin bangaskiya.
and also put no difference between us and them, having purified their hearts by faith;
10 To, fa, don me kuke ƙoƙari ku gwada Allah ta wurin ɗora wa almajiran nan kayan da mu ko kakanninmu ba mu iya ɗauka ba?
now, therefore, why do you tempt God, to put a yoke on the neck of the disciples, which neither our fathers nor we were able to bear?
11 A’a! Mun gaskata cewa ta wurin alherin Ubangiji Yesu ne muka sami ceto, kamar yadda su ma suka samu.”
But through the grace of the Lord Jesus Christ, we believe to be saved, even as also they.”
12 Sai duk taron suka yi tsit yayinda suke sauraron Barnabas da Bulus suna ba da labari game da ayyuka da kuma abubuwan banmamakin da Allah ya yi a cikin Al’ummai ta wurinsu.
And all the multitude kept silence and were listening to Barnabas and Paul expounding as many signs and wonders as God did among the nations through them;
13 Da suka gama, sai Yaƙub ya yi magana ya ce, “’Yan’uwa, ku saurare ni.
and after they were silent, James answered, saying, “Men, brothers, listen to me:
14 Siman ya bayyana mana yadda Allah da farko ya nuna damuwarsa ta wurin ɗaukan mutane daga cikin Al’ummai su zama nasa.
Simeon expounded how at first God looked on [us] to take a people out of [the] nations for His Name,
15 Kalmomin annabawa sun yi daidai da wannan, kamar yadda yake a rubuce cewa,
and to this the words of the Prophets agree, as it has been written:
16 “‘Bayan wannan zan koma in kuma sāke gina tentin Dawuda da ya rushe. Kufansa zan sāke gina, in kuma mai da shi,
After these things I will return, And I will rebuild the dwelling place of David that has fallen down, And I will rebuild its ruins, And will set it upright—
17 don ragowar mutane su nemi Ubangiji, kuma duk Al’umman da suke kira bisa sunana, in ji Ubangiji, wanda yake yin waɗannan abubuwa’
That the remnant of men may seek after the LORD, And all the nations on whom My Name has been called, Says the LORD, who is doing all these things.
18 da aka sani tun zamanai. (aiōn )
Known from the ages to God are all His works. (aiōn )
19 “Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa Al’ummai waɗanda suke juyowa ga Allah.
For this reason I judge: not to trouble those who turn back to God from the nations,
20 A maimakon haka, ya kamata mu rubuta musu cewa, su guji abincin da alloli suka ƙazantar, da fasikanci, da naman dabbar da aka murɗe da kuma jini.
but to write to them to abstain from the defilements of the idols, and the whoredom, and the strangled thing, and the blood;
21 Gama Musa ya yi wa’azi a kowace birni tun zamanin dā, ana kuma karanta shi a majami’u kowane Asabbaci.”
for Moses has those preaching him from former generations in every city—being read every Sabbath in the synagogues.”
22 Sai manzanni da dattawa, tare da dukan ikkilisiya, suka yanke shawara su zaɓi waɗansu daga cikin mutanensu su kuma aike su zuwa Antiyok tare da Bulus da Barnabas. Sai suka zaɓi Yahuda (wanda ake kira Barsabbas) da kuma Sila, mutum biyu da suke shugabanni cikin’yan’uwa.
Then it seemed good to the apostles and the elders, with the whole assembly, to send to Antioch with Paul and Barnabas chosen men out of themselves—Judas surnamed Barsabas, and Silas, leading men among the brothers—
23 Tare da su suka aika da wannan wasiƙa. Daga manzanni da dattawa,’yan’uwanku. Zuwa ga Al’ummai masu bi a Antiyok, Suriya da Silisiya. Gaisuwa.
having written through their hand thus: “The apostles, and the elders, and the brothers, to those in Antioch, and Syria, and Cilicia, brothers, who [are] of the nations, greeting;
24 Mun ji cewa, waɗansu da sun fita daga cikinmu ba tare da izininmu ba suka kuma dame ku, suna tā da hankalinku ta wurin abin da suka ce.
