< Ayyukan Manzanni 15 >
1 Waɗansu mutane suka gangara daga Yahudiya zuwa Antiyok suna kuma koya wa’yan’uwa cewa, “Sai ko an yi muku kaciya bisa ga al’ada da Musa ya koyar, in ba haka ba, ba za ku sami ceto ba.”
Og der kom nogle ned fra Judæa, som lærte Brødrene: "Dersom I ikke lade eder omskære efter Mose Skik, kunne I ikke blive frelste."
2 Wannan ya kai Bulus da Barnabas suka shiga babban gardama da muhawwara da su. Saboda haka aka naɗa Bulus da Barnabas tare da waɗansu masu bi, su haura zuwa Urushalima don su ga manzanni da dattawa a kan wannan magana.
Da nu Paulus og Barnabas kom i en ikke ringe Splid og Strid med dem, så besluttede man, at Paulus og Barnabas og nogle andre af dem skulde drage op til Jerusalem til Apostlene og de Ældste i Anledning af dette Spørgsmål.
3 Ikkilisiya ta raka su suka tafi, yayinda suke ratsawa ta Funisiya da Samariya, suka ba da labari yadda Al’ummai suka tuba. Wannan labarin ya sa dukan’yan’uwa suka yi murna ƙwarai.
Disse bleve da sendte af Sted af Menigheden og droge igennem Fønikien og Samaria og fortalte om Hedningernes Omvendelse, og de gjorde alle Brødrene stor Glæde.
4 Sa’ad da suka isa Urushalima, sai ikkilisiya da manzanni da kuma dattawa suka marabce su, sai suka ba su rahoton dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu.
Men da de kom til Jerusalem, bleve de modtagne af Menigheden og Apostlene og de Ældste, og de kundgjorde, hvor store Ting Gud havde gjort med dem.
5 Sai waɗansu daga cikin masu bin da suke na ƙungiyar Farisiyawa suka miƙe tsaye suka ce, “Dole ne a yi wa Al’ummai kaciya a kuma bukace su su yi biyayya da dokokin Musa.”
Men nogle af Farisæernes Parti, som vare blevne troende, stode op og sagde: "Man bør omskære dem og befale dem at holde Mose Lov."
6 Sai manzanni da dattawa suka taru don su duba maganar.
Men Apostlene og de Ældste forsamlede sig for at overlægge denne Sag.
7 Bayan aka yi muhawwara da sosai, sai Bitrus ya miƙe tsaye ya yi musu jawabi ya ce, “’Yan’uwa, kun san cewa a kwanakin baya Allah ya yi zaɓe a cikinku don Al’ummai su ji daga leɓunana saƙon bishara su kuma gaskata.
Men da man havde tvistet meget herom, stod Peter op og sagde til dem: "I Mænd, Brødre! I vide, at for lang Tid siden gjorde Gud det Valg iblandt eder, at Hedningerne ved min Mund skulde høre Evangeliets Ord og tro.
8 Allah, wanda ya san zuciya, ya nuna cewa ya karɓe su ta wurin ba su Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya ba mu.
Og Gud, som kender Hjerterne, gav dem Vidnesbyrd ved at give dem den Helligånd lige så vel som os.
9 Bai nuna bambanci tsakaninmu da su ba, gama ya tsarkake zukatansu ta wurin bangaskiya.
Og han gjorde ingen Forskel imellem os og dem, idet han ved Troen rensede deres Hjerter.
10 To, fa, don me kuke ƙoƙari ku gwada Allah ta wurin ɗora wa almajiran nan kayan da mu ko kakanninmu ba mu iya ɗauka ba?
Hvorfor friste I da nu Gud, så I lægge et Åg på Disciplenes Nakke, som hverken vore Fædre eller vi have formået at bære?
11 A’a! Mun gaskata cewa ta wurin alherin Ubangiji Yesu ne muka sami ceto, kamar yadda su ma suka samu.”
Men vi tro, at vi bliver frelste ved den Herres Jesu Nåde på samme Måde som også de."
12 Sai duk taron suka yi tsit yayinda suke sauraron Barnabas da Bulus suna ba da labari game da ayyuka da kuma abubuwan banmamakin da Allah ya yi a cikin Al’ummai ta wurinsu.
