< Ayyukan Manzanni 14 >
1 A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
В Іконії Павло та Варнава увійшли також в юдейську синагогу та говорили так [переконливо], що багато юдеїв та греків увірувало.
2 Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
Ті ж юдеї, які відмовилися повірити, підбурили та роз’ятрили душі язичників проти братів.
3 Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
Однак [Павло та Варнава] залишалися там досить довго. Вони сміливо говорили про Господа, Який свідчив про Слово благодаті, роблячи чудеса та знамення через їхні руки.
4 Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
Мешканці міста розділилися: одні підтримували юдеїв, а інші – апостолів.
5 Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
Язичники та юдеї разом із керівниками задумали закидати їх камінням.
6 Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
Дізнавшись про це, [Павло та Варнава] втекли до міст Лікаонії – Лістри, Дервії та околиць,
7 inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
де продовжували проповідувати Добру Звістку.
8 A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
У Лістрі сидів безсилий чоловік, який ніколи не ходив, тому що був калікою від народження.
9 Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
Він слухав, як говорив Павло. Поглянувши на нього уважно й побачивши, що той має віру для зцілення,
10 sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
[Павло] голосно промовив: «Встань прямо на ноги!» Той піднявся й почав ходити.
11 Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
Люди, побачивши, що зробив Павло, почали голосно говорити лікаонською: «Боги до нас зійшли в людській подобі!»
12 Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
Вони назвали Варнаву Зевсом, а Павла Гермесом, оскільки він був головним у промові.
13 Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
Жрець Зевса, храм якого був перед містом, привів биків із вінками до воріт, бажаючи разом із народом принести жертву.
14 Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
Коли апостоли Варнава та Павло почули про це, то роздерли свій одяг, кинулися до натовпу та закричали:
15 “Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
«Люди, навіщо ви це робите? Ми такі ж люди, як і ви! Ми звіщаємо вам Добру Звістку, щоб ви відвернулися від цих марнот до живого Бога, Який створив небеса, землю, море й усе, що в них.
16 A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
У минулому Він дозволяв усім народам ходити своїми шляхами,
17 Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
хоч і не залишав їх без свідоцтва про Себе, роблячи добро, даючи дощі з неба та врожайні часи, наповняючи їжею й радощами серця ваші».
18 Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
І, говорячи це, ледве переконали народ, щоб не приносили їм жертви.
19 Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
Однак деякі юдеї, які прийшли з Антіохії та Іконії, схилили натовп [на свій бік]. Вони побили Павла камінням та виволікли його за місто, думаючи, що він уже помер.
20 Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
Але коли учні зібралися навколо нього, він піднявся та повернувся в місто. Наступного дня він разом із Варнавою вирушив у Дервію.
21 Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
У цьому місті вони проповідували Добру Звістку й набули чимало учнів. Потім повернулися до Лістри, Іконії та Антіохії.
22 suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
[Павло та Варнава] зміцнювали душі учнів, закликаючи їх продовжувати твердо вірити, та [навчали], що через великі скорботи нам треба увійти в Царство Боже.
23 Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
Вони обрали пресвітерів для кожної церкви й постом та молитвою передали їх Господеві, в Якого увірували.
24 Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
Далі, пройшовши Пісідію, [Павло та Варнава] прийшли до Памфілії.
25 kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
Звістивши Слово в Пергії, прийшли до Атталії.
26 Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
Звідти відпливли до Антіохії, де були передані благодаті Божій для справи, яку виконали.
27 Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
Повернувшись, вони скликали всю церкву та розповіли, як багато Бог зробив через них і як Він відчинив для язичників двері віри.
28 Suka kuma jima a can tare da almajirai.
Вони залишалися з учнями чимало часу.