seeing we have heard that some having gone forth from us troubled you with words, subverting your souls, saying to be circumcised and to keep the Law, to whom we gave no charge,
25 Saboda haka dukanmu mun yarda mu zaɓi waɗansu mutane mu kuma aike su wurinku tare da ƙaunatattun abokanmu Barnabas da Bulus
it seemed good to us, having come together with one accord, to send to you chosen men, with our beloved Barnabas and Paul—
26 mutanen da suka sa rayukansu cikin hatsari saboda sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi.
men who have given up their lives for the Name of our Lord Jesus Christ—
27 Saboda haka muna aika Yahuda da Sila don su tabbatar muku da baki abin da muka rubuta.
we have sent, therefore, Judas and Silas, and they are telling the same things by word.
28 Ya gamshe Ruhu Mai Tsarki da mu ma kada a ɗora muku nauyi fiye da na waɗannan abubuwa.
For it seemed good to the Holy Spirit, and to us, to lay no more burden on you, except these necessary things:
29 Ku guji abincin da aka yi wa alloli hadaya, da jini, da naman dabbar da aka murɗe da kuma fasikanci. Za ku kyauta in kun kiyaye waɗannan abubuwa. Ku huta lafiya.
to abstain from things offered to idols, and blood, and a strangled thing, and whoredom; keeping yourselves from which, you will do well; be strong!”
30 Aka sallami mutanen sai suka gangara zuwa Antiyok, inda suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da wasiƙar.
They then, indeed, having been let go, went to Antioch, and having brought the multitude together, delivered the letter,
31 Mutanen suka karantata suka kuma yi farin ciki saboda saƙonta mai ƙarfafawa.
and having read [it] they rejoiced for the consolation;
32 Yahuda da Sila, waɗanda su kansu annabawa ne, suka yi magana sosai don su gina su kuma ƙarfafa’yan’uwa.
Judas also and Silas, also being prophets themselves, through much discourse exhorted the brothers, and confirmed,
33 Bayan suka yi’yan kwanaki a can, sai’yan’uwa suka sallame su da albarkar salama su dawo wurin waɗanda suka aike su.
and having passed some time, they were let go with peace from the brothers to the apostles;
[[and it seemed good to Silas to remain there still.]]
35 Amma Bulus da Barnabas kuwa suka dakata a Antiyok, inda su da waɗansu da yawa suka yi koyarwa suka kuma yi wa’azin maganar Ubangiji.
And Paul and Barnabas continued in Antioch, teaching and proclaiming good news—with many others also—the word of the LORD;
36 Bayan’yan kwanaki sai Bulus ya ce wa Barnabas, “Mu koma mu ziyarci’yan’uwa a duk garuruwan da muka yi wa’azin bisharar Ubangiji mu ga yadda suke.”
and after certain days, Paul said to Barnabas, “Having turned back again, we may look after our brothers, in every city in which we have preached the word of the LORD—how they are.”
37 Barnabas ya so Yohanna, wanda ake kira Markus ya tafi tare da su,
And Barnabas resolved to take with [them] John called Mark,
38 amma Bulus bai ga ya kyautu ya tafi da shi ba, domin ya yashe su a Famfiliya bai kuwa ci gaba tare da su a aikin ba.
and Paul was not thinking it good to take him with them who withdrew from them from Pamphylia, and did not go with them to the work;
39 Suka sami saɓanin ra’ayi tsakaninsu har suka rabu. Barnabas ya ɗauki Markus suka shiga jirgin ruwa zuwa Saifurus,
there came, therefore, a sharp contention, so that they were parted from one another, and Barnabas having taken Mark, sailed to Cyprus,
40 amma Bulus ya zaɓi Sila suka kuwa tashi, bayan’yan’uwa suka danƙa su ga alherin Ubangiji.
and Paul having chosen Silas, went forth, having been given up to the grace of God by the brothers;
41 Ya ratsa ta Suriya da Silisiya, yana ƙarfafa ikkilisiyoyi.
and he went through Syria and Cilicia, confirming the assemblies.