< Ayyukan Manzanni 14 >

1 A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
And it came to pass in Iconium according to the same thing, for them to enter into the synagogue of the Jews, and to speak so as for a great quantity to believe, both of Jews and of Greeks.
2 Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
But the disobedient Jews aroused the souls of the Gentiles, and made them evil against the brothers.
3 Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
Indeed therefore they remained a considerable time speaking boldly in the Lord-him testifying to the word of his grace, granting signs and wonders to occur by their hands.
4 Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
But the majority of the city was divided, and verily there were those with the Jews, and those with the apostles.
5 Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
And as a violent movement developed, both of the Gentiles and of the Jews, with their rulers, to denounce and to stone them,
6 Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
having become aware of it, they fled to the cities of Lycaonia, Lystra, and Derbe, and the neighboring region.
7 inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
And there they were preaching the good news.
8 A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
And a certain man was sitting in Lystra, disabled in his feet, being a cripple from his mother's belly, who had never walked.
9 Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
This man was listening to Paul speaking, who, having gazed at him, and having seen that he has faith to be healed,
10 sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
said with a great voice, Stand correctly on thy feet. And he leaped up and walked.
11 Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
And the multitudes who saw what Paul did, lifted up their voice, speaking Lycaonian, The gods came down to us, having become like men.
12 Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
And they actually called Barnabas, Zeus, and Paul, Hermes, because he was the man who led the word.
13 Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
And the priest of Zeus, being in front of their city, after bringing oxen and garlands to the gates, wanted to sacrifice with the multitudes.
14 Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
But when the apostles, Barnabas and Paul, heard, having torn their garments, they rushed into the crowd, crying out
15 “Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
and saying, Men, why are ye doing these things? We also are men of like nature with you, proclaiming good news to you, to turn from these vain things to the living God, who made the heaven and the earth and the sea, and all the things in them,
16 A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
who in the generations that have passed allowed all the nations to go in their own ways,
17 Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
although he did not leave himself without evidence, doing good and giving you rains from heaven and fruitful seasons, filling our hearts of food and gladness.
18 Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
And saying these things, they scarcely restrained the multitudes not to sacrifice to them.
19 Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
But Jews came from Antioch and Iconium. And having persuaded the crowds, and having stoned Paul, they dragged him out of the city, after presuming him to be dead.
20 Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
But the disciples having surrounded him, after rising, he came into the city. And on the morrow he departed with Barnabas to Derbe.
21 Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
And having preached the good news to that city, and having made considerable disciples, they returned to Lystra, and to Iconium, and to Antioch,
22 suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
strengthening the souls of the disciples, exhorting them to continue in the faith, and that it was necessary for us to enter into the kingdom of God through many tribulations.
23 Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
And having appointed elders for them in every congregation, having prayed with fasting, they entrusted them to the Lord, in whom they had believed.
24 Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
And after passing through Pisidia, they came to Pamphylia.
25 kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
And when they spoke the word in Perga, they went down to Attalia,
26 Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
and from there they sailed to Antioch, from where they were delivered to the grace of God for the work that they fulfilled.
27 Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
And after arriving, and after gathering the assembly together, they reported as many things as God did with them, and that he opened a door of faith to the Gentiles.
28 Suka kuma jima a can tare da almajirai.
And they remained there no little time with the disciples.

< Ayyukan Manzanni 14 >