Men hele Mængden tav og de hørte Barnabas og Paulus fortælle, hvor store Tegn og Undere Gud havde gjort iblandt Hedningerne ved dem.
13 Da suka gama, sai Yaƙub ya yi magana ya ce, “’Yan’uwa, ku saurare ni.
Men da de havde hørt op at tale, tog Jakob til Orde og sagde: "I Mænd, Brødre, hører mig!"
14 Siman ya bayyana mana yadda Allah da farko ya nuna damuwarsa ta wurin ɗaukan mutane daga cikin Al’ummai su zama nasa.
Simon har fortalt, hvorledes Gud først drog Omsorg for at tage ud af Hedninger et Folk for sit Navn.
15 Kalmomin annabawa sun yi daidai da wannan, kamar yadda yake a rubuce cewa,
Og dermed stemme Profeternes Tale overens, som der er skrevet:
16 “‘Bayan wannan zan koma in kuma sāke gina tentin Dawuda da ya rushe. Kufansa zan sāke gina, in kuma mai da shi,
"Derefter vil jeg vende tilbage og atter opbygge Davids faldne Hytte, og det nedrevne af den vil jeg atter opbygge og oprejse den igen,
17 don ragowar mutane su nemi Ubangiji, kuma duk Al’umman da suke kira bisa sunana, in ji Ubangiji, wanda yake yin waɗannan abubuwa’
for at de øvrige af Menneskene skulle søge Herren, og alle Hedningerne, over hvilke mit Navn er nævnet, siger Herren, som gør dette."
18 da aka sani tun zamanai. (aiōn )
Gud kender fra Evighed af alle sine Gerninger. (aiōn )
19 “Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa Al’ummai waɗanda suke juyowa ga Allah.
Derfor mener jeg, at man ikke skal besvære dem af Hedningerne, som omvende sig til Gud,
20 A maimakon haka, ya kamata mu rubuta musu cewa, su guji abincin da alloli suka ƙazantar, da fasikanci, da naman dabbar da aka murɗe da kuma jini.
men skrive til dem, at de skulle afholde sig fra Besmittelse med Afguderne og fra Utugt og fra det kvalte og fra Blodet.
21 Gama Musa ya yi wa’azi a kowace birni tun zamanin dā, ana kuma karanta shi a majami’u kowane Asabbaci.”
Thi Moses har fra gammel Tid i hver By Mennesker, som prædike ham, idet han oplæses hver Sabbat i Synagogerne."
22 Sai manzanni da dattawa, tare da dukan ikkilisiya, suka yanke shawara su zaɓi waɗansu daga cikin mutanensu su kuma aike su zuwa Antiyok tare da Bulus da Barnabas. Sai suka zaɓi Yahuda (wanda ake kira Barsabbas) da kuma Sila, mutum biyu da suke shugabanni cikin’yan’uwa.
Da besluttede Apostelene og de Ældste tillige med hele Menigheden at udvælge nogle Mænd af deres Midte og sende dem til Antiokia tillige med Paulus og Barnabas, nemlig Judas, kaldet Barsabbas, og Silas, hvilke Mænd vare ansete iblandt Brødrene.
23 Tare da su suka aika da wannan wasiƙa. Daga manzanni da dattawa,’yan’uwanku. Zuwa ga Al’ummai masu bi a Antiyok, Suriya da Silisiya. Gaisuwa.
Og de skreve således med dem: "Apostlene og de Ældste og Brødrene hilse Brødrene af Hedningerne i Antiokia og Syrien og Kilikien.
24 Mun ji cewa, waɗansu da sun fita daga cikinmu ba tare da izininmu ba suka kuma dame ku, suna tā da hankalinku ta wurin abin da suka ce.
Efterdi vi have hørt, at nogle, som ere komne fra os, have forvirret eder med Ord og voldt eders Sjæle Uro uden at have nogen Befaling fra os,
25 Saboda haka dukanmu mun yarda mu zaɓi waɗansu mutane mu kuma aike su wurinku tare da ƙaunatattun abokanmu Barnabas da Bulus
så have vi endrægtigt forsamlede, besluttet at udvælge nogle Mænd og sende dem til eder med vore elskelige Barnabas og Paulus,
26 mutanen da suka sa rayukansu cikin hatsari saboda sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Mænd, som have vovet deres Liv for vor Herres Jesu Kristi Navn.
