< Ayyukan Manzanni 15 >

1 Waɗansu mutane suka gangara daga Yahudiya zuwa Antiyok suna kuma koya wa’yan’uwa cewa, “Sai ko an yi muku kaciya bisa ga al’ada da Musa ya koyar, in ba haka ba, ba za ku sami ceto ba.”
And certain men came down from Judea, and taught the brethren, saying: Unless you be circumcised, according to the custom of Moses, you can not be saved.
2 Wannan ya kai Bulus da Barnabas suka shiga babban gardama da muhawwara da su. Saboda haka aka naɗa Bulus da Barnabas tare da waɗansu masu bi, su haura zuwa Urushalima don su ga manzanni da dattawa a kan wannan magana.
Therefore, after Paul and Barnabas had no little dissension and disputation with them, they determined that Paul and Barnabas, and certain others from among them, should go up to Jerusalem, to the apostles and elders, about this question.
3 Ikkilisiya ta raka su suka tafi, yayinda suke ratsawa ta Funisiya da Samariya, suka ba da labari yadda Al’ummai suka tuba. Wannan labarin ya sa dukan’yan’uwa suka yi murna ƙwarai.
Being, therefore, con ducted on their journey by the church, they passed through Phenicia and Samaria, making known the conversion of the Gentiles; and they gave great joy to all the brethren.
4 Sa’ad da suka isa Urushalima, sai ikkilisiya da manzanni da kuma dattawa suka marabce su, sai suka ba su rahoton dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu.
When they arrived at Jerusalem, they were received by the church, and the apostles and elders, and they declared all that God had done with them.
5 Sai waɗansu daga cikin masu bin da suke na ƙungiyar Farisiyawa suka miƙe tsaye suka ce, “Dole ne a yi wa Al’ummai kaciya a kuma bukace su su yi biyayya da dokokin Musa.”
But some of the sect of the Pharisees, who believed, arose, saying, that it was necessary to circumcise them, and to command them to keep the law of Moses.
6 Sai manzanni da dattawa suka taru don su duba maganar.
And the apostles and elders came together to deliberate about this matter.
7 Bayan aka yi muhawwara da sosai, sai Bitrus ya miƙe tsaye ya yi musu jawabi ya ce, “’Yan’uwa, kun san cewa a kwanakin baya Allah ya yi zaɓe a cikinku don Al’ummai su ji daga leɓunana saƙon bishara su kuma gaskata.
And after there had been much disputing, Peter arose, and said to them: Brethren, you know that, at the beginning, God made choice among us, that, by my mouth, the Gentiles should hear the word of the Gospel, and believe.
8 Allah, wanda ya san zuciya, ya nuna cewa ya karɓe su ta wurin ba su Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya ba mu.
And God, who knows the heart, became a witness for them, by giving them the Holy Spirit, as he gave it also to us;
9 Bai nuna bambanci tsakaninmu da su ba, gama ya tsarkake zukatansu ta wurin bangaskiya.
and he made no distinction between us and them, purifying their hearts by faith.
10 To, fa, don me kuke ƙoƙari ku gwada Allah ta wurin ɗora wa almajiran nan kayan da mu ko kakanninmu ba mu iya ɗauka ba?
Now, therefore, why do you put God to the proof, by placing a yoke upon the neck of the disciples, which neither our fathers, nor we ourselves, were able to bear?
11 A’a! Mun gaskata cewa ta wurin alherin Ubangiji Yesu ne muka sami ceto, kamar yadda su ma suka samu.”
But we believe that we shall be saved, even as they, through the grace of our Lord Jesus Christ.
12 Sai duk taron suka yi tsit yayinda suke sauraron Barnabas da Bulus suna ba da labari game da ayyuka da kuma abubuwan banmamakin da Allah ya yi a cikin Al’ummai ta wurinsu.
Then all the multitude kept silence, and listened to Barnabas and Paul, while they made known what signs and wonders God had done by them among the Gentiles.
13 Da suka gama, sai Yaƙub ya yi magana ya ce, “’Yan’uwa, ku saurare ni.
And after they were silent, James answered and said: Brethren, hear me;
14 Siman ya bayyana mana yadda Allah da farko ya nuna damuwarsa ta wurin ɗaukan mutane daga cikin Al’ummai su zama nasa.
Simeon has declared how God, at the first, did visit the Gentiles, in order to take out from among them a people for his name.
15 Kalmomin annabawa sun yi daidai da wannan, kamar yadda yake a rubuce cewa,
And with this agree the words of the prophets; as it is written,
16 “‘Bayan wannan zan koma in kuma sāke gina tentin Dawuda da ya rushe. Kufansa zan sāke gina, in kuma mai da shi,
After this I will return, and build again the tabernacle of David which has fallen down; and I will build again its ruins, and I will set it up;
17 don ragowar mutane su nemi Ubangiji, kuma duk Al’umman da suke kira bisa sunana, in ji Ubangiji, wanda yake yin waɗannan abubuwa’
that the rest of men may seek after the Lord, and all the Gentiles, upon whom my name has been called, says the Lord, who does all these things.
18 da aka sani tun zamanai. (aiōn g165)
Known to God from eternity are all bis works. (aiōn g165)
19 “Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa Al’ummai waɗanda suke juyowa ga Allah.
For these reasons, my judgment is, that we give no trouble to those who, from among the Gentiles, have turned to God;
20 A maimakon haka, ya kamata mu rubuta musu cewa, su guji abincin da alloli suka ƙazantar, da fasikanci, da naman dabbar da aka murɗe da kuma jini.
but that we write to them to abstain from pollutions of idols, and from lewdness, and from what is strangled, and from blood.
