< Ayyukan Manzanni 14 >

1 A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
Il arriva qu'à Iconium, ils se rendirent ensemble à la synagogue, juive et y parlèrent de telle sorte que Juifs et Grecs devinrent croyants en grand nombre.
2 Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
Mais les Juifs restés incrédules excitèrent et indisposèrent la population païenne contre les frères.
3 Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
Ceux-ci prolongèrent alors leur séjour, pleins de courage et se confiant au Seigneur qui rendait témoignage à la prédication de sa grâce en leur donnant de faire des miracles et des prodiges.
4 Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
Cependant la population de la ville se divisa, les uns furent pour les Juifs, les autres pour les apôtres;
5 Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
et comme les Juifs et les païens, d'accord avec les autorités, parlaient de les maltraiter et de les lapider,
6 Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
les apôtres, l'ayant appris, se réfugièrent dans les villes de Lycaonie, à Lystre, à Derbé et aux environs,
7 inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
et ils y annoncèrent l'Évangile.
8 A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
Or, il y avait à Lystre un homme paralysé des jambes, estropié de naissance; toujours assis, il n'avait jamais marché.
9 Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
Cet homme écoutait Paul parler et lui, arrêtant sur lui son regard, vit qu'il avait la foi pour être guéri. Il lui dit alors à haute voix:
10 sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
«Lève-toi droit sur tes pieds; » il se leva d'un saut; il marchait!
11 Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
Le peuple, voyant ce que Paul avait fait, se mit à pousser des acclamations, et à s'écrier en langue lycaonienne: «Les dieux sous forme humaine sont descendus vers nous»!
12 Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
Barnabas fut appelé Zeus, et Paul Hermès, parce que c'était lui qui portait la parole.
13 Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
Le prêtre de Zeus, qui avait un temple à l'entrée de la ville, amena des taureaux et apporta des guirlandes devant les portes, et, d'accord avec le peuple, il allait offrir un sacrifice.
14 Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
Mais les apôtres Barnabas et Paul, apprenant cela, déchirèrent leurs vêtements, et se jetèrent au milieu de la foule en s'écriant:
15 “Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
Lycaoniens «Pourquoi faites-vous cela? Nous sommes de même nature que vous, nous ne sommes que des hommes, nous vous prêchons l'Évangile qui vous dit de renoncer à ces idoles inutiles, de vous tourner vers le Dieu vivant, créateur du ciel, de la terre, de la mer,
16 A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
et de tout ce qu'ils renferment. Il a laissé, dans les siècles passés, toutes les nations païennes suivre leurs propres voies;
17 Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
et cependant il s'est fait connaître à vous par ses bienfaits; c'est lui qui vous donne la pluie du ciel, les saisons avec leurs fruits, la nourriture et toutes les joies du coeur dont vous êtes comblés.»
18 Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
Malgré ces paroles, ce ne fut pas sans peine qu'ils empêchèrent le peuple de leur offrir un sacrifice.
19 Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
Cependant, survinrent d'Antioche et d'Iconium des Juifs qui gagnèrent le peuple et Paul fut lapidé, traîné hors de la ville et laissé pour mort.
20 Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
Quand les disciples vinrent l'entourer, il se releva et rentra dans la ville. Le lendemain, il partit avec Barnabas pour Derbé.
21 Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
Ils y annoncèrent l'Évangile et y firent de nombreux disciples, puis retournèrent à Lystre, à Iconium et à Antioche,
22 suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
affermissant l'esprit des disciples, les exhortant à persévérer dans la foi et leur apprenant que c'est par beaucoup de tribulations qu'on entre dans le Royaume de Dieu.
23 Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
Ils firent nommer des Anciens dans chaque Église, puis ils les recommandèrent par des jeûnes et des prières au Seigneur en qui ils avaient cru.
24 Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
Ils traversèrent ensuite la Pisidie, vinrent en Pamphylie
25 kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
et, après avoir annoncé la parole à Perge, ils descendirent à Attalie.
26 Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
De là ils firent voile pour Antioche, où ils avaient été livrés à la grâce de Dieu pour l'oeuvre qu'ils venaient d'accomplir.
27 Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
A leur arrivée, ils convoquèrent l'Église et racontèrent les choses que Dieu avait faites par eux. «Il a ouvert aux païens, dirent-ils, la porte de la foi.»
28 Suka kuma jima a can tare da almajirai.
Ils faisaient un assez long séjour auprès des disciples

< Ayyukan Manzanni 14 >