27 Saboda haka muna aika Yahuda da Sila don su tabbatar muku da baki abin da muka rubuta.
Vi have derfor sendt Judas og Silas, der også mundtligt skulle forkynde det samme.
28 Ya gamshe Ruhu Mai Tsarki da mu ma kada a ɗora muku nauyi fiye da na waɗannan abubuwa.
Thi det er den Helligånds Beslutning og vor, ingen videre Byrde at pålægge eder uden disse nødvendige Ting:
29 Ku guji abincin da aka yi wa alloli hadaya, da jini, da naman dabbar da aka murɗe da kuma fasikanci. Za ku kyauta in kun kiyaye waɗannan abubuwa. Ku huta lafiya.
At I skulle afholde eder fra Afgudsofferkød og fra Blod og fra det kvalte og fra Utugt. Når I holde eder derfra, vil det gå eder godt. Lever vel!"
30 Aka sallami mutanen sai suka gangara zuwa Antiyok, inda suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da wasiƙar.
Så lod man dem da fare, og de kom ned til Antiokia og forsamlede Mængden og overgave Brevet.
31 Mutanen suka karantata suka kuma yi farin ciki saboda saƙonta mai ƙarfafawa.
Men da de læste det, bleve de glade over Trøsten.
32 Yahuda da Sila, waɗanda su kansu annabawa ne, suka yi magana sosai don su gina su kuma ƙarfafa’yan’uwa.
Og Judas og Silas, som også selv vare Profeter, opmuntrede Brødrene med megen Tale og styrkede dem.
33 Bayan suka yi’yan kwanaki a can, sai’yan’uwa suka sallame su da albarkar salama su dawo wurin waɗanda suka aike su.
Men da de havde opholdt sig der nogen Tid, lode Brødrene dem fare med Fred til dem, som havde udsendt dem.
(Men Silas besluttede at blive der.)
35 Amma Bulus da Barnabas kuwa suka dakata a Antiyok, inda su da waɗansu da yawa suka yi koyarwa suka kuma yi wa’azin maganar Ubangiji.
Men Paulus og Barnabas opholdt sig i Antiokia, hvor de tillige med mange andre lærte og forkyndte Herrens Ord.
36 Bayan’yan kwanaki sai Bulus ya ce wa Barnabas, “Mu koma mu ziyarci’yan’uwa a duk garuruwan da muka yi wa’azin bisharar Ubangiji mu ga yadda suke.”
Men efter nogen Tids Forløb sagde Paulus til Barnabas: "Lader os dog drage tilbage og besøge vore Brødre i hver By, hvor vi have forkyndt Herrens Ord, for at se, hvorledes det går dem."
37 Barnabas ya so Yohanna, wanda ake kira Markus ya tafi tare da su,
Men Barnabas vilde også tage Johannes, kaldet Markus, med.
38 amma Bulus bai ga ya kyautu ya tafi da shi ba, domin ya yashe su a Famfiliya bai kuwa ci gaba tare da su a aikin ba.
Men Paulus holdt for, at de ikke skulde tage den med, som havde forladt dem i Pamfylien og ikke havde fulgt med dem til Arbejdet.
39 Suka sami saɓanin ra’ayi tsakaninsu har suka rabu. Barnabas ya ɗauki Markus suka shiga jirgin ruwa zuwa Saifurus,
Der blev da en heftig Strid, så at de skiltes fra hverandre, og Barnabas tog Markus med sig og sejlede til Kypern.
40 amma Bulus ya zaɓi Sila suka kuwa tashi, bayan’yan’uwa suka danƙa su ga alherin Ubangiji.
Men Paulus udvalgte Silas og drog ud, anbefalet af Brødrene til Herrens Nåde.
41 Ya ratsa ta Suriya da Silisiya, yana ƙarfafa ikkilisiyoyi.
Men han rejste omkring i Syrien og Kilikien og styrkede Menighederne.