21 Gama Musa ya yi wa’azi a kowace birni tun zamanin dā, ana kuma karanta shi a majami’u kowane Asabbaci.”
For, from ancient times, Moses has, in every city, those who preach him, being read in the synagogue every sabbath-day.
22 Sai manzanni da dattawa, tare da dukan ikkilisiya, suka yanke shawara su zaɓi waɗansu daga cikin mutanensu su kuma aike su zuwa Antiyok tare da Bulus da Barnabas. Sai suka zaɓi Yahuda (wanda ake kira Barsabbas) da kuma Sila, mutum biyu da suke shugabanni cikin’yan’uwa.
Then it pleased the apostles and the elders, with the whole church, to send to Antioch, with Paul and Barnabas, chosen men from among themselves; Judas, who was surnamed Barsabas, and Silas, chief men among the brethren;
23 Tare da su suka aika da wannan wasiƙa. Daga manzanni da dattawa,’yan’uwanku. Zuwa ga Al’ummai masu bi a Antiyok, Suriya da Silisiya. Gaisuwa.
and they wrote by their hands as follows: The apostles, and the elders, and the brethren, to the brethren of the Gentiles in Antioch and Syria and Cilicia, greeting:
24 Mun ji cewa, waɗansu da sun fita daga cikinmu ba tare da izininmu ba suka kuma dame ku, suna tā da hankalinku ta wurin abin da suka ce.
Inasmuch as we have heard that certain persons went out from us and troubled you with words, subverting your souls, saying, That you must be circumcised, and keep the law, to whom we gave no commandment,
25 Saboda haka dukanmu mun yarda mu zaɓi waɗansu mutane mu kuma aike su wurinku tare da ƙaunatattun abokanmu Barnabas da Bulus
it has seemed good to us, having come together with one mind, to send chosen men to you, with our beloved Barnabas and Paul,
26 mutanen da suka sa rayukansu cikin hatsari saboda sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi.
men who have endangered their lives for the name of our Lord Jesus Christ.
27 Saboda haka muna aika Yahuda da Sila don su tabbatar muku da baki abin da muka rubuta.
We have sent, therefore, Judas and Silas, who will tell you the same things in word.
28 Ya gamshe Ruhu Mai Tsarki da mu ma kada a ɗora muku nauyi fiye da na waɗannan abubuwa.
For it has seemed good to the Holy Spirit, and to us, to lay upon you no greater burden than these necessary things:
29 Ku guji abincin da aka yi wa alloli hadaya, da jini, da naman dabbar da aka murɗe da kuma fasikanci. Za ku kyauta in kun kiyaye waɗannan abubuwa. Ku huta lafiya.
That you abstain from things sacrificed to idols, and from blood, and from what is strangled, and from lewdness; from which if you keep yourselves carefully, you will do well. Farewell.
30 Aka sallami mutanen sai suka gangara zuwa Antiyok, inda suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da wasiƙar.
So when these men were dismissed, they came to Antioch: and having assembled the multitude, they delivered this letter.
31 Mutanen suka karantata suka kuma yi farin ciki saboda saƙonta mai ƙarfafawa.
When they had read it, they rejoiced for the consolation which it gave.
32 Yahuda da Sila, waɗanda su kansu annabawa ne, suka yi magana sosai don su gina su kuma ƙarfafa’yan’uwa.
And Judas and Silas, who were also prophets, exhorted the brethren with many words, and strengthened them.
33 Bayan suka yi’yan kwanaki a can, sai’yan’uwa suka sallame su da albarkar salama su dawo wurin waɗanda suka aike su.
And after spending some time, they were dismissed in peace from the brethren, to those who had sent them.
But it pleased Silas to remain there.
35 Amma Bulus da Barnabas kuwa suka dakata a Antiyok, inda su da waɗansu da yawa suka yi koyarwa suka kuma yi wa’azin maganar Ubangiji.
Paul also and Barnabas continued in Antioch, teaching and preaching, with many others, the word of the Lord.
36 Bayan’yan kwanaki sai Bulus ya ce wa Barnabas, “Mu koma mu ziyarci’yan’uwa a duk garuruwan da muka yi wa’azin bisharar Ubangiji mu ga yadda suke.”
And, after some days, Paul said to Barnabas, let us return, and visit our brethren in every city in which we have preached the word of the Lord, and see how they do.
37 Barnabas ya so Yohanna, wanda ake kira Markus ya tafi tare da su,
And Barnabas determined to take with him John, whose surname was Mark.
38 amma Bulus bai ga ya kyautu ya tafi da shi ba, domin ya yashe su a Famfiliya bai kuwa ci gaba tare da su a aikin ba.
But Paul did not think it proper to take with them him who had departed from them from Pamphylia, and did not go with them to the work.
39 Suka sami saɓanin ra’ayi tsakaninsu har suka rabu. Barnabas ya ɗauki Markus suka shiga jirgin ruwa zuwa Saifurus,
There was, therefore, a sharp contention, so that they separated from each other: and Barnabas took Mark, and sailed to Cyprus.
40 amma Bulus ya zaɓi Sila suka kuwa tashi, bayan’yan’uwa suka danƙa su ga alherin Ubangiji.
But Paul chose Silas, and departed, having been commended to the grace of God by the brethren.
41 Ya ratsa ta Suriya da Silisiya, yana ƙarfafa ikkilisiyoyi.
And he passed through Syria and Cilicia, strengthening the churches.

< Ayyukan Manzanni 15 >