< Ayyukan Manzanni 14 >
1 A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
Také v Ikoniu kázali Pavel s Barnabášem nejprve v synagoze, a to tak mocně, že uvěřilo mnoho židů i pohanů.
2 Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
I tam se ovšem vyskytli židé, kterým se to nelíbilo, popouzeli místní obyvatele a šířili nenávist proti křesťanům.
3 Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
Pavel s Barnabášem tam přesto zůstali dost dlouho a neohroženě zvěstovali Krista. Pán se přiznával k jejich hlásání evangelia, dával jim moc konat znamení a divy.
4 Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
Obyvatelé Ikonia se rozdělili na dva tábory – jedni byli s pravověrnými židy a druzí s křesťany.
5 Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
Apoštolové se dozvěděli, že jejich odpůrci – pohané i židé v čele s představenstvem synagogy – je chtějí napadnout a ukamenovat. Proto utekli a zdržovali se v nedalekých městech Lystře, Derbe a v jejich okolí.
6 Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
7 inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
Nedali se však zastrašit a hlásali tam dále Kristovo evangelium.
8 A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
V Lystře žil muž s ochrnutýma nohama. Měl vrozenou vadu, takže nikdy v životě nechodil.
9 Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
Ten byl také mezi Pavlovými posluchači. Pavel se na něj pozorně zahleděl a poznal u něho víru v Boží pomoc.
10 sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
Zavolal na něj: „Narovnej se a postav se na nohy!“Chromý vyskočil a chodil.
11 Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
Lidé, kteří byli u toho, začali provolávat: „Navštívili nás bohové v lidské podobě!“
12 Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
O Barnabášovi tvrdili, že je Zeus, a o Pavlovi, že je Hermes – posel bohů, protože většinou mluvil.
13 Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
Došlo to tak daleko, že kněz místního Diova chrámu už přiváděl na shromaždiště ověnčené býky a chystali se je apoštolům obětovat. Ti nejprve netušili, co se děje, protože lidé mezi sebou mluvili lykaonsky.
14 Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
Když to však pochopili, roztrhli svá vrchní roucha na znamení nesouhlasu, rychle sestoupili z vyvýšeného místa, odkud mluvili k lidem,
15 “Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
a horlivě je přesvědčovali: „Přátelé, co to děláte? My jsme přece lidé jako vy! Vyzýváme vás, abyste zanechali též marné modloslužby a obrátili se k jedinému živému Bohu, stvořiteli nebe, země, moře a všech tvorů.
16 A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
Dosud vás nechával jít po vašich vlastních cestách, ale nyní chce, abyste opustili své bludy.
17 Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
Vždyť vás má rád a všechno dobré máte od něho: déšť, úrodu, jídla dosyta a každou radost.“
18 Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
Jen stěží jim apoštolové rozmluvili, aby jim neobětovali jako bohům.
19 Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
Potom se však objevili židé z Antiochie a Ikonia, přetáhli zmatený zástup na svou stranu a poštvali ho proti apoštolům. A tak místo pocty Pavla kamenovali a jeho bezvládné tělo vyvlekli za hradby, protože se domnívali, že je mrtev.
20 Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
Křesťané se k němu sběhli, a když se Pavel probral, vrátil se do města. Příštího dne však raději odešel s Barnabášem do Derbe,
21 Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
kde opět kázali radostnou zvěst o Kristu a získali mu tam mnoho následovníků. Pak se vydali na zpáteční cestu přes Lystru, Ikonium a Pisidiskou Antiochii.
22 suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
Všude dodávali křesťanům odvahu a povzbuzovali je: „Jen vytrvejte ve víře! Čeká nás mnoho utrpení, ale cíl – Boží království – za to stojí.“
23 Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
V každém sboru po modlitbách a půstu ustanovili správce a odevzdali všechny do ochrany Pána, v něhož uvěřili.
24 Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
Pisidií tentokrát jen prošli,
25 kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
ale v Pamfylii kázali ve městě Perge. Z přístavu Attalia
26 Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
se pak plavili zpět do Antiochie v Sýrii, kde jim před časem vyprosili Boží milost k práci, kterou právě dokončili.
27 Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
Po návratu apoštolů se shromáždil celý sbor a oni vyprávěli, co Bůh konal jejich prostřednictvím a jak otevírá pohanům přístup k víře.
28 Suka kuma jima a can tare da almajirai.
Pavel a Barnabáš pak zůstali s křesťany v Antiochii delší dobu.